Zeenatu (complete)

Sunday 13 ga watan July 2010 K'arfe goma da rabi 10am dede ta fito sanye d'aure da d'aurin k'irji ta d'ora karamin hijab da alama wanka Zatai, kitchen ta shiga ta fito ta d'anyi tsaki inda ta k'wala kiran .... "Sadiq! Sadiq! Wai kana inane "?


Tsayawa tai tana huci da mirrow ahannu tana duba afuskarta Saboda kurkum en da ta saka ,tsaki tayi tai side en d'akin Sadiq ta shiga ta buga gadon da Sadiq keta sharara bacci. " Ah lallema bacci kake kwasa ko to wallahi sai ka tashi", sadiq ta fad'a da k'arfi ,tashi yai zaune yana mik'a tareda mutstsike Ido Alamar baccin bai sake shi ba,"haba ya zee me yasa sei mutum na bacci kizo Kina tashin sa? haba ay wan nan bayi bane" yai tsaki, "ah lalle Sadiq wuyanka yayi kauri to ka tashi kayo cefane don yanzu 11 don kaga mom da sauran 'yan gidan basa nan shine zaka kwanta ko so kake Ni naje gaka agida"? . ****** *** "to Ni kad'ai ne agidan? ina Faty ita taje man seni da kika raina to wallahi baza Ni ba,kinsan dai Yau weekend wallahi ko kinfi Mayen k'arfe naci Yau ranar Hutu nane haka kawai kinsa kai na na ciwo kin wani saka Abu afuska kamar aljana" duka ta kai mai ya kau ce "wallahi saduqu Yau baka da kwano agidan nan sai dai kaci walk'iya " tashi yay ya nuna ta da yatsa "kifa Dena cemun saduqu idan bara ki ce mun Sadiq ba Ki shiru". " Anfad'a saduqu wallahi yau baka da abinci agidan nan ,Allah ya soka Yau 'yan fad'an basa kaina kasan de halina ,Yau cike nake dam da kud'I shi'isa zan saurarra maka ,don rashin kunya ina ya yarka muna sa'insa dakai" haushi ne ya ishe shi don ya tsani atada shi a bacci duk sai yaji wani iri, "malama Ki fita kona hamb'arar dake almasifatu kawai" dariya tai tace zaka gane kurenka ne Yau. . ********* fita tai ta banko mai k'ofar suk Dan yaji haushi ,wanko fuskarta tai abakin famfo ta shiga d'aki ta d'au mirrow ta duba fuskarta taga tai fes murmushi tai ta zari mayafi ta fita siiyan kayan miyaan....kad'an kenan Daga ZEENATU . . *© Queen



* . [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page2* . ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. . *®NWA* . tafiya take da sauri sauri don ta siyo kayan miyan ta dawo da wuri ,bayan tayo cefanen munay da Aneesa kawayen ta na islamiyar su adede bakin bishiya suna hira ,munay tace" Aneesa kinga zee dama abinda Abu mai kitso tafad'a Gaskyne"? Aneesa tace" nifa ban San maganar ba ,nan munay ta janyo kunnen Aneesa ta rad'a mata dagowa tai "ke Dan Allah tab ,bari mu mata Magana ,Munay tace zeenat ,zee dake sauri Sam bata lura dasu ba jin Ana kiran ta ta juya arba tai dasu ahhh" manyan k'asa dama kuna nan" kallon juna sukai suka jun-jina kai. . ************* gaisawa sukai inda Aneesa tace" wai ni zeenat mijin naki tafiya yai ne naganki agida wajen 2 month fa" ?,munay dake zungurar Aneesa kar ta Jan gwalo musu masifa nan kwaa zee ta aje Kayan miyan agefe ta gyara zaaman mayafinta "to magulmata ay dama tin sanda naji kun kirani nasan da gulma abakin ku ,to Dan k'aniyar ku meye ruwan ku da rayuwa ta idan ma kaso auren nai bata shafeku ba banzaye nade fi wanda ko lalle ba' a tab'a saka suba",Aneesa da yake tafi tafi munay fad'a ta kalleta ke dallah zee saurarra kinji mun ambaci kaso aure harda zakina cemana muna fukai ,tabbas maganar Abu mai kitso gaskiyace ashe anji kunya"ji kake tas tas zeena ta kai ma Aneesa maree tare da nuna ta da yatsa "Ni ba kanwar laasa bace kin san bana barin ta kwana karki manta zeemasifa Nake domin kinfi kowa sanina a school ban san gulma Kuma wallahi Abu mai kitso zata rena kanta munafukan banza da wofi ta kalli munay ta Harare ta ta d'au kayan miyanta tai gaba ,tana tafiya tana huci haka ta shiga gidan su Lokacin Sadiq ya biyo Faty zai daka bangaje zee tai take zee ta kamota ta d'uma mata dundu tahau ta da bala'I kuka sosai Faty Keyi "Kiyi hkr ya zee ya Sadiq ne ya biyoni zai dake Ni don na ta sheshi Daga barci ya ban Hansin zan sayo book " . . ************* "dallah malama yiwa mutane shuru kin san de saduqu mugune in yana mayen baccin nan nasa Ni matsa kiban gu karna huce akanki don raina abace yake" ,sanin Halin yayar tata yasa ta matsa. Aje mayafinta tai ta gyara kayan miyan duba agogo tai taga 12 tayi tsaki tad'ebi kad'an Daga kayan miyar zata jajjaga sanin idan tajira marked'e har 3 sai tai muusu ba agama ba ga blender ensu ta lalace ,sharp -sharp tai markad'en ta D'ora jallof rice ,sai wajen 2:30 ta gama ,bayan tayi wanka ,ta zuba musu itada Faty suna ci afalo sunsa film en D'an ibro suna kalla. ******** Sadiq ne ya fito Daga d'akinsa ya shiga kitchen ya d'au fillet ya bud'e flaks ya d'ebe abinci taf ya juya zai d'au spoon Faty ta shiga d'aukan cup da gudu ta juya "ya zee Sadiq ya hanani d'au ka da sauri zee ta fita ta shiga kitchen en ganin ya cika fillet da abinci yasa ta d'auke "wallahi saduqu baza kaci abincin nan ba" juyowa yai "wallahi sai naci ay bake kika kawo abincin ba " dan bani na kawo ba aini na girka nan nace kayo cefane kak'i " juyewa tai a flks ta d'auke takai can cikin d'akin mum nasu ganin ba sarki sai Allah ya fita yana tsaki ,yana k'wafa kofar gida yaje ya zauna , wajen 4 ya koma gidan ya gansu sai sharar bacci suke silalawa yai ya d'auke flask en ya iba ya aje a kitchen yaci ya fice . ********** wajen 6 mum nasu suka dawo nan gida ya har gitse, zeena sai bala'I take kan Sadiq tad'au abinci saida mum ta bata hkr hira suke tayi sadiya me bin Sadiq sautsayi yasa ta zubarwa da zee humra enta, duka tai mata kuka sosai sadeey keyi mum na zaune a kan tabarma tai tsaki wai" ke zeena mesa Baki da hak'uri ne? Kome akai miki Saikin rama haba Baki da Aiki sai masifa ba zafa kizo Ki takurawa yarana ba mesa l Baki zamanki agidanki ba". Fitowa tai ta turo Baki da hijab tace Allah" mum Yau raina ab'ace yake" mum ta kalleta tace "haka de kurlum kice ranki ab'ace kide dunga Sawa zuciyanki ruwan sanyi ,ruwan alwala ta d'auko ta tsuguna tanayi "haba ayi mutum ba hkr "haushi ne ya isheta ta saka takalminta tai waje tana huci............... *©Queen



* [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page3* . ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. . *®NWA* . bayan fitarta bata zame ko ina ba sai gidan Abu mai kitso Sallama take ta dokawa kallon gidan tai ta tab'e Baki ,Sallama ta kuma dokawa Abu tafito Daga d'aki" Aa zeena ce Yau hala de yau kitson kike so wan nan uban kan naki me yawa da tsawo dama yaci ace Kina kitse shi Amma naga ke Baki son kitso". Hannu ta d'aga wa Abu alamar tai mata shuru ,kujera 'yar tsuguno ta d'auka ta zauna ta kalli Abu ta turo d'an kwalinta gaba. "Abu idan kin gama soki burutsun naki sai Ki tsaya na d'ora Daga inda kika tsaya,yanzu Abu abinda kikai ya dace kenan meye ruwanki dani wai zakina cewa nakaso aure harda gayawa su munay da gurmanki da komi ay wallahi badon ina jin kunayarki Dana miki tatas kin san Ni bana ragowa domin Ni zafi ce kana mun zan maka don haka akula don haka sai anjima", sakato Abun tai ta tab'e Baki tashigo d'aki domin tasan itace da lefi. ************ 8:pm Zee na zaune tana gyara kayan business nata data keyi ,k'irrr wayarta tai k'ara dubawa tai taga me kiran tsaki tai ta basar wajen 3 times Ana bigowa Amma Batai pickin ba wayar aka kuma kira ra d'auka afusace "malam ko naci wani Abu bam baka ba zakana kirana kasan banida sauran wani issues dakai yanzu don haka leave me alone" Daga can akace pls" zee kiyi hkr balaifina bane ba kema kin sani baran iya rayuwa babu ke ba zee ta,pls ",tsaki tayi haidar na gayama ka k'yaleni kabi wani Sarkin" kit ta kashe wayar "ayi mutum da naci" . ************* Sadiq ne ya shigo d'akin ganin kudi ahannun zeee yace "ah ya zee hannunki da kyau zama yai gefen ta yad'au wata powder Alin yana juyawa "nawa wan nan "?d'agowa tai ta kalleshi "600hundred me Zakai dashi kai ba mace ba "? Dariya yasa lalle" ashe haka kike cin kud'in mutane yanzu wan nan abar har 600 hundred tab Ni de in kin sai dan 200 gata "wait Sadiq wai me zakai da powder? "My fiancy zan sai dawa tana gogawa afuskar ta idan naje zance"dariya ta fara harda su tafi ,mum ce ta shigo d'akin Yau zeena da Sadiq ke shiri ,mum" ashe Sadiq nada budurwa da sauri ya toshe bakin ta ,Allah mum k'arya take k'arami dani zan budurwa abin ne yabaw mum dariya tace" ai Batai k'arya ba tunda yanzu zamani yazo don rashin kunya sai kaga yaro yaje gun wadda ta girmesa zance", "sosai ma mum ,harda cewa zai sai da mata tana shafawa afuskarta don yagani yaji dadi. "Allah mum k'arya take sai sunne kai yake ,kallonsa mum tai tace Banda de shirme yanzu karatu ne gabanka ba harkar Shime ba ,da gudu ya fita zee ta fashe da dariya. **************** "zeena" Naam mami Ki" saurareni kiji d'azu babanki ya bani sak'o gunki yace wai ya maganar koma warki gidan haidar yace Bazai miki dole ba. Tunda abun ya had'o da iyayen haidar in yace bai son akoma yar gidan Jiya,domin Jiya sai da haidar yaje gun sa. Kan maganar" kuka zee ta fara Ni mum bazan koma ba yanzu har kin manta abunda sukai mun Allah mum ku kyaleshi Ni na hkr Allah ya had'a kowa da rabonsa "shuru mum tayi nad'an lokaci san nan tace" To Allah yasa hakan shiyafi alkairi " kasa kasa zeena tai dariya tareda cewa "Ameeen" sai" kuma Ki koma school sosaima mum, tashi tai ta shige d'aki Jikinta asanyaye tana tuno haidar missn ensa take sosai................. © *Queen



* , [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page4* . ? ? ? ? ?. ?. ?. ?. ?. . *®NWA* . *[ Mon 5 Sep 2016]* *Wacece ZEENATU* Asalin mahaifan Zeenatu Malam kabir da bilki fulanin garko ne dake cikin kano state aikin gwabnati ne ya kai mahaifin Zeenatu jigawa inda ya ke Aiki a k'aramar hukumar Dutse local government, su biyar ne 'ya'yansu Zeenatu itace babba sai Sadiq dake bi mata ,sai sadeey, fatyma da autansu Khalid,gidan su ba wani babba bane Amma Saboda akwai tsafta kullum zaka kaganshi fes fes Maman su na sana'ar saida atampofi dede gwargwado suna da Rufun asiri ,Zeenatu tun tana yarinya Allah yayita rigimarmiya kwata- kwata bata da hkr duk abinda kai mata sai ta rama komi k'an -kantar sa,ga tarar fad'a koba da ita ake ba sai ta sai fad'an Zeenatu na shekara goma shabiyu Lokacin tana jss 2 mamanta tana saida meatpie da lemo da sauransu unguwar d suke kullum cikin cin bashi suke basa biyanta abin na bawa zeena haushi in yaro yazo siyan Abu taita hararar sa. ************** wata rana wani yaro yazo siyan meatpie da lemu tana falon mum tana cin abinci Lokacin bata dad'e da dawowa Daga school ba ,Sallama yaron ke tayi da gudu ta fita ta tsaya akansa "kai kace babu ku kullum bara ku tawo da kud'i ba sai bashi to bara abayar ba " tai shuru tana jijjiga yaro yace to" ai ke bake ce Matar gidan ba kuma mamana ta bani kud'in" "au mugani yaro ya mika mata "Allah yaso ka me katon kai d'auko mai tai ta dungure mai kai ,saida yaje soro yace ALLAH ya isa da gudu ta bishi har waje sai kwasar gudu suke takama shi ya fadi lemon da meatpie en suka fadi kas ta d'uma mai dundu,haka yaro ya tafi sai ihu yake. ************** fad'a sosai ya kaure tsakanin Sadiq da Zeenatu mum dake d'akin malam ta fito "Aa zeena wai me yaron nan yai miki ne tun Jiya d dare kike jibgarsa kunshe Baki tai ,"Nama na ya cinyen kuma sai na rama" kai Sadiq mesa ka cinye mata "?mum wlh Jiya da darene bansan na hada da namanta ba na cinye kuma na bata hkr taki hkr " da yke da one yr ta girmeshi kasan kansu daya ,haba" zee ayke yayarsa ce bakya ganin k'aninki ne "?mum nifa bazan hkr ba sai ya biya Ni" sanin halinta Inde be biya ba sai tai sati tana mita ,mum ce d'auke da yankan Nama d'aya data tsamo amiya ta mik'awa zee murmishi tai ta karb'a Allah ya soka da yau ka daku" Zeee Ki dinga hkr banso Ki tashi ahakan kin san de zaki aure kidena duk wanda yai miki Abu ya Baki hkr to Ki hkr domin rayuwa ba haka take ba " school bag enta ta islamiya ta d'auko "to mum zan koyi hkrn ,haka tai ficewarta tana 'yan wak'ok'inta. ********* zuwanta makarantar dede class nasu wasu yara na fad'a d'ayan babba ce tafi d'ayar girma naka ta tai da kas ,zeena dake tawowa ta tsaya ta kama baki dama" futha Baki da k'arfi" ,zuwa tai ta tsaya Ki" ban biyar na sai fad'an futha ta juyo Allah" zeena ita kadai gareni" cizo daayar ta gantsarawa futha ihu tasa ,naira biyr en ta d'auko ta mik'awa zeeena wata dariya tasa ta damk'o hijab en nafeee nan fad'a ya kaure Dukan tsiya taiwa nafeee ,"Ki kuma dukan wani Ki gani "ta d'au Jakarta "ke kuma ban biyar en da sauri ta mika mata ta shige class.........: . *©Queen



* [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page5*. . . ? ? ? . ? ? ? . ? ? . *®NWA* . *[TUE 6 sep 2016]* . *Dedicated to Benazir Omar & Lubie maitafsir* . K'anwar mum ta haihu tun safe suke shiri zasu suna da yake jigawa da kano ba nisa wajen 12 sukaje ,kid'an k'warya keta tashi agidan inda uwani mai kid'an kwarya keta bugawa mai jego da danginta na rawa shingar su zeena sai kumbure -kumbure take sabili da Sadiq ya jik'a mata gyalenta zata da keshi mum ta hana ,shi'isa take ta had'e -had'en rai haka aka kawo musu abincin suna da su drinks suna ci zee ko gallon abincin Batai ba ,mum ta juya ta kalleta "zeena wai mesa ke kullum fushi haka da rashin hak'uri haba ayi mutum bai da afuwa (yafiya) Allah de ya tsaida wan nan halin naki a yarinta",turo Baki tai haba" mum kullum Sadiq sai yayii ta mun abu ina k'ya leshi" "zeena amman de kin san shi idan kikai mai da kin bashi hak'uri yake hak'ura ,to ke mesa Inshi yayi miki bakya hak'ura"? Juya baya tai bata ce komi ba . ************* bara'atu itace mai jegon ta tawo Aa" my zee ya naga kina kuka"? Mum ko kallon su Batai ba ,"yaya bilki meya faru da zeena ne"? Uhum" bara'atu kenan kema dai kin san de halin 'yar taki Sam bata yafiya na rasa halin wa ta d'auko,Ana cewa goggo tayo ay wallahi bahaka take ba"(goggo kamar zeena) Jan zeena tai "rabu dasu kinji my zee zo Ki ga abinda zan miki, kalli sadeey bata irin haka sai ke baki San kin fara zamaa 'yammata ba",murmushi zee tai "bakomi Anty bara" gurun uwanii mai kid'an k'warya Anty bara taje ta rad'a mata Magana akunne nan da nan kid'a ya canja uwani tace" kowa dake filin rawar yaje ya zauna . ************ uwani mai kid'a tace zeena ta shiga filin rawa kunya ce ta kama ta ganin hakan uwani tace yara dede sa'aninta suzo su taya ta rawar wan nan kid'an nata ne ,hakan kuwa sai wak'e zeena take sosai ,tana *_zeena yar yarinya kyakykyawa ga gashi mai dara-daran Ida nuwa kai ku bani kid'an zeena_* nan da nan zeena kanta ya ' fasu ta fara rawa taji Ana wasa ta har dasu girgiza sauran yaran na biye mata baya ,Anty bara sai lik'i take mata ita kanta mum sai da zeena ta bata dariya,wata acikin yaran garin tik'ar rawa ta takewa zeena k'afa bata sani ba ,hak'uri ta bawa zeena kallonta tai ta girgiza kai, yarinyar tace nagode , sai bayan da uwani ta tsaida kid'an don suyi sallah,zeena sai Ne man yarinyar da ta take mata k'afa take bata ganta ba. *********** sai can taga nota tana zuwa ta d'uma mata duka ta taka mata k'afa kuka sosai yarinyar keyi , "amma ai nabaki Hak'urri" eh" nasan kin bani hak'uri banyi bane" yarinyar tace" ,ban yafe miki ba" dukanta ta kuma nan da nan sukahau kokawa ta yagwa yarinyar Riga babar yarinyar tazo ta rabasu tanai wa zeena masifa "rank'washita tai nan zeena idanta ya kawo ruwa ta dai-daici yrinyar ta wanka mata Mari hakan maman yarinyar itama ta kwad'awa maree zeena kuka sosai take ,mum ta fito taja zeena, " haba baiwar Allah keda yakamata ki raba su Amma sai ki tarewa 'yar ki ki hau dukanta ai d'a na kowa ne" matar tace "kinga malama tun d'azu 'yar taki ke dukanta ji yanda ta yaga mata Riga don haka inna dake ta ita taja,ya kamata kiwa 'yarki fad'a ta ja hannun 'yar tata suka fita,ran mum ya baci "kinga abinda kika janyon ko ina zaman zaamana kinsa angayan Magana rashin hak'urinki na kusa Dena fita dake tunda Magana kike janyon k'wafa tai ta shige ciki zeena na binta abaya tasan intai Magana duka zata sha............. . *©Queen



* *



queen.pun.bz* . [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page6* . ?. ?. ?. ?. ?. . ? ?. ? . *®NWA* . *[THU 8 Sep 2016]* *dedicated to Lubie & bena* . Haka rayuwar zeena tacii gaba da gudana mai hali baya fasa halinsa ,shigarta ss1 ta tsiri felek'e da iyayi Saboda ta zama 'yan mata ga son girma akwai wata k'awarta mariya class nasu d'aya tana sit in baya zeena na na gaba Anai musu note biro inta ya kare ta juya ta au na mariya ta ci gaba da note ,mariya ta duba Ba taga biro inta ba ta tashi tseye ta le'a gaban zee ta warce abinta zee ta juya " meye don na au biro naki zaki k'wace "? Shuru mariya tai "wai ba Magana nake miki ba" ina jinki zee sai kin gama nunan isa da gadarar Se in Baki amsa ,kuma biro ne baran bayarba". ***************** "ke in banza ko kunya bakiji ba,ran nan nasayo miki book Amma biro ki kasa Aran kin san nafi arfinsa",warcewa ta kumayi nan da nan mariya ta cakumeta da fa a ,dayake ba teacher aciki haka sukaita Dan batuwa ,vice princepal yazo wucewa yaji hayaniya nan ya shiga ya tarwatse su ya fita dasu yasa basu punishment Seda sukai 1 hour San nan akai musu bulala ya sallamesu yayiwa zee fa a Kan ta dena tsokana ,harara suke ta dokawa juna ,zee kam bata Ha'ura ba duk da itace da tsokana taci alwashin seta daketa ,shigar su cikin class in 'yan team in zeena suka hau aga mata hannu "sai zeee " murmushi tai wata lubna close frnd in mariya Tai tsaki " zee en da ba k'arfi gareta ba sai tsokana " mariya tace" kema Kya Fa a k'awalli" nan suka kwashe da dariya suka tafa,haushi ya ishi zeee ta cafko lubna k'awar mariya ta kai mata maree take idon ta ya k'ak'-k'afe alamu aljanunta sun tashi. ************ zo kuga yanda idon zee ya Firi-fito Saboda tsoro ,ihu lubna ta fara ta cafko rigar zeee ta matse ta ihu tai tayi ,idanuwan lubna sukai jajawur gumi ihu lubna ta kuma sakawa nan ta fadi as tana birgima take class ya har gitse tuni malamai suka zo aka samu wani malami a cikin su ya farai mata karatu ihu ta kuma yi tana surutai " ku gayawa zeena tunda ta tab'oni sai ta gane kurenta mesa zata b'atan rai wallahi yau Sekin gane kurenki in kinje gida kuka wiwi zee keyi ta bud'e baki "lubna kiyi hkr" baruwana se kin gane kurenki ,fizge -fizge lubna ta fara da k'yar aljana suka sauka tai bacci zo ku ga yanda idanuwan zeena ke tsiyayar da hawaye ta had'a gumi nan monitor suka fitar da lubna ,asalub'e zee ta zauna Kan bench inta nan 'yan class suka fashe da shewa ,d'ago kai tayi ta bisu da Ido tai k'wafa ,nan suka dinga had'a Baki suuna cewa "anyi walk'iya mung...... Tashi tsaye tai "wallahi duk se kun gane kurenku banzaye kawai ,ihu suka kuma sawa suka kuma had'a Baki "anyi walk'iya.... ,dai2 tym in aka buga k'ararrawa da gudu suka dinga fita Saboda sun San halin zeemasifa............... . *©Queen



* *



queen.pun.bz [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page7* . ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ? . . *®NWA . [SAT 10 2016] dedicated to Lubie & bena* . . Asalub'e taje gida idonta yai zuru- zuru haka tai sallah ta zauna cin abinci sai had'e rai take ,haka Sadiq ma ya shigo gidan wujiga-wujiga da alama yunwa yakeji sai k'walawa mum kira yake shigar sa falon yai tozali da zee sai kai Loma take "wayyo zee dama yunwa nakeji" zama yai ya tsumbula hannu cikin kwanon yakai Loma,zee ta rik'e hannunsa "waya baka izinin samun ban zan hannunka daba ka eanke cikin abinci na"? ta ture hannun " haba zee yunwa fa nakeji" "to baraka bari mum tazo ta baka ba ko faty bara tazo inacin abinci ta saka hannu ba sekai da girman ka". "wallahi zee sai naci Saboda yau a school banci komi ba kai hannu yai ya cigaba daci tsam ta tashi taje ta wanko hannunta shi kam ya cinye yana mata gwalo k'wafa tai "zaka sani ne". *********** wajen 3 zee ta tashi ta shiga toilet Dan yin wanka Saboda Lokacin islamiyar su yayi,mum na d'aki tana kallon tsoffin picture inta ihun zee ta jiyo da gudu ta fita ta bud'e toilet en tana "meye zee"? "wayyo mum shikenan abunda lubna ta fad'a gaskiyane wayyo na shiga uku" tsaki mum tayi "idan bara ki fad'an ba to kiwa mutane shuru" gunjin kuka taci gaba " mum Aljana ne ta kashen fitilar K'wan band'akin nan Lokacin Dana shigo akunne yake Amma na sunkuya ina cud'a k'afa na ina d'agowa Naga d'if ya mutu shine na d'aura zanina na d'auka shigowa akai Seda na duba Naga bakowa "kuka ta kuma fashewa Jikinta na rawa "dama munyi fad'a da lubna ashool kuma tana da aljanu shine tace wai in sauraraeta inna koma gida"hannu mum dake Kan hab'ar ta ta sauke " Amma ke zee anyi mai wawta to wutar nepa aka d'auke ,Inde kinyi adduar shiga toilet to Allah zai kareki kuma ki kwantar da hankalinki wasa take "rufo mata band'akin tai dak'yar zee ta k'arasa wan kan tai shirin school idon nan yai luhu-luhu Saboda kuka. ************ haka suna zaune da dare duk an hallara Ana hira faty na Kan cinyar mum Lokacin tana Sadiq na Kan kushin sadeey na zaune tana note uwargarin zee tana danna wayar mum ,faty ta taso ta zauna Kan ciyar zee tana k'ok'rain k'wace wayar hannun zee ,kin bata tai faty tasa kuka da tsamin bakinta tana "ki bani"doke hannunta tai "dalla tashi kibar nan uwar naci " dai- dai sai cinyar zee faty ta dai -dai ta ta gantsara mata cizo cin zafin datai yasa ta murd'a bakin Auta nan ta fara ihu mum tace" sannu zeena yanzu autar ki kaiwa haka "? "Mum kina ganin de cizon da tai mun bayan an hanata cizon mutane" "to kuma sai ki mata dukan k'arfi ai ba k'warunku d'aya ba " "ai hakuri mum " kwace wayar tai ta mikawa faty tace kowa yaje ya kwanta tunda 9pm tayi hakan kuwa sukai. *********** zeena har ta kwanta ta taashi don ta tuno fad'an ta da lubna nan tsoro ya shige ta sauri tai ta kunna K'wan cikin haske ya gauraye sai kalle -kalle take ahankali ta kwanta ,sai juye-juye take Saboda bata saba kwanada fitila ba ,taashi tai ta kashe fitilar har bacci yai awon gaba da ita jin motsi yasa ta fasa ihu "wayyo mum ga Lubna nan " mum dake d'akinta ta shiga dakin su zee ta kunna fitila ganin sadeey tai a tsaye Jikinta na karkarwa ga zee akan gado ta k'udun -dune. " wai meye hakane zee ?ke kuma sadeey meya tada ke?" Sadeey tace" fitsari na tashi zanyi shine naji ya zee ta fasa ihu taban Tsoro" zee dake zaune sai fiki-fiki take da Ido "mum wallahi ban d'auka ita bace ba" "jini nan zeena mesa ne yau duk kin birkice na gayamiki Lubna kawai don ta tsorata ki ne" zama tai Abakin gadon abinda" zan gaya miki kinga mutan b'oye in ka nuna kana Yawwan jin tsoro to sunfi shigar ka ina cede kinyi alwala da zaki kwanta da, adduoi,"? eh nayi ,San nan zee ki rage wasu abubuwan kinga girma kike yanzu fa shekararki 15 yrs pls ki rage yawan fushi da tsokana kinga gashi wata kunyi fad'a ta tsorata ki a banza" to mum naji nagode " "addua ta sasu suka kumayi ta kashe fitila ta fita da k'yar da bacci........ ************ . *to fanz ena Kuyi hkr da wan nan Saboda sallah ta k'arato insha Allahu Zeenatu zai daka ta anan sai kuma bayan sallah idan mai kowa mai komi ya kaimu insha Allahu zan cigaba,Fatan zakuyi sallah lafiya ku kasance dani akoda Yaushe taku har kullum



 . *Happy eid el Adhar to u ol* *©Queen



* [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page8* ?.         ?.         ?.           ?.           ?.           ? ?.              ?.          ?                 *®NWA* *dedicated to lubie maitafsir & Benazir*      *[9 Sep 2016]* ******** Zee tsaye a Gaban Allo ajin yayi tsit Ana jira aji ta fara karatun haddar da aka basu malam haruna dake tsaye ganin Zee Tai shiru yace "zeenatu ke nake saurare" tsuru -tsuru Tai da idanuwa take ya Nuna Munay da taxo Tai nata karatun Cikin nutuswa ta karanto dai-dai iya Inda akaa basu haddar haka ya umarceta dataje ta zauna ya kirawo Aneesa itama tayi ta zauna nan ya had'e rai ya juya gun Zee yace " wato duk abokan surutun naki sun iya haddar banda ke ko? me ya hanaki to"?. Shiru Tai ya daaka Mata tsawa ,jiki na rawa tace" ya sayyadi wallhi k'auye mukaje biki shiisa banyi haddar ba Amma na iya rabi " "ay dama zeena bakya hadda to wallhi kinsan Allah,idon baki haddar nan ba sekin D'an D'ana " ya sayyadi ta fad'a kallonta Yai "meye"? Dama cewa nai zan biya da qur'anin nan ya mika Mata aya biyu ta karanta Tai shiru ya d'ago ya" Naga kink'i k'arasawa nan ta kai qur' anin dai-dai idon ta ya" sayyadi bana ganin rubutun ne haka ta mutsits-tsike idonta ta kuma k'urawa qur anin Ido ,"wayyyo Allah na wai meya faru da idon nawa ne"? Hata kuma maimai ta ayoyin  bayan haka ta kuma tsayawa dariya malam haruna yasa nan 'yan class ma suka tuntsire da dariya. ******* Haka tabisu da Ido Tai k'wafa ,"ya sayyadi na gama" ta sunkwi dakai ,had'e rai yayi ai" sekin k'arasa kunya ce ta isheta ta kai wajen mintuna ahaka ganin zata b'ata musu lokacin yasa ya karb'e qur'anin yace ta matso kamar an dasa ta. ******* "Ba dake nake magana ba" bulala ya d'auko Yai Mata k'warara biyar ya K'ara Mata page d'aya "kuka take ahankali tana matse Ido munay ta sunkuya tana dariya haka malam haruna ya cigaba da karatunsa ita kam se kalle-kallen 'yan class en take taga Wanda yai Mata dariya ta rubuta Shi alist can ta gano ummi bogaza sunan Wata aclass en nasu dariya Zee tasa ganin bogaza da Tai na dariya haka malam haruna ya gama ya fice k'irrrr aka kad'a da sauri taje wani lungu ta tsaya ganin bogaza yasa tazo ta rik'eta "wa kikewa dariya don na kasa hadda " wallah ni ban miki dariya ba jikin ta se b'ari yake don dama tsoron Zee take d'uuu 'yan makaranta sukazo wucewa nan suka taru Wata kubra tace" ummi wallahi kima Zee duka kalleki ba jibgegiya  duk ajinmu ba Wanda ya kaiki k'iba Amma ki zauna jikinki na kar- karwa kan Zee". ganin hakan yasa Zee ta cafko ummi bogaza ta kai Mata duka dambe suka fara ummi bogaza ta d'aga Zee takai kass I'donta ya rufe sai dukan Zee take zo kuga idon Zee ya raina fata se Hawaye take cikin k'arfin hali ta gantsarawa bogaza cizo nan fad'an ya kuma rikicewa sai da wani mutum yazo wucewa ya rabasu kowa ya kama gabansa. ******** duk dukan nan da tasha bai sa ta hak'ura ba, haka tai ta falfalar gudu ga k'afarta na Mata zafii dukan da bogaza Tai Mata ,sai da ta kamo su munay har sun kusa Zuwa gida ta cakumo munay, munay tace" me nai miki"? Ai" kema kin san me ki kai mun dariyar da kikai mun kin d'auka zata tafi a banza ne"? Haka ta gasawa munay rak'washi take suka hautsine  Aneeaa na rabasu lokacin 6 dai-dai dadyn Zee zai tafi masallaci ya ganota, dak'yar ya rabasu yace "yanzu zeena yauma fad'an naki kika tsaya"? ga maminki can na nemanki " ya kalli munay daketa gurshek'en kuka ya bata hak'uri ya tambayeta meya had'asu nan ta rattaba mai cikin Jimami ya kalle Zee "yanzu kan hakan kika yaga Mata hijab har Abada ke baki da hak'uri wace irin zuciya gareki ne ehe"? naira hamsin ya d'auko ya bawa munay yace  taje a d'inke Mata. haka ya juya ya kalli Zee ya nuna Mata hanyar gida,haka ta tafi duk fuska a karce saboda fad'a ga Shi tana d'ingishi. *By*    *Queen



* . . [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queen



 page 9* ?.          ?.          ?.           ?.            ?.           ? ?.               ?.            ?              *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena*            *[17sep2016]* Haka taje gida tana d'ingishi mum dake kitchen tana kwashe tuwo ta ganta tace" Aa Zee meya faru da k'afar ne"?sukwi dakai tai bata ce komi ta shiga d'aki mum ta girgiza kai tabbas tasan fad'an nata ta janyo ,fitowa Tai ta d'ebo ruwa a buta ta fara Alwala dede zuba ruwan da Tai a fuska ta k'wala k'ara mum ta fito " ke mene" ?ganin fuskarta duk akarce yasa mum ta sa dariya "ai maganinta kema. Ayi mutum bai da Aiki se fushi da fada tunda Naga fuskarki nasan kinyi fad'a,da k'yer Tai Alwalar taje Tai sallah . *8 :pm* ****** duk suna zaune Ana ta kallo Zee ta had'e rai sai k'wafa take,tsam ta tashi ta ta shiga d'aki ta d'au qur'aninta tana hadda "mum wai me akaiwa Zee ne"? cewar sadiq mum tace" kasan Halin yayar taka kutsuwa ce" haka suka kwanta ba wanda ta cewa k'ala. *7:am* da safe kuwa kowa ya tashi Zee ta kasa tashi. Sai da mum ta shiga d'akin ta tadda ta  tana kuka sosai "wayyo mum k'afata na kasa tashi" taci gaba da kuka "muga kafar " mum ta d'aga k'afar taga ta kumbura daga gefe "Ashsha! garin yaya haka Zee"? sadiq dake k'ok'arin shiga d'akin yace "mum inaga fad'an da sukai  ne da ita da wasu kawayenta ,domin Naga suna ta dambe Allah mum Dan bakiga wadda suke fad'an da itaba gandamemiya ". dariya mum tasa ah" da walakin ai dama tin jiya na gano     Ai ga Shi nan Wata abanza ta jibgeki ke zeena ki Dena neman fad'a ayi mutum baya yafiya wallhi ke zaki sha wahala banza ahofi " zumb'ura baki Tai "mum dariya fa suke mun "     d'aga ta mum tayi k'ara ta saki sadiq sai dariya yake "Allah mum inna warke sai sadiq ya sani ".    Mum tace " Allah de ya Sawwak'e miki Zee ".    Da k'yar ta tashi ta kaita falo ta ebo ruwan zafi tana gasa Mata ,lokacin dadyn su ya fito zai kai su sadiq da sadeey da faty school nan ya tambayi meya faru,take mum taga ya mai.   Dady yace"Ai jiya nan nan na ganota suna fad'a da yaran gidan Alhaji tanko wai sun Mata dariya don takasa hadda"    Mum tace "Ah to Wanda baiji bari ba ai yaji hoho ai gashi nan jikinta ya gaya Mata".   Dady ya fita yace zai dawo da mai gyaran targad'e don da Alama Tai targad'e haka Tai sallah a zaune .   Wajen 12 Dady ya dawo da mai gyaran targad'e kama k'afarta yai ya duba nan ya fara gyarawa tun tana matsae -matse har ta fara ihu mum na rik'eta kuka sosai take.      Bayan ya gama ya bada magani asha fa agun haka ta zauna tana jinya .    Da yamma Dady ya kawo Mata hanta gasashshiya da milk nan Zee ta hau murna haka Tai taiwa su sadiq dangwaliliya . *7pm* ******** su munay da Aneesa suka zo dubiya Zee sai harare-Harare take Aneesa ta fito da Iv ta mik'awa Zee "gashi na bikin Anty ramla ne ranar Sunday" dariya tasa don Zee akwai son zuwa biki ko ba a gayyace ta ba.   Munay tace" to idan lokacin baki warke ba fa"?    "To 'yar bak'in ciki wlh ko ban warke ba senaje shine first fa da aka fara gayyatana biki"    Shiru sukai san nan suka tafi ,haka Zee Tai ta jinyar fuskrta da k'afarta har Ana I gobe bikin gidan su Aneesa Fes Zee ta mik'e ko Dan washe gari taje biki..... *© Queen



* [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page10* ?.             ?.           ?.       ?.              ?.            ? ?.                ?.              ?                *®NWA* *dedicated to Lubie & bena*      *[18 Sep,2016]* Tun sassafe Zee ke duba kalar Kayan da zata sa ko wanne se taje ta duba mirrow ta ga yanayin zamansa a k'alla ta d'auki kaya sun kai kala 5 duk basi Mata ba se ak'arshe ta gano wani kayan ta da Anty bara ta d'in koma Mata Harda mayafinsa ta aje gefe har wani yanga take . Haka taje ta duba takalman ta ta gano wani me d'an uban tsini Wanda sanda sukaje kano aka sai Mata ,Shi ma ta d'auko ta aje a gefe.    Mum dake shiga d'akin "oh su Zee gargaji ga ke tun yanzu kike had'a kayan zuwan bikin sekace Wata shaharriyar budurwa " dariya tasa mum" wallahi kwalliya zanci don har powder da lips stick zan sa"                   "haka ai akeso ki nutsu saura kuma kije ki neman fad'an agun biki"    "Mum ai bazanba " Bud'e kanta Tai tagan shi a cunkushe nan mum Ta taje Mata tasa ribborm .   Saboda dad'in za ta biki sai Aiki take yau har dasu wak'e -wak'e lokaci kad'an -kad'an sai ta kalli agogo haka da rana kowa ya kwanta bacci da yake weekend ne amma Banda Zee ta kafawa agogo Ido. *3:pm* ******* Zumbur Zee ta mik'e ta shiga wanka so biyu tana sab'a sabulu da gudu ta fito ta shige d'akinsu ta tsane jiki ta mulka mai Abu kad'an sai ta kalli agogo haka ta zira kayan dai-dai sun Mata kyau adai-dai shekarunta d'akin mum ta shiga lokacin tana kan sallaya "mum ki mun kwalliya na kasa kin san ni ban iya ba "    "To dama wane kwalliya za ki iya aise fad'a" dariya Tai" kai mum ai na Dena "    To Allah yasa my Zee haka mum ta zizarawa Zee kwalliya tasa Mata kwalli sosai a idon da yake masha Allah Tana da wadatattun idanuwa dara-dara tasa Mata lipstick ta taje Mata gira da yake irin girar nan ce da ita cunkus me yawa bak'a Sega zeee d'au skin inta me kalar choculate ta haskaka.     Haka ta feshe ta ta perfume sai ga zee Tamkar flower Tai kyau sai kallon mirrow take tana murmushi "mum dama Nima ina da kyau".?   "Sosaima Zee ai sema kin Dena fad'a kyanki zai dad'a fitowa"  Tsalle ta daka "ai mum na kusa Daina wa" dariya mum Tai to Allah yasa".     Agogo ta kalla taga 4:15 da gudu ta fita ta sako takalmin ta da wani mayafi shima dai-dai shekarun ta tsayawa Tai "mum na tafi "    "Zee kar naji kar na gani ". ************ Ahankali Zee ke tafiya don kar ta fad'I har yanga ake dosar gidan su Anee Tai taga motoci birjik K'ara sauri Tai jikin ta na rawa .wasu manyan 'yan Mata ne atsaye ganin yanda Zee ke tafiya yasa suka sa laugh Wata tace " ga yarinyar can se yanga take kuma masha Allah me kyau da ita, harara Zee ta buga musu dai -dai,shiga gidan taga munay.nan suka tsaya . Zee tace" wai  a ina za ai ne "?munay tace" a wani big house za ai  kusa da gidan Antyn su Anee ke kings gidan tab ya had'u "Zee ta yatsine fuska "to,mu a ina zamu "? munay tace" bakya ganin motoci ai aciki zamu shiga".    Ganin an fara shiga su zeee suka doshi Wata dalleliyar mota garin sauri Zee ta buge wani bata Sani ba  jiyawa Tai sukai Ido Hud'u da wani matashin saurayi da sauri  Ta k'arasa suka bud'e motar zasu shiga manyan 'yan Matan nan suka tsai dasu.     "Ku yaran nan ina zaku shiga? kuje ga bus can nan yara ke shiga" zeee ta tab'e baki tace to" dame kuka fimu "Wata tace zan mauje ki kina kwaila kina cusa kai". "Zee tace malama duk girmanki ba tsoronki zanji ba ta far-fara idon ta   Dariya suka sa Zee taja hannun munay suka doshi Wata mota waddama tafi d'ayar kyau bud'ewa  sukai suka zaman su .......ku dakace ni plsss. *©Queen



** [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . . . . . . *ZEENATU by Queen



 page11* ?.          ?.          ?.          ?.           ?.             ? ?.               ?.             ?                *®NWA* *dedicated to bena &Lubie*   *[18sep 2016]* Zaman su keda wuya suka hau magana zaune yake a driver sit yana kallonsu ta mudubi sai murmushi yake yana kallon Zee dake juya idanuwa wai ala dole Tai kyau ,haka kawai tun sa'ilin da ya ganta yake son kallon ta. Wasu 'yan Mata again suka shiga motar nan aka fara tafiya ,tamkar mudubi ya samu domin yarinyar ta tafi da ruhinsa duk da ba Wata babba bace dai-dai k'ofar get gidan motocin suka tsats-tsaya cikin rawar jiki su zee suka shiga tsadadden saurayin ya bisu da kallon tareda wani kwantaccen murmushi asaman fuskar sa.     Fitowa Yayi ahankali ya taka ya shige cikin gidan direct main house in  ya shiga karo suka kumayi Zee ta juya takalle shi "sorry" bece da ita k'ala ba sai kallon face nata da yai ganin yanda Tai murmushi wushiryar ta ta fito alal hak'ika duk wajen ba wace Tai mai se wan nan 'yar yarinyar ga tsiwarta na birgeshi. HAIDAR kenan mata shin saurayi d'an shekara 24 me Tashen had'uwa da naira gashi ma 'abocin murmushi sede bai da yawn magana ga Wanda bai sani ba.   Shiga falon yai yana kiran mami Wata hamtsak'iyar Mata ce ta fito fara sol me k'iba ta fito tana k'ok'arin yafa mayafi "Aa my haidar hala  ka d'auko 'yan bikin kasan matar nan tace  mu basu aron mota ko " eh" mami ai na d'auko su ma ashe anan gidan  zasuyi"? "Haidar wallahi ara sukai kasan wajen da girma kanaa ciki ko" ? .   Eh mami ba inada zani saboda yau weekend " fita mami Tai wajen bikin haka haidar ya zauna kan three seater yana murmushi don tuno irin  farfara idon da Zee ke duk da bai san name nata ba. ************* K'arar kid'a ne ya gauraye d'aukacin gidan harma da waje nan 'yan Mata suka motsa gano Zee nai a tsakiyar filli sai rawa take tanayi manyan 'yan Mata na ture ta .    Kujeru ne birjik  ga Amarya acan gefe anyi decoration en wajen su Aneesa munay ,da Zee nata giggiwa.      Agajiye Zee Tai bayan gidan neman ruwa domin tana jin kishi lokacin yana zaune kan kujera yana danna phone d'ago kan da zai ya ganota wani murmushi ya saki kan yaje ta bar gun abaya ya bita.    Wajen rawa ta shige dama gwanar iya rawa ce daga can nesa ta tsaya yana kallota sai shafa Gefan fuskar sa yake.    *6:30* Idanuwan Zee sukai tsuru-tsuru ganin Ana ta tafiya lokacin haidar ya fito zai tafi masallaci ya gano su adai-dai kusa da motar sa Zee tana ganinsa ta sunkwi da kai haidar ya murmursa ya bud'e motar yai musu alamar da su shiga,wani kunyar sa Zee ta ji yana tuki yana kallonta ya ci gaba da yi zo ku ga yanda jikin Zee ke b'aari saboda yau ne  first time da wani namji ke Mata irin wanga kallo. ******* "your name"? Shuuru basu ce komi ba, "You sitting at the right" take ya kuma watso musu tambaya munay ta rad'awa Zee yau mun kawo kammu motar nan .    Zee ta d'ago dara-daran idanuwanta Alamar tsiwa.na cinta  "suna na ZEENATU " .    "What a wonderful name "? Haka munay Tai mirsisi taki fad'ar sunanta haka sukai tamai direction har yazo unguwarsu haka ya saukesu ya tafi.    Zee ta cire ta kalmanta da duk sun sa k'afarta ta k'age ta shige gida.   Shigar ta gida ta hau basu  su mum labari sadiq dake zaune yana drawing yace" Zee amma kin kwaso kud'ii agun rawa ko"?.    "Kai an gaya ma da yanzu ce ai nadena tun a bikin karimat van kuma ba" mum tace "Zee ay hakan na keso "dariya sadiq Yayi yai Mata gwalo tareda ce Mata zasu nijer biki amma Banda ita, hade rai Tai "mum da gaske" mum Tai dariya eh mana ko kin manta saura 3 month bikin inada biki" tsalle ta daka mum" lokacin ai munyi holiday ".    "Nade gaya miki Allah ki ka kuma janyo fad'a bazamu dake ba "..    *** Haidar oh ku dakace ni ...... *©Queen



 [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: . . . *ZEENATU by Queen



 page12* ?.            ?.          ?.          ?.               ?.           ?    ?.              ?.           ?               *®NWA* *[19 sep 2016]* *Dedicated to Lubie nd bena* ******** *Haidar* kuwa tun ganin sa da zeena ya kamu da k'aunar ta, daram ta zauna a zuciyarsa yau kwana biyu kenann da had'uwar su amma ya kasa delatin inta a mind na sa sede kawai aga yana murmushi.    Yauma data kasance ranar Tuesday yana zaune kan dining yana kurb'ar tea suna hira da mami, shiru Yayi can mami tace Aa" my haidar ya naga kayi shiru"? sumar sa ya shafa. "mami wallahi mota nane ya lalace kuma injinta ya samu matsala".   "Ok ai da kai magana basai Audu driver ya kaima gyara ba" .     Tashi yai ta bishi da kallo yanda yake tafiya akasalance shiru Tai ta d'au phone nata tana waya da muta nenta .     *Haidar* D'ana ne a gidan Alhaji mai dala shahararren mai kud'i da yai shura afa'in jahar jigawa dama garuruwan dake kewayen ta ,matar sa d'aya hajiya Zahra sai 'ya'yansu 2 haidar da husna husna dai-dai sa 'ar Zee ce itama ayanzu hakan tana sa1 tana bording school,Wanda haidar ya gama university ensa a k'asar malaysia a yanzu hakan bai Dad'e da dawowa ba ,mahaifinsu shekarar sa 2 da rasuwa asanadin hatsarin mota.   Hajiya ke tafi da dukiyarsu da yake 'yar business ce sai     company sa da k'anin baban haidar ke tafi da Shi Wanda jiran haidar ake ya shiga 25 yrs a dank'a mai wan nan kenan.    ********?? Yau ta kama Sunday haidar ya makance Akan zee tunanin ta yay mai yawa new car ensa ya hau Wanda jiya aka kawo mai ita bai zame ko ina ba sai anguwar su tsayawa yai can nesa da gidan nasu .    Yana cikin motar ya fito ya duba body en motarsa, yasa T -shirt white da black jeans ga sumarasa na shining haidar kenan ma'abocin tsafta Sam atsarinsa bai San farar mace shiisa farat d'aya Zee ta tafi dashi .    Yana tsaye sai ga Zee Sun fito ita da sadeey zasu islamiyya k'ura Mata Ido Yayi daga can nesa sadeey sai June-juye  take ,Tai tuntub'e da wani dutse Zee ta jiyo "dalla kina ganin gabanki nan ta kai Mata rank'washi a kai had'e rai sadeey Tai "me nai miki ya Zee? Ba mum ta hana rank'washi ba".      "eh naji kina kallon gabanki ki asanadin kije kiji ciwo ace na barki wallahi ko  kuma ki koma Kya  tafi keda sadiq". "suna tafiya tana zungurar sadeey da gudu ta koma gida "Allah na fasa jerawa dake"     Wani juya Ido Tai "tafi nono fari yarinya dama hanani sauri kike "    Haidar daga gefe sai murmushi yake duk abinda take birgesa take.   ganin taxo dab dashi ya  tazo ta wuce ta tana mita  ya bita da Ido motarsa ya shige ya figa yabar unguwar yana tafiya yana murmushi da zarar ya tuno yanda Zee ke juya idanuwan ta.     Yana San yaga Tai fari da I'do kai Shi komi Zee Tai birgeshi take.    Gidan su abokinsa ya zarce direct dake lowcost lokacin kb ya fito zashi fita suka had'u suna hira kb ke cemai gun budrwarsa zashi nan haidar yai murmushi.    " nima de ku Dena mun tsiya na samo Wata d'anyar baby yarinyar ta had'u amma sede yarinya ce sosai bazata fi 15 yrs nd half ba" dariya kb yasa kun" dai-daita kenan."      Kb Harda buga k'afa ai" wasan yara ne wan nan ina lefiin ka nemi yar 20 yrs"      " mtws dad'ina da kai kb sai mutum ya kawoma magana ka tsaya kana dariya 15yr ai tasan so ni kam  ahakan nake Santa nid'in ai ba wani babba bane itace dai-dai ni yanzu kasan me, narasa yanda zan da Alama yarinyar ba lalle abarta ta fara luv yanzu ba wlh gashi tunanin ta yai mun yawa"     kb ya dafa kafad'ar sa "cool down haidar zanzo gida mi shawara kar kaji komi " motar haidar suka shiga suka fita.      *Washegari da yamma* zuwan zeena islamiyya ta shiga  class nasu da k'arfinta malam haruna dake classs en ya yana musu k'ari zeena ta gaidashi taje ta zauna ta bud'e Alqur'anin ta tana sauraro.     "Zeena" malam haruna yai Mata izini data iso gaban Allo haka ta taso wasu daga cikin 'yan class en suka fara sunkwi dakai suna dariya.     "Oya zeena karanto haddar da na baki ".    Bisumillah ta fara nan tafara karantowa tun daga inda ya basu haka tai ta karantowa harma ta wuce inda  yace su tsaya sai da ya tsaida ita San nan ta d'aga manyan idanuwanta ta kalli 'yai  class en   *Attakbir*yace suyi mata    Komawa Tai ta zauna . Haidar dake tsaye bakin wani super market shida kb wayar kb Tai ruri ya d'aga daga can maman sa tace yaje ya d'auko khdija a islamiyya bayan Sun gama wayar kb ya kalli haidar.     "Pls frnd Zoka mik'a Ni na dauk'o khady daga islamiyya"    Shiga motar sukai ya ja *6:00* Adai -Dai lokacin aka tashi su zeee Sun fito kubra tace "yau su wa'e an kawo hadda"   Dariya suka sa Zee dake bayan su Tai k'wafa munay tace"Zee karki Kula su "     Aneesa tace "pls Zee ki k'yalesu".    "Ay kun san bana barin ta kwana wallahi saina Tanka"    Dafa kafad'ar kubra Tai tace" kubcy kike kowa me naji kina fada"?   Tab'e baki Tai abunda" mutum yaji shinake fada".   "Wallahi yau se kin gane wa kikai wa hakan Ni kin san ba kanwar lasa bace"   Kubra ta kaiwa Zee Mari tace "kan na gane kure na ke kya fara gane naki".    "Dafe kunci Tai tabawa Aneesa qur'anin kubra batai Aune ba Zee ta kai mata nan da nan suka hau fad'a Sam Zee tak'I yarda suyi dambe sai cacar baki suke Sun cika gun.    Dai- dai lokacin wani Malami ya rabasu.      Zuuu motar haidar ta tsaya direct idonsa ya sauka Akan Zee dake ta fad'a tana hararar kubra murmushi ya saki ganin yanda Tai mai kyau kb dake kusa dashi yace" mutumin Ya tab'a Shi firgit ya jiyo.    "Gafa babyn can" nan kb ya ware Ido yana son ganin ta.    Zee dake ta had'e rai suka zo tagaban motar suka wuce haidar yace "kaga waccen choculate en itace"    Kb yace" amma fa yarinyar tayi wallahi kalarta tayi amma she's very young"                Haidar yace" bata nan da 2 yrs kaga big gal"   Kb yasa dariya na ga" yanda za ai wan nan luv" Haka suka d'auki k'anwar kb suka wuce gida....... *_Writting_* *_Queen



_* [9:24pm, 01/11/2016]



 basheer: *ZEENATU by Queenie



 page 13* *Dedicated to Lubie nd bena* *[21,Sep 2016]* ?. ?. ?. ? ? ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* Yau *HAIDAR* ke shirin tafiya China kan wani course da ze yo Akan business saboda mami so take ya fara tafiyar da harkar dukiyar sa sabili da ba Shi ya karanta ba a uni. Ba haka yaso ba saboda irin ya fiso kan ya tafi ya kafa gwabmatin sa agun Zee tuna Ni Yayi ya basar aganin sa yarinyace yana zaune kan stool yana gyara takalmin sa wani tunani yai se ya d'au phone nasa ya latso layin kb k'irr kb na guga ya d'au wayar . "Haidar ya de " "Kb ka san de jibi zan tafi China to kasan har,yanzu ban tun kari wan nan choculate en ba kaga kuma banso na tafi ban tasamma matsaya ba wallah i have gone deep in loving her". Dariya kb yasa *"HAIDAR* wan nan fa ba wani abin tashin hankali bane wan nan yarinyar she's young har kaje kadawo daram zaka ganta". "Look kb abari ya wuce Shi ke kawo da rabon wani ,idan bazaka ban idear ba pls chapter close" Ok sorry frnd yanzu ka saurareni around 6pm kaga sai muje gidan nasu ko"? "Ok tnks se yanzu kai magana nan suka kashe wayar atare *haidar* har d'an wani dad'I -dad'I yaji ya tashi ya fice side en mum nasa har wani d'an tsalle yake. ******** *ZEENA* zaune kan kujera tana gyara d'an kunnaye Wanda ta fara saidawa nasu don Allah Yayi ta akwai son taga tana sana'a irin k'Ana nan d'an kunnaye ne da zobuna Anty bara ta aikoma ta su daga kano daman Tai Mata alk'awari. Munay ce Tai sallama mum dake kitchen ta amsa tsugunnawa Tai ta gaida ita taamsa "Zee na nanan kuwa "?. "Eh munay tana nan a falo" haka ta shiga tsalle Zee Tai ta rungume munay. Da k'arfi tace "ke na fara sai da d'an kunnaye da zobe". mum dake tsakargida tace "zeena wan nan k'arar fa?ki fa nutsu na gaya miki". "Yi hakuri mum" Munay dake ta jujjuya d'an kunnayen tace "Zee yanzu kina k'aramarki zaki,fara saye da sayarwa ". "Eh mana munay to meye nikam wallahi ina sha 'awar business idan na girma kinga yanzu na samu Anty ta aikon". "Dan Allah ki kaiwa mama ta sai miki" Dariya munay tasa "wai ba afara siya bane "?. "Eh mana to zan kaiwa mama ta sai mun Yawwa kinga muje gidan Abu mai kitso dawuya kiga ba asaya ba tunda Mata na shiga ". "Eh haka ne amma da wuya mum ta barni kin san tun fad'an da mukai da zulaiha a gidan Abu lokacin danaje kitso mum ta hanani zuwa". "Zamuje ahakan Kode gobe in an taso daga islamiyya mu biya "?. "Eh hakan za ai" Taashi munay Tai ta d'au d'an kunne d'aya kan zata kawo Mata kud'in. *6:pm* ********* *HAIDAR* yaci shadda blue dark da ligh en hula da takalmi rigar iya gwiwa kana ganinsa kaga matshin saurayi ga kb shima zaune a gaban motar haidar Sun d'auki hanyar gidan su Zee. Dai-dai k'ofar gidan su Zee suka tsaya basuga kowa ba tsai kamar minti 5 sadiq dake k'ok'arin shiga gidan kb yai kiransa. Zuwan sa ya tsaya kb yace"kai dad naku na nan"?. "Eh yana nan Amma yanzu zai,tafi masallaci" suna cikin magana sai ga Shi nan ya fito. Da sauri suka fito suka gaisa nan kb ke ce masa wajensa suka zo lokacin har an kira sallah. Dady en Zee yace" ba matsala amma ku bari na dawo daga masallaci"nan haidar yace bari Muma muje haka suka d'unguma suka tafi. Bayan kamar minti goma sha suka dawo tabarma ya fito Masu da ita suka kuma gaisawa. "'Yan samari ban shedaku ba" Kb yace" eh wlh dama mu Masu son yarinyar wajenka ne". dariya dad yai "ZEENATU kenan ko"?. Suka ce eh kb ya nuna haidar "ga Wanda ke Sonta nan dama muna neman izini don zuwa gunta " "Masha Allah kunyi tunani me kyau hakan shine tsarin musulnci idan kaga yarinya to ka fara neman izini daga wajen mahaifanta kan tazo gunta". "Ba matsala gobe in Allah ya kaimu sai kuzo ku gana sai ka nemi soyayyrta". Wani Dad'i ne ya bai baye Haidar haka sukai godia sukai sallama Dadi ya shige gida su kuma suka shiga mota haidar sai dukan sitiyari yake don Dad'i Kb yace" gaskiya kama son Zee choculate en nan " Dariya haidar yasa "wan nan sunan kuma fa " Kb yace"ai ya dace da ita "..... Shigar dad gida ya lek'a falon mum tana zaune kan sallaya ita kad'ai ya kalleta yace " akwai wasu samari da suka zo mun da maganar zeena suna so to na basu izinin zuwa gobe" mum tace " masha Allah, Allah ya kaimu goben. *Washe agri* Zee na shirin school tana bakin k'ofa ta sunkuya tana d'aura sandal enta Dady ya fito shima zai fita . "Dady ina kwana" Zee ta gaidashi, "Yawwa zeena zo nan" da sauri taje ya mik'a Mata kudin mota San nan yace" anjima akwai wad'anda zasu zo gun ki " Dafe k'irji tai "dad Ni"?. "Eh ke mana kuka ta fara shikenan yanzzu su munay zasu Farai mun dariya idan sukaga ina zance". Dariya dad yai "oh zeena rigima to meye ban son shirme" Sakai Yayi ya fice inda zeena ta shige d'akin mum da gudu ta tsaya gaban mudubi tana kuka mum tace" amma zeena anyi mashirmaciya sekace Wanda in sunzo zasu cinyeki"? "Mum Aneesa da munay fa duk basu da saurayi kuma ba wadda take zance seni ace zan fara". Mum da ta rik'e Hab'arta cike da mamaki se yau na tabbatr da shirmenki Zee to ai farinjini ne to ban san shirirta kinji ,ki tashi ki tafi school" Kuka sosai take bilhak'k'i da gaskiya kirjin ta yana fat-fat haka suka tafi..... To ko Zee zata amince da soyayyr haidar ? Idan ta amince ya soyayyrsu zata kasance? Ku biyo



 Queenie don jin yanda zata kasance. *Writteen* *By* *Queenie



* *



* [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . . *ZEENATU by Queenie



 page14* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *[ 23 Sep 2016]* *Washegari!* Tun safe zeena ke kumbur-kumbure sai shige da fice take tsakanin d'akinsu Dana mum wajen uku dai- Dai Aneesa ta zo duba kayan da take sai dawa Sam tak'i sakin fuskarta ta wajensu. Aneesa na zaune ta d'aga wani D'an kunne Zee ta wapce Ni ki bani namaa fasa sai dawa jin an k'wala sallama ta shige d'aki sai Fatyce ta dubo fitowa tai jikin ta asanyaye "ke faty suwaye" "wani fa almajiri ne" nan tai hamdala ta zauna sai kaffa-kaffa take tsoronta d'aya Kar bak'inta suzo Aneesa na nan ganin 4: 00 yasa ta kwanta alamar bacci ya take ji duk Dan de Aneesa ta tafi. *4:30* Mum ta k'wala kiran Zee da sauri ta shige mum tace" Maza kije ki wanka kizo ki kwalliya kin San bak'I zaki" zama tai "mum Aneesa fa na nan yanzu so kike nai wanka nasa kaya me kyau wallah zata gane". "Ke ban San shirirta in zaki je ki wanka ki yi to meye ruwanki da ita". Mum ba yanzu fa zata tafi ba mamansu bata nan fa shiisa ta zauna" To tsaya don Aneesa na nan sai ki shiiryawa an gaya miki idan itace saurararki zatai "mum ta had'e rai Oya get out kije kona sab'a miki" jiki asanyaye ta futa sai hararar Aneesa take ,haka taje tayyo wankan ta dawo nan ma mum ta sa ta shafa mai tasa kayan ta Sa tai light makeup ,dai-dai. Lokacin akazo kiran Aneesa sallama tai ta tafi sai alokacin zeena taji nyc mum ta kalle ta tai murmushi tana mamakin ta Zuwa tai falo ta cake ta zauna haushi yasa ta tuje d'an kwalin ta wajen 5:00 Dady ya dawo ya kawo magani saboda sadeey batada lfy . *HAIDAR* Yaci wanka ya had'e ya je suka tafi shida kb zuwan su keda wuya dad na fitowa zai fita take suka gai dashi dad yai murmushi kun" dawo kenan to sannun ku da zuwa " Koma wa ciki Yayi ya kira zeena tafito ta tsaya "ga bak'inki nan jeki d'auko mayafi"ahankali ta koma d'aki. mum ta kuma gyara ta ta yafa mata mayafi "zeena na san halinki saura ki nuna kalarki ki nutsu Banda shirme ki nutsu ki nuna nutsuwarki gabansu". turo baki tai azuciyar ta tana kamar ni'yar k'arama ta dani ace senai zance nifa na tsani zan cen nan dad dake tsakar gida ya k'wala kiranta "kefa nake jira damm! Kirjinta ya buga fita tai ahankali nan ya nuna Mata hanya. soro ta lek'a ta ganosu kan baranda ta k'ofar gidansu nan taa kasa fita saboda gano su d'an matsare da tai Akan bench suna hira Komawa tai dad yace" meya dawo dake "? "Dad kace su shigo soron Ni kunya nakeji" Tsawa ya daka Mata Ni ne ma zan ce suzo kije kona Saba miki" Da sas- sarfa ta koma baya inda take matse hawaye zuwan ta soron tafi mintuna San nan ta D'an leka kanta kb ya gano ta nan suka taso suka shiga soron kanta ak'as jikin ta na rawa ruf ta rufe idonta da mayafinta. Shiru ba Wanda yace k'ala can kb yai ta Maza yace" zeena gamu bak'in ki fatan kinji dad'in zuwan mu" bata ce komi ba sewasa da take da mayafi. Tashi kb yai ya basu gu ganin hakan haidar ya shafa sumarsa ya taso ya matso kusa da ita da sauri ta matsa baya murmushi ya saki. "zeena ta d'ago kan naga face naki ganin taki d'agowa yad'an tab'a k'auren k'ofa da sauri ta d'ago manyan idanuwan ta Masu Zara -zaran gashin Ido ta 'd'oraa su kan fuskar haidar take ta sunkwi dakai inda kirjinta ke fat-fat cike da tsoro kar wasu su shigo su ganta tana zance. Haka haidar ya k'araci surutan sa bata ce komi ba se hmm Aa gabatowar kiran magriba ya kalli agogon sa ya mik'e zai tafi itama ta tashi se alokacin tad'an saci kallon sa ak'asan zuciyarta ya burgeta Musammn tashin k'ashin da taji yana yi Alal hak'ik'a tana son taji mutum mace ko namji na kamshi . "I really luv u zeena" dumm! taji gabanta ya fad'I da wani yanayi da bata tab'a ji.ba "pls say something my choculate". idan ka taba zeena lokacin zata iya runtumawa saboda tsananin yanda taji "do you love me"?. San yayyar ajiyar zuciya tai sabida tambayoyin daya wa watso Mata lokacin da ta ankaro da hon en da kb ke yi. Hon kb ya kuma matsowa take haidar ya Ankara tashi yai ya kalleta "ok bari na tafi kinji pls i need ur answer pls" ,kallon sa tai tad'an sunkwi da kai tana Allah ,Allah ya tafi. ganin ya fita ,itama ta shige gida su mum na tsakar gida kanta ak'as ta shige d'aki kallon juna Dady da mum sukai sukai murmushi dad yace " zeena rigima an girma". mum tace" ade Girman Allah ya zab'a mafi alheri" dad yace Ameeen ya tashi ya tafi masallaci. Shigar zeena d'aki ta rasa wane yanayi take ciki ba abunda take tunawa da haidar se k'amshin sa, yau jinta take kamar a sabuwar duniya take ita kan ta ji take kamar an d'ora Mata wani nauyi. Wajen k'arfe 8pm haidar ya shiga gida bayan ya aje kb a gidansu,Shigar sa gida lokacin mum na zaune kan dinning tana cin tuwon shinkafa miyar shuwaka ."Aa my haidar". Naan "mum" kitchen ya zarce hardasu d'an tsalle yana wak'a. Mum ta kalleshi tai.murmushi lalle Yayi D'an nata da labari a abakinsa ,dama can d'abiarsa ce tun yana yaro inde abin wani farin cikin ya same Shi haka zai tafi yana tsalle yana waka alamar abun yai mai. Dawowa yai ya zauna d'aukeda maltina a hannu "mum ya Sosa k'eya yau naje gidan su Zee " . "Wace kuma Zee"? nan yace" oh mum na manta ban gaya miki ba ai na samu yarinyar da na keso nan ya sunkwi da kai kuma Allah mum irin kalar da nake so". Mum tace oh su haidar ko kunyata bakaji seka ce kakar ka don gidanku Ni mece in ba fara ba ". "Mum aike daban ce " Dariya tai tana Son haidar sobada shima yana matukar Sonta. "Lalle kwa zanso ganin surukar tawa" . "Idan na dawo mum ai zaki ganta". "to Allah yasa". Haka ya tashi ya shige d'aki ya fad'a gado kawai idanuwan Zee yake hangowa ahaka bacci ya kwashe Shi tareda tunanin zeena ..... *Written* *By* *Queenie



* [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: *ZEENATU by Queenie



 page 15* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Lubie &bena* *[25,Sep,2016]* ****** Da sassafe Haidar ya tashi ya shirya da yake jirgin 1 zai hau gashi so yake yaje kano da wuri wajen 8 ya fito da jakarsa mami na zaune yaje ya gaida ta . "Aa my haidar tafiyar ce"? "Eh mami so nake naje kano da wuri don jirgin 1 ne" "Ok Allah ya taimaka yasa agama lafiy sede zan missn ka gashi husna basi Hutu ba ". Mami ay saura Wata d'aya si Hutu ko kin manta " "Hakane fa kaga shirin bazai yawa ba". wayar kb ce ta shigo adai- dai lokacin tashi yai to" mami Allah ya k'addara saduwar" mu haka ta raka Shi har wajen gate tana mai adduar kiyayewa. Shigarsa mota bai zame ko ina ba sai gidan su kb nan ya d'auko Shi. Suna cikin mota kb yace" ya kun sallama da mutuniyar "? "Aa yanzu de zamu je sai da suka biya ta super market suka lodowa Zee kayan k'walam tarkacen su alawowi da kalolin biscuits irin manya manyan nan da su turare mai da sauransu haka suka loda suka doshi gidan su Zee. Zuwan su keda wuya Zee na fitowa zata school ai tana ganin su ta runtuma aguje tana haki haidar yai murmushi, firfitowa sukai lokacin dai -dai yake da fitowr Dadyn su Zee zai,kai su faty school. ******* "Aa haidar" nan suka gaisa suka sanar dashi tafiyar haidar China sunzo sallama da Zee ne Dady yai dariya har" abada de zeena ba ta rabo da shirme ina ga ganin ku ne h yasa ta runtuma bari to na kirawo muku ita" . Kallon juna sukai Suka jin gina damotar kamar b'arauniya haka ta fito sai sunkwi dakai take dad ya zo ya wuce sukai mai adawo lafiya ganin tafiyar dad yasa ta koma soro jikinta na rawa se kallon hanya take kar ta ga idon sani. Haidar dake tsaye inda ya kafeta da idanuwansa ganin yanda tai kyau a uniform in yana wani murmushi ya tako ahankali "zeena" bata ce k'ala ba. "Ina amsata" sunkwi da kai tayi tana dariya "kinga tafiya zanyi na 3 month zanyi course na business a China San nan zan dawo pls tell me" school bag inta ta d'auko ta zaro pencil da paper . Ta tsuguna tai short note ta mik'a mai zuciyar ta na bugawa saboda yanda ta kamu da son haidar. Bud'e takardar Yayi ya k'urawa rubutun Ido ya fara karanta wa kamar haka: _whenever I see you I feel happy,seeing you is the best thing of my life I become glamorous about you, you are my lovely and good looking._ Ninke takardar Yayi yaasa A aljihu tare da mamaki a kan fuskarsa na yanda ta iya watso wan nan kalamai sanyin Dad'i yaji zai Mata magana ta shige gida aguje Juyi Yayi yad'an ya daki hannunsa ya fita yana murmushi ta gefen bakinsa kb ya kwashe da dariya idan" zaka zo mutafi to kasan kano muka nufa ka zauna tsinkar fure" ,kayan da suka sayowa Zee suka fito dasu wani almajiri suka kira ya d'auka ya shiga dashi. Haka suma suka Hau motar su suka tafi inda haidar keta murmushi duk sanda ya kafa eyes nasa Akan paper. Zee kam ganin 9 am tayi yasa ta cire uniform inta ta kwanta kayanda aka kawo Mata ta bud'e nan taga choculate jingim murmushi tai"lalle yau zan yank'wana su sadiq in bada order in anki bi aga ina Shan sweat bazan bawa mutum ba" ita kad'ai keta magana. Dad'in da t akeji haidar bazai kuma zuwa zance ba sayya dawo dukda tana sonsa ta tsani hirar nan . 12 :30 su haidar na kano ditect airport suka zarce 1 dai-dai jirgin su haidar ya tashi inda kb ya tafi ta motar haidar Wanda Shi zai koma da ita jigawa....... *After 3 week* zeena ce zaune Akan Kujera ita da su munay sunje gidan biki,ta Lula duniyar tunani Wanda kwanin ya zameta saboda yanda take yawan tunanin haidar Aneesa ce ta tab'o zeena "yana ga kin yi shin shiru munata hira kin Lula tunani" Zeena da ta yatsine fuska. "Kin san me Aneesa wallahi Ni yanzu a ban San yawan magana don Ni yanzu innaga Ana fad'a ma abin dariya yake ban saboda fad'a ai,se yara" dariya su munay sukai. "Anya kwa Zee Ked'in da baki da hak'uri kamar zazzab'i". "Uhum munay kenan ai koke yanzu kika ganni ina hakan ai kya mun fad'a da d'in ma yarinta ce ai ,kin manta yanzu mun kusa shiga ss2 daga wan nan hutun da zamu tafi ya k'are fa sai ss2 kin San me Allah in na shiga ko senai tsiya duk da ba bordin bace" " hmm adai juri zuwa tafi Zee ,Mu ai haka muke so ki dena fad'an zeena" . dai- dai time en Wata yarinya yar yabawa tazo wucewa ta take wa Zee k'afa "wash" take ta kaiwa yarinyar duka "dalla malama bakya gani ne kin taken k'afa " "Yi hak'uri ban ganki bane cewar yarinyar jin zafin da tai yasa ta kuma hararar ta "banza kawai bar nan kona mauje ki yarinyar ta murgud'a Mata baki "na baki hkr se wani masifa kinamun to karki hak'ura". Ji kaje kau Zee ta kai wa yarinyar Mari ta d'uma Mata dundu munay tace" haba Zee yan zufa kikace kin dena irin hakan" "Wallahi haushi taban,yarinyar ta tafi basu Dad'e ba saiga ta nan da Wata hamshakiyar Mata kana ganinta kaga mai naira Ganota sukai matar ta tsaya tace" nunan wadda ta dake ki nan ta nuna zeena. "Haba yarinya ya zaki kama ki ta dukanta bayan ta baki hkr"? hjia rashin kunya tai mun " badai Dad'i hakan yanzu idan uwarta ta ganki ai bazata ji Dad'i ba Ni ta bawa ajiyar yarinyar akusa dani take kinga kamar Amana taban karde ki kuma dukan ta" tab'e baki zeena tai ta juyar da kai . Matar ta kalle ta tace" Allah ya kyauta". Bayan tafiyar matar nan zeena dai sai mita take munay tace" mai hali de baya fasa halinsa Sun tafi ma bazaki hak'ura ba".......... *Writtng* *By* *Queenie



* [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . . *ZEENATU by Queenie



 page16* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *[26,Sep,2016]* Zeena afalo ta duk'a tana gugar kayanta tana wak'ar adamsy ,mum dake kusa da ita suna hira jefi -jefi "mum wai an fasa zuwa bikin ne?,nifa na k'agu" kinga munyi holiday yau sati d'aya fa " Zeena ai an fasa bikin mijin yarinyar ya rasu". Zeena ta d'ago eyya" mum Amma na tausaya Mata Allah ya jikansa. Ameen zeena amma akwai wata Jikar goggo ta birji za ai bikin ta wani satin don bakiga yanda take ta fad'a ba wai bama zumunci duk baku San 'yan uwanku ba tace lalle muje daku" Tsalle zee tayi "yeeeeh zamu k'auye Allah tunda wani satin ne yau zan fara had'a kayana, ta tsaya ta rik'e k'ugu tana tunani nan ta shige d'aki ta fito "mum kwana nawa zami"?. Dariya "mum tai to Amara sati d'aya zamii nan ta kamo hannun mum ta sa dariya wushiryar ta ta fito I" luv u mum naji dad'in sweat labarin nan". Dariya mum tai ta kalli zeena tana jin k'aunar ta aranta,haka su sadiq suka shigo ta gaya musu suna ta murna. da yamma zeena ta d'au d'an kunnayen ta tasa zumbulelen hijab har k'as ta gayawa mum zata gidan su munay. Fitar ta kam taje gidan su,munay en nan suka rankaya gidan Abu mai kitso. Shigar su gidan suka ga Mata su 2 d'aya Ana Mata kitso d'aya na jira Abu ta kalle su Aa 'yan Mata dama kuna nan"? Su zeena an girma nan suka zauna suna ta hira zeena tace dama jewels na kawo ko zaku saya masu kyau, nan matar da akewa kitso,tace mu gani karb'a tai tana ganin amma Sun kyau nawa " Zee tace" 600 hundred" matar tace tana son biyu zeena tace" akwai ma awarwaro inkina so " Ok ki bayar akawon Zaro kud'i tai,ta mikawa zeena jikin ta na bari ganin an ciniki nan suka mik'e zeena tace zata aiko a kawo Mata. Fitar su zeena tace "wayyo dadi"munay tace ba na gaya miki ba gashi kinyi ciniki nan suka rabu zeena tai hanyar gida Shigar ta ko cire hijab batai ba ta d'auko,awarwaro leda 2 ta bawa sadeey ta kai . Mum dake karanta hisnul Muslim ta aje gefe tace " zeena wan nan rawar jikinfa" "Mum wallahi kinga daga fita ta har ansai jewels yanzu na bada sadeey ta kai musu awarwaro . Sadeey ce tai sallama a gidan Abu da sauri taje ta amshe ahankali ta ce "ke nawa tace miki "sadeey tace 500 hundred " ok Yawwa sadeey Komawa ciki tai tace wa matar 600 hundred ,sadeey da bata gama fita ba ta jiyo aikwa da gudu ta arta ta shiga gida tana haki "ya Zee ta k'wala Mata kira Zee tace" meye"?. Sadeey tace" wallahi Abu naji tace 600 bayan na cemata 500". Zee tace" jar uban can lalle ma matar nan". Zarar hijab inta tai ta lallab'a lokacin mum na toilet ta fice sauri-sauri take har taje gidan Abu zuwan taga har matar ta tafi sai d'ayar. Zeena tace Abu Kiban kud'i nan ta mik'o dubu d'aya Zee tace" saura dari biyu" "ke ban san rashin kunya Ni me zan da kud'in ki naga d'ari biyar kika ce ". "Eh na sani amma ai 600 ki kace ai labari yaje mun don haka kiban ". Dama zeena baki da kunya "? "Nifa ba rashin kunya nai ba taya zan bada kaya ki K'ara alhali ni bake na bayar akawowa ba" "To Mara kunya ba custormer ita ce ta saya ba" nan ta wulla Mata naira d'ari tace" kuma wallahi ba zan bada dayar ba ". Zee ta d'auka tace" akwai Allah,kuma Nayi mamaki tai ficewar ta. Abu ta tab'e baki yarinya k'arama dake sai tsabar son kud'I tai taki,Ni



 Nace su Abu de aji tsoron Allah. ************** *China* Haidar kwance Akan kujera yasa rigar sanyi saboda sanyin da ake rik'e yake da littafi yana dubawa ajewa yai gefe ya Lula tunaninta Tunda yaje yau one month kenan baiji muryarta tsaki yai ya fad'a afili rashin waya,laptop ensa dake gefe ya d'auka yai wa kb msg ta email ya tura kan ya saiwa Zee waya ya kai Mata don suna gaisawa bayan ya gama aika sak'on ya koma ya kwanta yana lumshe Ido ya kagu ya koma 9ja,haidar kenan kowa yabar gida, gida ya barshi lol... Kb ne tsaye a k'afar gidan su Zee yai sallama dady ya fito lokacin da sassafe ne da yake Ana Hutu duk yaran na gida suka fito shida sadiq gaisawa sukai inda kb yace " dama haidar ne yace abawa zeena waya za suna gaisawa" "Eyya Dady yace sede Ni banso Zee ta rik'e waya yanzu,har se ta gama secondry saboda rawar kanta amma ba matsala tunda yana wani garin ,kuma gaisawa zasuna yi karba yai da godia . Da gudu sadiq ya shige gida Zee" wallahi kema kin kusa fasowa gari naga an kawo miki waya". nan ta doka tsalle Allah" swt bro inde kwa hakane Allah sai na baka 200". Haka Zee tai ta murna tana jiran shigowar Dady amma shiru har akai azahar la 'asar gashi magriba ta k'arato . Zee sai kallon k'ofa take nan tace dama nasan halin sadiq akwai k'arya. Koda Dady ya dawo da dare tanaso taji ance Zee tazo taji shuru haka ta hak'ura ta kwanta Hhh Zee kenan.......... *Written* *by* *Queenie



* [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queenie



 page17* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to bena &Lubie* *[28,Sep,2016]* *9am* Zeena ce zaune a kitchen tana soya musu wainar fulawa kallon su sadiq tai duk sun tsaya Mata akai tace"dallah malamai kun mun duhu aka sadiq ya had'e amma dai ai nine zaki sakawa yanzu ko".? Zee tace faty zan sawa saboda ita ta yan kan Albasa daga ita sai sadeey ita kuma ita ta d'ebon mai sai kabari Kaine ak'arshe bece komi ba ya juya ya fita. D'akin Dady ya shiga yana zaune ga kayan breakfast ensa agefe sadiq ya gaida Shi " Dady". "naam sadiq" . "Zeena ta sakawa kowa waina bandani wai nine ak'arshe". "Jeka kirata" da sauri yaje ya tsaya "Zee kizo inji dady".da sauri ta d'ago "Kode wayar ze ban"? sadiq yace" ke kika sani"tashi tai ta shiga falon Dady ta tsuguna "Dady gani". "Yawwa me sadiq yai da baza a bashi wainar ba"? "Dady wallahi ko cokali kace ya d'auke bazai ba" "ai kinga namji ne se hkr yanzu de ki bashi" "to Dady". Har ta kai bakin k'ofa Dady yai kiranta Komawa tai ta tsuguna nan ya d'auko waya sabuwa dal a kwalinta k'irar c2 jikinta na rawa ta amshe Dady ya kalleta " zakuna waya da haidar shiyace abaki ,Banda shiririta inde naji wani Abu sena k'waceta" "Insha Allahu Dady zanyi abunda kace". "Masha Allah" cewar Dady. Da sauri ta fita tai hanyar d'aki "sadeey tace zeey kizo ki cigaba mana muna jira" "ku k'arasa man"mum dake d'aki "zeena kije ki k'arasa musu kona k'wace wayar donni banso ya baki ba" cikin sauri ta jona charge ta fita don k'arasa musu. *After 3 hours* Mum keta kiran zeena bata amsa ba ta kurawa waya Ido tana latsawa, seda ta kuma kiranta San nan ta d'ago ,"gani mum" fita tai mum ta mik'a Mata salak don ta yanka tana cikin yankawa kirrrrr ringtone en Nokia ya tashi. "ba wayarki ake kira ba ne zeena"? "bande sani ba" "jeki duba tashi tai Kafin taje wayar ta tsinke again aka kuma bugowa ahankali ta d'auka ta Kara akunne, voice en namji taji "who on d line" ?. tsaki tai zata kashe wayar don taji ba ai magana ba "my choculate I really miss u" murmushi tayi se alokacin ta gane, gaidashi tayi daga can yace "zeena kina tunani na kuwa"? Murmushi tai "ina tuna ka man" . "Kunyi holiday ko"? tace eh "tom idan kun koma class nawa zaki shiga"? murmushi tai wushiryar ta ta fito ,"ss2 zamu shiga". Zama tai kan kujera ta lumshe Ido yace "zeeta Kice na fara shiri" bata gane me yake nufi ba tai murmushi haka de sukai ta hira nan tace" mum na kirana" badon yaso ba suka rabu . "ki kularmun da kanki kinji tawan". nan tace" Insha Allah" haka sukai ta waya sukai sallama suka rabu. Kwanciya tai kan kujerar tana murmushi,jin alamun mum zata shigo yasa ta aje wayar tai waje. *Bayan kwana 2* Yau ta kama talata yau su zeena ke ta shirin tafiya birji wajen k'arfe 12 Dady yaiyo musu shatar mota suka loda kayan su mum zeena sadeey sadiq da faty suka d'uru amotar ,sai wajen 4 sukaje k'auyen. Zeena tai mamakin ganin yara na bin motar su ak'ofar gidan goggo suka tsaya firfitowa sukai aka aje musu kayan su da gudu wani saurayi yazo ya ya kin-kimi kayan mum ta kalle Shi "kar de ace yahya ne"dariya yai ya sunkwi da kai "eh nine" haka ya loda ya shige ciki da su, su Zee suka rufa mai baya. Goggo dake kan-karar goro ta d'ago kai" yahya ina zaka da kayan nan" d'agowa yai yace" mutan birni ne fa ". Dede lokacin su mum. Suka shiga "goggo tai ,murna da ganin su abinci aka zubo musu sukaci goggo na kwasar zeena suna ta dariya. *Da yamma* Amarya ta je gun goggo suna zaune Ana ta hira su Zee Ana b'arar gyad'a haule ta shiga goggo na ganinta tace "Yawwa zeena ga Amaryar nan kince baki Santa ba". Bud'e baki tai kai" goggo yanzu wan nan 'yar fificiyar za a aurar." Goggo tace "kinci gidanku Zee yanzu wan nan zabgegiyar kina ganinta haka shekararta goma sha uku kuma an aurar da shad'aya ma ak'auyen mu nan na birji ,danke kin gansame kamar ki birjik har da masu 'ya daya". Zee tasa dariya kai goggo shekarata fa 16 ace nai girma ". "To ay k'auye da birni ba d'aya ba. Haule data zauna ta gai dasu goggo tace haule taja Zee suje inda 'yan matan suke. Tashi tai suka fita se kallon haule take da mamaki haka suka shiga gidan da yan matam suke zeena tagan su duk bazasu.wuce sa anin haulen ba se wasu guda 3 kamar Zee da Alama da auren su. Haka Zee ta zauna sai ya tsina take ita ga wayayyiya 'yar birni C2 enta ta d'auko sai daddanawa take se jiyowa suke suna kallonta don ta basu sha awa. Sai wak'e -wak'en su suke ganin ta gaji da zaman gun ta fita tai hanyar gidan goggo sai kallonta samarin k'auye suke . *8:pm* Suna zaune birjik a tsakar gida anata hira yaro yai sallama " wai bak'uwar 'yar birni tazo". Goggo tace " injiwa"yace inji mutari ". "Kace tana zuwa" ke zeena kin goshi daga zuwa anfara sallama tashi kije" Zeena ta kalli mum ta gyara zama "gaskiya Ni goggo ba zani ba" "Dan k'aniyarki ki tashi kije" ganin tana ta magana yasa zeena ta d'au mayafin ta tai k'wafa Wallh",zai gane kurensa ne besan wace zeena ba".sai k'un-k'uni take haka ta fita .... ...to ku dakaceni fanz ina busy ne ga wan nan na yawa. *www.Queen



* *Writting* *By* *Queenie



*?? . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . . *ZEENATU by Queenie



 page19* ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *1,Oct 2016* *Queen



* ******** *After 3 month* Haidar ya dawo daga tafiyar sa inda bayan dawowar sa bada da d'ewa ba mami ta zaunar dashi ,duk wani business nasu datake sawa Ana juyawa ta bashi San nan company ma ya koma hannunsa shike juyawa . Yau data kama ranar Saturday zeena ce sanye da dogon hijabin ta tana tafiya ta shawo kwanar gidansu taga motar haidar nan 'kirjinta ya bada damm! Tun daga nesa ya ganota yana cikin motar sa yana danna phone murmushi yai ya kalli side en window sa daf dashi ta k'araso ta D'an saki murmushi bud'e murfin mota yai ya fito sunkwi dakai tai ta D'an juyata kalli hanya kamar a tsorace ,kallon ta yai yace to" ko har yanzun kina jin kunyar a ganki kina zance"?. hararar sa tai ta kau da Kai daga can nesa ta ga no Aneesa na tawo wa ai da gudu tai cikin gida dariya yasa ya jingina da jikin motar. Da sallama ta shiga mum na wa sadeey tsifa tace" ke kuma kamar an jeho". "Mum wallahi Aneesa Ce ke tawo wa banso tagan ni Haidar ne yazo". Tsaki mum tasa, ni" kam naga randa zaki deina wan abun zauna karkii fita ,kiga idan ita Aneesar ce zata saurareki ma". Shigowar Aneesa da sallama mum ta tsai da magana gai da ita tai nan mum ta k'walawa zee kira fitowa tai da hijab Aneesa tace to" mantau kud'inki kika manta mik'a Mata tai ta karba,ciki tai,zata koma zee ta jawo ta Allah sai kin rakani" ,zee tace" ke nak'I" ******** "To kin karb'e kud'i kuma baza kizo ko rakani ba " "kallonta tai tace nan da nan sai na raka ki" ,ganin mum na hararar ta yasa tafita rakata haidar na tsaye suka fito zee ko kallon sa batai ba tad'an taka ma Aneesa. Dafa kafad'ar zee Aneesa tai zee kin San me" wallahi wan cen saurayin ina son namji irinsa Allah da zai ce yaana sona zan amsa"wani kallo zee ta aikawa Anee ta tab"e baki. Zee tace" ai na rako ki sai ki gaba" dariya Anee tasa ta juya zee kam kishi ne ya turnuk'e ta saboda haushi da tazo sai da ta harari haidar murmushi yay yasha gabanta sarauniyar" Mata da alama yau nai Lefi ko"?. "Eh" kawai tace ta juya ciki ba yanda ya iya haka ya tuka motar sa ya tafi. Shigarta mum ta daka tar da ita . "zauna nan zeena,wai mesa ne kike Abu tamkar bagidajiya Mara wayo sai kace 'yar k'auye meye don an ganki kina zance "to dai ki gyara abari dai ya wuce shike kawo da raban wani,duk da nasan hakan da kike shine dai-dai tunda dai karki saki jiki gwanda kina kamewa ,to Amma kin san dai dole ku fahimci juna kuma nan ce hanyar fahimtar kuma naga abun naki kamar da wulak'anci. Aciki ". "Nifa mum na tsani zance kawai ace mai ya daina zuwa sai na gama sec school kinga saura 1 yr fa". Mum tace" Sannu to yanzu muke so Dan haka karna K'ara jin bakin ki wai bakin san Allah ke tsara wa bawan sa rayuwa ba, to ke yanzu,Allah ya tsara miki in Banda abunki zamanin nan yanda 'yan Mata ke neman mijin Ido rufe ,ke da Allah ya bawa kuma kike shirme, rai-rai nan inya bugo waya kuke dashi har dasu dariya amma duk randa yace zai zo tun safe zaki hau kumbura, Ni wallahi har mamaki kike ban da wajen fad'a ne da fushi kinfi kowa amma mutum na son ki kina shash-shareshi ,nan nan wan cen satin daya zo saboda ganin sagir kika k'i futa haka ya gaji ya tafi kanki farau"?. to" in ba a fahimci juna ba ta taya zaku tan -tance halin juna"? "Mum kiyi hkr na daina". "A to kima ci gaba idan wani Abun yake miiki ai seki fad'a". Ni mum ba abunda yake mun". To daga yau karna K'ara jin hakan idan yazo kuka gaisa kuyi zance yanda addini ya tsara,tunda dai bayi miki shiriritar soyayya yake ba irin ta turawa". Jiki asalub'e ta tashi ta shige d'aki. ****** Haidar dake parking motar sa a wajen aje motoci ya fito ,husna ya gani da sauri tazo ta rungume Shi "ya haidar wlcme" "Meya dawo dake gida husy "?. "Uhum ya haidar akwai labari zo muje ciki na baka don wallahi bazan koma ba" Dariya yasa langwai kawai saura naga 1 yr ki gama amma kin kwaso jiki kin dawo gida. Mamin su dake zaune kan kujera". Tace Yawwa" haidar dama Kai nake jira kaga yarinyar nan wai don wata ta tada aljanu to aranar basi bacci ba shine cikin dare tazo,kan husy ta tsaya ganin hakan yasa ta yi ihu shine sai ga 'yan kwanar su,suka tashi suka hau dukan ta ita kuma daya ke ba k'arfinta bane na aljanu ne yasa tai musu duka har taiwa wasu targad'e wai shine akai suspension en su na sati d'aya ga ta nan wai baza ta koma ba." "Wallahi mami da gaske nake aje atambayo a school, Yawwa kuma ga matsalar gardi da yake haurowa Ni kam bazan koma ba kawai akaini wata school en na k'araasa aji biyar ena da shidan" Haidar yace" inma k'arya kike toya za? ai gwanda ma ki dai na bording en ki dawo day kinga mami ma taji Dad'i" . "Mum ta kalli haidar to hakan yai kyau , wai Ni ya zancen yarinyar da Kai mun". "Sosa k'eya yai zeena tana nan wallahi". "To so nake manya su shiga ciki ,to wai Ni kamar wa take ne "? Mum bazata fice kamar husy ba"mum tace eyya to a hakan manya en sa shiga ciki inyaso sai abari sai ta gama sec ayi biki, Don so nake Kai auren hankalin ka yafi kwanciya". Tashi yai ya d'an juya yana murmushi husy tace" yaya bari Nazo naga pic nata ko me kyau ce". D'an tsalle yai kamar mai wak'a mum tai dariya naga dai randa zaka daina wan nan tsalle duk yayin da Abu yai ma Dadi". Fita yai side nasa yana K'o k'asan kiran zeey... *Writting* *by* *Queenie



* . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queenie



 page18* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Bena &Lubie* *[28,Sep.2016]* Fitar Zee muntari ya washe wak'ora ya gyara tsayuwa "lalle na yarda da maganar tsalha da yace Wata tsaleliya tazo daga birni". Kuma gyara tsayuwa yai yace" wato Ni in nan in kinga yanda matan birji ke sona zaki mamaki, to amma tashi d'aya na ganki na yaba Allah kuwa" Zee ta harare shi " ka gama" "Ni zan koma"Ganin Zee zata koma yasha gabanta ya mik'a Mata leda ga" wan nan tsiren d'an kurma ne na sayo miki duk k'auyen birji Babu tsiren daya kai shi nan kuma k'wai dafaffen ne na zabbbi ,Sanin ku 'yan birni ba kwa rabo da son kayan Dad'i". Hararar sa tai ta shige gida ko zama batai ba wani yaro ya shigo da ledar ya mik'a aje wai gashi na bak'uwar birni ne". Goggo ta amshe ta bud'e lalle Zee kinga abinda nake fad'a ko. K'wan kawai Zee tachi . *Washegari* Aka fara gudanar da biki da yamma aka ss amarya alalle da yamma zeena anci kwalliya wajen bikin ta tafi zeena sai yanga take ,samarin k'auye sai kallon ta suke dai-dai zata shiga gidan ta Tarar da wani saurayi da Wata yarinya suna zance kallo ya k'urawa zeena yarinyar tace" tsalha me kake kallo"? yarinya tabi zeena da Ido Dan" kaga 'yar birni shine zaka shareni". "Ke bintalo yi mun shiru wayak'i kyau". Gudu ta falfala tana kuka ,da yake inda ake sa lallen irin gidan gandu ne me big soro Zee tsaye a soron tana gyarawa faty D'an kwali shigowar yarinyar. Yasa ta tsaya. "bak'uwar birni wallahi baki isa ki k'wacen saurayi ba". Zeena dariya tasa yanda taga tsigigiyar yarinyar na tsalle tana fad'a. "Ke bar nan kona kwad'eki,Ni sa arkice"? Yarinyar tace Kodan kinga kinsa kaya masu kyau wlh tsalha nawane" Mari Zee takai Mata yarinyar ta Dafe gun "wallahi bazan yarda ba" Haladu dake shiga yace "ke bintalo dama ba kida kunya bar nan kona mauje ki haka ta fita Zee tai tsaki ta shige ciiki . *8:pm* Su mum suna tsakar gida sai hirar bikin suke,wani yaro yazo "wai bak'uwa tazo" Zee ta tashi ta d'au mayafi . Ganin su tai su 2 a tsaye kowanne ya juyawa d'an uwansa baya sai data tsaya ta sha dariya San nan ta kunna tochligh take suka wai go kowanne ya tawo. Tace tare" kuke ne" ?suka ce Aa d'ayan ya koma baya. Dayan ya matso "wato suna na Haladu nasan zaki gane ni" tace" eh dama gani nai duk k'auyen nan tun zuwan ki kin haskaka to shine naga ban k'asa agwiwa ba na taho yanzu de kiban izini na turo" Dariya zee tai "daga ganin sarkin fawa sai miya tai zak'I" dariya yai yana kad'e k'urar k'afarsa aikece en daban ce" "To na sallameka kaga ga wani na jira fita yai yana washe baki. Haka d'ayan shima ya matso ya washe baki "zinaru" zee tace" ba sunana zinaru ba". yace to "nide suna na tsalha" kai bakai ne saurayin bintalo ba".? "Kai-kai Ni Mezan da.bintalo kullum jikinta k'ura ,ai yanzu se ke". "Tsalha to aini kaga tafiya zan". Dariya yai Ai" zan Biyoki garunku". "to tsalha Ngd" sallama sukai ta shige ciki. Dariya take tayi tana bawa mum labari ,suna dariya wasu yarane su 2 suka shigo d'aya d'auke da k'warya, d'aya d'auke da goro da k'uli-k'uli . Me k'warya yace wai gashi nono ne inji tsalha. D'ayan me goro yace gashi" inji haladu abawa zinaru." Dariya zee tasa ta salla mesu . *After 3 days* An gama biki ansai Amarya gabanta dake nan birjin ,su zeena nata shiri zasu tafi lokacin 6 dai-dai na yamma zeena ta fita gari ya wata wa ,muntari, tsalha da haladu na tsaye Abakin bishiya suna hira gamai rake agefe yana sayarwa . Daga can nesa tsalha ya taso "A yar gayu ina zuwa haka" ta bud'e baki zatai magaana haladu da muntari suka zo suka tsaya kowa yana so zee ta kula shi ganin ta d'auko waya tana dubawa muntari ya kama kwalar tsalha. Wacce na keso zakazo gunta,haladu ma yace ai" wai duk son ta kuke ne" take suka hau fad'a sai kumfar baki suke. Zee kam juyawa tai tai gaba tana dariya da mamakinsu. Tube riguna sukai suna ta dakuwa sai da wasu dattijai suka rabasu suka tambayi ba asi nan kowa ya fad'a. "To Banda abunku yarinyar daba nan take ba daga zuwa sai ku hau shirme bayan tafiya zatai haka kowa yasa rigarsa yai gaba zee kam tafiya gida tai tana basu Labari. *Washegari* Zeena suna ta shirin tafiya wajen k'arfe goma akayo musu shatar mota sun fito zasu tafi sai ga muntari da haladu sunzo kowanne da manyan k'warya cike da k'wan zabi dire wa sukai muntari yace" zinaru ga tsaraba nan hakama haladu. Godiya tayi musu nan goggo ta d'au kwarya d'aya aka shiga da d'aya zee ta d'aga musu hannu sunyi cirko-cirko kamar za suyi kuka sai suka bawa zee tausayi. Mota ta ja taga 'yan matansu muntari na tsalle suna murna kan ta tafi dama duk sun juya musu baya. Haka suka ja Sun kusa zuwa tasha tsalha ya kwaso aguje zee ta ce da driver ya tsaya tsalha ya k'araso yana haki zinaru" ban san zaki tafi ba ya d'aga hannu yace "wayyo Ni" mum tai dariya zee tace" hak'uri zakai tsalha tafiya zami". Kaji masu rai guda biyar ya mik'o "gashi tsaraba ba yawa don Allah zinaru kiban kwatan cen gidan ku" . Driver ne ya karb'i kajin yasa a bayan mota . Nan zeena tace" jigawa dutse shine garin mu " "To zinaru nagode wallahi zanzo" ya washe baki sukai sallama ya tafi. Mum tace" Ni zeena wai ina kika samo wa'yan nan mutanen ne"?. zee tace wallahi" mum tun zuwana garin suka nacen, kawai de don bakyau,wulakanta mutum ne" ,mum kin san Ni ban san zance nake ba amma wallahi dariya suke ban." Mum tace" to Ai gwanda da aka rabu lafiya ,haka motar taja sukai hanyar jigawa dutse ... nima na aje Alk'alamina don na huta luv u o my Tnz.... *Nayi muku wan nan ne saboda gobe bazan Sami damar typing ba saboda ina da Abubuwan yi ,kusaurari page19 Ranar Friday idan mai kowa mai komi ya kaimu taku Queenie????????* *Queen



* *Writting* *By* *Queen



*?? . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queenie



 page 20* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *[3 Oct 2016]* Haka rayuwar zeena taci gaba da tafiya inda ayanzu suke shirin shiga ss3, girma sosai zee tayi tazama cikakkiyar budurwa kyawunta ya fito rad'au skin enta mekyau fuskarta sid'ik no pimples duk Wanda ya ganta sayya K'ara saboda tana da structure me kyau, ta b'angaren halayya kuma ta dai na fad'a ko a school, sede har yanzu tana da saurin fushi sosai in aka tab'ota ,yanzu ta dage karatu a islamiyya don sun kusa sauka shiisa ma duk wasu abubuwan ta rage haka aboko shima . B'angaren haidar kuwa tunda mum tai Mata fad'a ta sake yanzu zuba soyayyar su suke tamkar sa hadiye juna don hatta su Aneesa da Munay sun sani sabili da haidar ya tab'a zuwa suna cikin hira su munay suka zo bayanda zatai haka ta gabatar dasu as k'awayanta. Su Anee sun mamaki haka su kai Mata tsiya suka k'yale. ********* Yau data kasance Saturday Yau iyayen haidar zasu zo don asan dasu a kuma tsai da magana, da yake ba Maza ne zasu zo ba Mata ne ba ai komi ba ,Amma duk da hakan mum sai da tai musu cake me Dad'i da soyayyun Kaji. Zeena dake dan na waya don ta samu cigaba yanzu Samsung take rik'ewa tace " mum waina ba kawai zuwa za suyi asan dasu ba Amma naga sai soye- soye ake"?. Mum tace" yo don zasu zo ay karrama D'an Adam ne Wanda ke son naka aiya gama ma komi". Wajen 5 suka zo gidan baban haidar da wan babansa da k'anin mami an sauke su cikin girmamawa da mutunta juna an kawo musu ruwan sanyi da zob'o drink mai sanyi yaji kayan kamshi su citta da flavour. Haka suka sha suna s hira wan baban haidar yayi gyaran murya" wato Munzo akan maganar haidar da yarinyar wajen ka to da zamuzo ne kawai don tambaya Amma yanzu inda yarda zamu bada kud'in zance " dad yace Masha Allah hakan yayi Allah ya sanya Alheri nan suka bada kud'i dubu dari kud'in zance haka suka sha hirar su da zasu tafi aka had'o su da soyayyun kayan da mum tayi. Bayan kwana 2 haidar zaune ad'akin sa shida kb yana nuna mai irin ginin da zai daga su zauna shida zee, kb yace "gaskiya kana k'aunar baby en nan koda yake tayi ne Amma kamata yai kabari sai nawa yazo sai mu had'o muyi". "Haidar yace tafi can sai aukin duk bidurwar daka gani kace kana so Amma har yanzu Kaki tsaida d'aya" Kb yace Ni" ai se fara kaga kuma duk yawancin 'yan matan nawa bak'ak'ene " haidar yace" to ka zab'a aciki man". kb yace Ayni" fara ko yaya take ita zan aura . In ma bak'ar ce sede en me kyau ce kamar zee inka". Haidar yace to" meye da bak'ar adduar zabo ta gari da farar da bak'ar duk d'aya suke" kb yasa laugh to" Allah ya zab'a mai kyan hali Da dare haidar na zaune kan dining husy na karanta novel mami ta kalle Shi "my haidar tunda an engagement inku da zeena ya kamata ka kawo mun ita na ganta ko yaya kace"? "eh haka ne mum Yau ds anjima zan je side na su sai nai Mata maganar weekend kawai sai ta zo ". Husy ta mik'e Kai" Amma naji Dad'i zanga matar ya haidar Allah yasa de me kyau ce", haidar ya harare ta "tafi ki kyau fa kawai fari kika fita. Husy "zadai muganta". *Da yamma* Haidar yaci wanka wajen 5 ya cale da yake zan cen yamma yake tunda dadyn zeey yace mai yana zuwa da yamma kb har tsiya yake mai ,wai ai hirar yamma ba dad'I. Zeey ce ta fito sanye da atampha blue tai kwalliya bakin nan yasha white lips ga hanunn nan yasha kunshi sai tashin k'amshi take kafe ta Ido yai ganin yanda take tawo wa da salon tafiyarta murmushi tai tai farrr da Ido take yaji wani sanyi tsayuwa tai tace" haidar barka da zuwa". nuna Mata gaban mota yai don ta shiga juyar dakai tai "no bazan shiga ba ai kasan bana hira agaban mota" fitowa yai "tuba nake sarauniya" juya wa tai ya bita abaya . Zaama Sukai inda suka Saba zama ta kawo mai abin motsa baki kallon ta yai "ZEENATU." "Naam dear na". "wallahi har na k'agu ai bikin mu cuz kina kasheni da soyayyrki I really luv u Musamman idan kika mun fari da eyes naki se naji tamkar nai hug enki" Murmushi tai ta d'ago Ido ta kalleshi nan suka k'urawa junan su Ido suna murmushi . "My choculate mami na nason ta ganki yanzu ya za ai zaki je"?. Sunkwi dakai tai "dear zanje man Amma fa inajin kunya but zan sanar da mum if ta amince zanje" "Ok sai ki gayan ta waya pls karfa ki manta" haka suka sha hirar su Ana kiran sallah haidar ya tafi yana mai missn choculate en sa . Zee data shiga gida tai Alwala tai sallah ,tana idarwa wayarta tai K'ara ganin kiran haidar yasa ta D'an murmursa ta Kara a akunne. "Dear na har kaje gida " daga can yace "naje har na dawo daga masallaci kawai na bugo ne na k'arajin sweat voice naki" . Murmushi tai mai sauti yayin da ta D'an kwanta "nima tun d'azu kake mun gizo murya ta rage "haidar na you are the twinkle of my eyes the smile on my cheeks the joy of my face without u I 'am incomplete". Jan numfashi yai ya furzar da iskar bakin sa I luv u zeena" shuru Sukai sai numfashin su dake Kai kawo" k'arfin hali yai yace" kide sanar da mum kan maganar zuwanki gun mami" . "Ok no matsala" Atare suka kashe inda zeey ta manna wa wayar kiss ta tashi ta shiga D"akin mum ta zauna bakin gadon tace "mami kinji wai hardar zan je gidan su na gaida mamin su " Mum tace anya" kuwa Nifa duk ban San irin wan nan kawai abari sai kinje can ta ganki " zee tace mum" karya ga kamar wulak'anci" "Aa bawani wulaknci ai hanyar lafiya abita da shekara inma zan barki sai dai sadeey ta rakaki". "To mami hakan ma yayi bari nai mai waya ". Tashi tai ta fita Nima na dakata anan. Ina Baku hkr fans rashin ganin ZEENATU da ba kwayi. Kullm wallahi abubuwa ne Sukai mun yawa Amma Insha Allahu ayanzu zakuna ganin sa akai -akai. *Written* *by* *Queen



* . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queenie



 page21* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *[4,Oct 2016]* *Queen



* ******* Yau zee zata gidan surukai 4 dai -dai haidar na k'ofar gidan su ,waya yai Mata zee na zaune sai k'alk'alar face take ganin kiran haidar yasa ta d'auka cikin salon dake rikita haidar tace" my man har ka iso"? Daka can yace gani a k'ofar gida ku fito". Bayan ta kashe phone en ta yafa mayafi tai tsaki "dallah sadeey ki fito sai wani Lak'ai -Lak'ai kike". Daga can cikin d'aki tace" gani nan ya zeey". fito wa tai suka jera mum na musu fad'an kar su Dad'e. Fitar zee yasa haidar fitowa ganin bala'in kyan da tai ta nad'a lafaya red me ratsin black tasa dogon takalmi black da bag blag tai balain kyau shashan cewa yai yana kallon ta sadeey nata gaida shi Bai ji ba tsaida zee tai mai magana San nan ya Ankara. Gaban mota ta shiga sadeey a baya haka ya jasu suna tafiya suna hira ina rabi kallon zeey rabi kallon titi don ta tafi dashi ainun. dai-dai supermarket ya tsaya ya shiga ya sayo atampha da turare ya dawo ya aje Mata kan cinya "gashi nan ki bawa mami in Kinje godia tai suka ja. Dai-dai round da zai Kai su unguwar su haidar idanuwan zee suka gano Mata tsalha da jaka aka an sauke Shi a adaidaita sahu Dafe kirji tai ganin sai tafiya yake yana kalle -kalle sunkwi da Kai tai ganin ya tsallako side da suke haka ta duk'a har saida aka basu hannu, mamaki take ganin tsalha a dutse Kode wajenna yazo, Kai bazai yiwu ba Yau wajen 5month da zuwan mu k'auye yaci ace ya hak'ura ya manta da Ni Amma dai ba lalle bane haka tai ta zancen zuci . Sai da haidar yai Mata magana San nan ta d'ago ganin har sunzo nan ta sunne Kai suka shiga ciki da yake a harabar gidan yai parkin ,da gudu husy ta fito tana Juyi "oyoyo Antin mu" murmushi zeey tai. Bayan sun shiga ciki zee taja lafaya inta ta rufe fuskarta har k'asa ta tsugunna kan carpet mami ta fito daga side nata hannuwan ta yasha zabba tasa wani d'anyen less hakinmce wa tai kan 2 seater kallon sadeey tai. " 'yan Mata ya sunanki" sadeey ta fad'a husna ta shigo da try na lemu da dambun kaza ta aje bakin ta d'auke da murmushi. Ta kalli mami. "Mami gafa matar ya haidar en ta Nuna zeey data sunkwi da Kai mami tai murmushi . "zeena Ni ba a surukan ta ka dani bud'e idonki na ganki mugaisa". Da k'yar ta bud'e fuskarta suka gaisa tsai mami tai ta tsaya tana kallonta azuciyarta tana tabbs ta San fuskar yarinyar . Da girar da idanuwan ta tafi ganeta, nan da nan ta tuno da rashin kunyar da tai Mata ji tai haushi ya ishe ta don kar suga wani abin tai murmushi "Masha Allah haidar ya iya zab'e Allah had'a kanku tashi tai ta haye saman bene, nan husy ta zauna sai kwasar hira suke da k'yar zee ta D'an sha ruwan da lemon. wajen 6 haidar yace su fito mik'ewa sukai mum ta sakko da leda a hannu cike taf ta mik'awa sadeey da k'yar suka karb'a husy kam kamar karta bar zeey don ta ganta mekyau kuma dai -dai age inta haka ta raka su har bakin mota suka tafi suna tafiya haidar na Satan kallon zee,kallon zeey yai yace" "Zee wallahi ina son mami na don bakiji dad'in da naji ba ganin yanda kika girmama mami gashi itama ta karb'e ki hannu bibbiyu ,inde mutum na so mu shirya dashi to yaso mami na cuz bani da tamkarta aduniyar nan". zee tace" tabbs uwa tafi gaban hakan" Ana kiran magriba ya Aje su. ******** Husy ta shiga akin mum ta zauna kan stool "mami wallahi budurwar ya haidar she's so fine & friendly kinga har mun saba wallah ta had'u ". Mami ta tab'e baki "ina yarinyar Dana tab'a baki alokacin Dana je bikin gidan d'an azumi? to itace wadda ta daki wata yarinya nai Mata fa a ta tab'en baki tana neman mun rashin kunya". Husy tace "dama itace tab! Amma dai mami kiyi hak'uri yanzu surukar ki ce ". "Tafi can Ni yarinyar ba taimun ba da zaibi ta tawa daya rabu da ita". Mami kema kin san haydar inya k'wallafa rai a Abu kiyi hkr, Amma naga mum ai an Dad'e da bikin ak'alla za ai shekara aya da rabi kinga alokacin da yarinta akanta pls mami kiyi hkr". Tsaki tayi tace" rufen baki kinji ko kinji Nace wani abin". Asanyaye ta tashi ta fita . *************** Bangaren su zeey suna zuwa gida sadeey ta bud'e baki "mum kinga kwa gidan su haydar en zeey wallah yayi kyau Kai Amma ya had'u" sai sunbatu take . Zee tace Kai sadeey se kace yar k'auye sai wani kod'a Abu kike". mum tace to" meye taga yai Mata kyau ne "suka bud'e ledar da aka basu super ce da mayafi sai kayan make-up da tarkacen sweat. . ************** *Bayan kwana 3* "Zeey wai mai sa bazaki fito ki tafi da wuri ba, salan dare yayi maki a hanya ko".? "mami gani nan" fitowa tai da hijab mami ta mik'o Mata leda kashi zee ki,kaiwa Hajiya kice abawa larai". Karb'a tai ta fita ahankali take tafiya har taje bakin titi ta hau adai-daita sahu har zai ja wani ya tsaida Shi d'ago kan da zatai ta ga tsalha. "shima ita yake kallo ya wage baki "zinaru dama zan ganki wajen kwana na hud'u a garinan nan ina neman gidan ku". bata ce Komi ba tacewa d'an adaidaita pls" muje" nan D'an babur yaja tsalha yabi bayan sa da Ido dai -dai nan wani yaro yazo wucewa nan tsalha ya tsai da Shi . "Don Allah yaro wan nan ta shiga babur en nan inane gidan su"? Almajiri yace" na Santa agidan su nake Aiki ina masu aike-aike sunan ta zeena". "Yawwa yaro ko zaka nunan gdan nasu"?. yaro yace" biyoni haka ya bishi suka je hargidan su zeey ya nuna mai ya tafi, tsalha ya kusa rabin awa a tsaye San nan ya tafi inda yake kwana ........... *Written* *By* *Queen



* *Queen



* . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queenie



 page 22* ?. ?. ?. ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *Dedicated to Lubie nd bena* *[5 Oct,2016*] **************** Zeey kan tana baby adai- daita tana tunanin abinda ya kawo tsalha dutse,haka taje ta Kai sak'on ta dawo dai -dai titin unguwar su babur ya lalace ganin Ana ta k'wala kiran sallah yasa ta fito ta bawa driver kud'in sa ta taka ak'afa Shigar ta kwanar layin su taji ansha gaban ta ganin tsalha ne yasa ta kalle Shi, "wai Kai me kake nema agu nane haka tun dasu kake bina ". "Haba zeenatu kin manta tsalhan ki na k'auyen birji"?. Tsaki tayi "to angaya ma dama sonka nake yanzu haka ma an kusa bikina,Ayni na d'auka Kawai irin D'an ganin budurwar birni taje k'auye yasa kukai ta tururruwa ashe Kai naga abun naka da gaske ne". "Haba zeena wlh sonki nake saboda ke fa na rabu da bintalo tunda kika tafi na kasa sukuni ganin hakan yasa na tawo don manya su shiga". "Wai nan ma k'auyanvcin zakai mun? to ka rabu da Ni". ta wuce Shi ta gefe. Binta yai yana k'wala Mata kira ko waiwaye batai ba. Shigar ta gidan su ta zauna sai had'e rai take mum tace "meya faru ne" . "Mum ina wadan nan Mutane da mukaje k'auye sukai ta zuwa gunta"? "Eh na ganesh". "to wallahi d'aya yazo garinn nan saboda Ni tunda na fita d'asu yake bina". Mum tace "to kide bi ahankali karde ki mai wulak'anci don ba kyau". "To mami yaya zan mai"?. "Ki bashi hkr Kawai" ,tom" hakan za ai. Tashi tai ta shiga d'aki ta cire hijab enta ta d'au phone enta ganin kiran hardar yasa tan nuna.jimami a face inta "OMG! Ban san ka kira ba my man". kiran sa tai ya dauka ,"tawan ina kika shiga ne"? . "Wallh dear naje unguwa ne". "Yawwa Amma dai baki make -up ba don ban san a gane min ke". dariya tasa "kar ka damu ko lipstick ban saba sai kwalli" "shima kwallin ay Kara wa big eyes naki kyau yake". "Sorry sir" "Yawwa ko kefa" agurguje suka kashe phone atare Don k'ok'rin yin sallah *Washegari* Haidar dake k'ok'arin fita ya shiga motar saya tada kenan, da sauri husy ta fito "wait ya haidar don Allah number en Anty zee zan kira ta mu gaisa". Fitowa yai "yawwa sis wai me zee taiwa hajj ne? jiya fa ta dad'e tana mun fad'a wai ita zee ba tai Mata ba kuma kin san Allah mum tayi fushi shiisa yau,ko kallo na batai ba". Husy ta gyara tsayuwa nan ta gaya mai abinda mami tace mata ,haidar yace "Kai mum wan nan fa tum tana K'ara mane ai yaci ace ta manta pls sis ki taushe ta ni kam in ba zee ba sai rijiya". Zeey tai dariya "karka damu ya yana zan taushe ta don Nima ina son zee". "yawwa k'anwata godia" haka ya bata number en ya tafi yana jimami. Bai zarce ko ina na sai gidansu kb ya faka mota ya fito k'anwar kb ta fito ganin sa yasa ta canja tafiya "ya haidar ina yini" kallon ta yai tai farrr da ido ,dai dai,lokacin kb ya fito tsawa ya daka mata "khady me kike atsaye" firgigit ta dawo daga duniyar data tafi don har ta ganota a lambun soyayyr haidar don ta dad'e da kamuwa da sonsa. Wucewa tai sum -sum. Kb yace "Aa aboki ya dai na ganka kamar baka dai dai" hmm "Kai dai bari wallahi mami ce kesan sani a matsala cuz tace bata sona da zee " . Kb yace to" me tai Mata"? haidar ya girgiza Kai no ban san reason ba Kawai de Ni kam bazan iya ba zee ba Kafad'ar sa ya dafa kar wann an ya d'aga hankalinka kowanne aure da irin nasa matsalar kai ta addua kana lalleshin hajiya zata sakko kai da ka kema D'an gaban goshin ta". "To kb Ngd" Motar sa suka shiga yaja suka fice daga harabar gidan. *Tsalha* Zaune yake a inda ya sauka yai ta gumi Audi mai kayan miya ya dafa Shi "meke faruwa tsalha kace sana'a ne ya kawowa garin nan Amma kaki ka fara". Jin-jina Kai yayi ba" haka bane Audi dama wata yarinya nabiyo wallahi sonta nake kodan ta ganni D'an k'auye wallah na kasa dena sonta,yanzu kaban shawara". "Ni kam shawarar dazan baka ka tafi garinku Kawai dama 'yan matan birnin nan ba kulaka zasuyi ba dai-dai ruwa dai dai tsaki ka kyaleta". Tsalha yace" bazan iya ba sonta nake ,Kawai na yanke shawara zanje gida na turo manya na". "Kai tsalha nan fa ba irin can bane Kai hakuri Kawai" takalman sa ya shura yai waje Audi ya kalle Shi ya jin-jina Kai. Fitar sa bai zame ko ina ba sai gidan su zeey k'ofar gidan su ya tsaya lokacin zeey suka fito ita da munay da Aneesa zasu islamiyya saboda sun kusa sauka shiisa suke zuwa da wuri Shan gaban su yayi "zeena don Allah karki tafi Ni ke na keso ba bintalo ba" ,munay da Anee suka kalli juna suka sa dariya. Zee ta kalleshi ta juya "pls tsalha wai Kai ba kaji ne? nace ma an kusa bikina kai hak'uri mana an tab'a so,dole ne fisabilillah ina zaka kaini". nan ta d'an sakko plss" tsalha Kayi hak'uri Kaji tai" D'an murmushi ganin hakan yasa yace"to Shi kenan Amma ki sani ina sonki duk da Ni D'an kauye ne" . "to naji ka tafi" haka ya tafi yana waiwayon su. Munay tace" ikon Allah zee ina kika samo wan nan mutumin"?. Aneesa tace" Ni bakiga bama ko kallonsa ban ba" . Zeey tace" wlh k'auyen birji mukaje biki nan ta basu labrn diramar da akai ak'auyen sukai ta dariya. Aneesa tace" ki dai bi Shi A hankali ki rabu lafiya kar kiga D'an k'auye ne wlh zai iya komi". Munay tace" haka ne to Allah ya kyauta" zee tace amee..... *Written* *by* *Queen



* *Queen



* . [10:02pm, 01/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queen



 page23* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. *®NWA* *dedicated to bena &Lubie* *[7 Oct 2016]* *Tsalha* Haka tsalha yaje d'akin daya sauka ya had'a kayan sa ya kalli mai kayan miya "Audi Ni na tafi birji Nanda kwana uku zan dawo" "Audi yace to kabari sai gobe mana kaga ai yamma Tayi" aje jaka yayi ya zauna "tom gobe da sassafe zan tafi" . Da sassafe haka tsalha ya d"auki jaka yaje tasha ya shiga motar birji yana ta tu nanin yanda zai tun kari malan na soro. Wajen k'arfe 12 yaje tun daya shiga cikin gari bai zarce ko ina ba sai gun baba na soro ,shigar sa baba na soro na zaune yana Shan kunu "Tsalha ina ka shiga ne "? "Wallah baba na d'anje jigawa ne". tome ya kai ka can jigawar kai da baka da komai acan"?. "Wallahi baba dama magana ne ke tafe dani saboda dama naiman aure nake acan to iyayen yarinyar nan sunce na turo" sunkwi da Kai yayi yana dariya. Tsalha kenan to yanzu ya kake so ayi"? Dama munyi da su zan koma jibi "shuru baba na soro yayi yace to Allah ya kaimu ,ai mu inde neman sunnar ma Aiki ne ai abun farin ciki ne ,yanzu jibi sai muje da kawunka farin ciki ne ya ishi tsalha kamar Wanda akace an bashi zeena,tsalha akwai ka da k'arfin hali lol. ********* *Hydar* Zaune yake yai tagumi mum dake tsaye kansa tace "haidar Ni mahaifiyar ka nace ka rabu da yarinyar nan mana kaje ka nemo ko wacce yarinya ce Amma Banda wan nan" . "Mami wai me Tai miki ne? wallahi zeena nada tarbiya" "Shut up haidar yarinyar nan kun san rashin kunyar da Tai mun Awani biki tana tab'en baki kamar Ni, akan ta daki wata yarinya,nai Mata fad'a to tabbas bata da tarbiyya". "Mum wallahi zeena tana da tarbiyya kuullm bata rabo da islamiyya yanzu next week fa zasuyi sauka wallahi mum lokacin k'uruciya ne" Kallonsa tai "Bawani k'uruciya Kawai rashin tarbiyya ne ka sani tun tuni na hak'ura da abinda tai mun, Amma yarinyar ce Kawai bata kwanta min ba". mami wallahi yanzu zeena ta daina ki hkr wallahi ita nake so" . "Tun yanzu ka fara sa'nisa dani Ina ga in Kai aure, to ban lamunta ba, ban amince ba, haidar ka nemi wata". tana fad'ar hakan tai gaba abinta. Haidar ya dafe Kai idanuwan sa sun jajawur jiyai kansa na sarawa tashi yayi ya shiga d'akin sa ya zube a gado yana Maida numfashi. Husna dai-dai lokacin ta dawo daga school agajiye da yake sun fara shirye -shiryen neco da waec ,direct D'akin haidar ta shiga gani tai ya k'urawa laptop ido Shiba dannawa yake ba. Zama tai kusa dashi ta lek'a laptop en ganin ya k'urawa Hotan zeena ido yasa tai magana. "Ya haidar" bai magana ba sai ido ya bita dashi. "husy I can't live without her , but mami tace bata Amince ba pls ya zan yi Allah in ba itaba bazan aure ba" Husy tace "ya haidar kadaina fad'ar haka in zeey matar kace ba makawa sai ka aureta Insha Allahu nai maka Alk'awarin shawo kan mami saboda Kai kad'ai ne brother ina you are d one & only ban son naganka cikin damuwa". Kallon ta yai yace" really"? "yes I'am sure ya haidar". "Tanks so much my husy" "my pleasure ya haidar dnt worry". Tashi tai ta fita ya bita da ido ,teble en gaban sa ya daka, "why mami" dafe kansa yayi Kawai ya suri key en motar sa ya fita ya shiga motar ya kwasa aguje....... ************* *Zeena* Zeena yanzu kullum tana busy saboda saukar su data k'arato Wanda za ai bikin saukar next Saturday,ga karatun waec agabanta shii'sa kullum tana busy,ko waya ma bata calling indai ba haidar nata ne ya bugo ba. Tana zaune tana d'aga less da atampha da takalmi da Dady ya sayo Mata Wanda zata sa ranar bikin saukar su , ta kalli mum tace" Amma zaki gayya ko mum"? tace "Aa Dan d'orawa Mutane wahala Kawai de zan gaya musu"Dan kar suji daga sama". "Hakan yayi kuwa" Su munay ne sukai sallama zee tace yawwa Aneesa gun tailo naki zaki rakani Naga yafi iya d'inki mai kyau" Aneesa tace" oke dama nima nakai mai na saukar mu" zeey taje gaban mum ta tsaugunna "mum bari nakai d'inkin don na samu da wuri" "Mum tace to adawo lafiya wai ba har da su sadiq za ai saukar ba". zeey tasa dariya wallah mum an fasa da su sai next year . Sadiq dake shigowa ya had'e rai mum tace" Sadiq ashe ban daku a saukar? kaga yanzu dadn ku ya Kai maka d'inki har kala 3 " Zeey tace "Allah kar abasshi" kallon ta yai ya daka Mata harara to yar black stomach wallahi sai an ban". Gwalo tai mai taja hannun Aneesa sukai waje suna dariya. Sadiq kamar yayi kuka ya shiga d'aKi yana had'e rai...... Haidar......oh kudakace Ni plss *Written* *by* *Queen



* *Queen



* . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queen



 page24* ?. ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *{10oct,2016}* Wata taxy ce ta danno layin su zeena tsalha ne gaban motar k'wam ya dogare hannuwan sa a bakin window en motar ,k'irr motar ta tsaya adai-dai bakin gidan su zeena ,tsalha ne ya fito bakin nan awashe yasha wata shadda ruwan goro ya d'ora blue en hula ,murfin motar ya bu e su baba na soro su uku suka firfito . Sallamar mai motar sukai san nan tsalha ya tun kari k'ofar gidan su Zeena,nan ma su baba na soro suka bi bayan sa. Kawun tsalha yace "Kai yanzu gidan sirukan naka shine Naga sai wani Rawar jiki kake". "Kawu sallama zan ai" k'wala sallama yayi sadiq ya fito ,nan ya gaidasu tsalha yace "baban ka muke son gani". Sadiq ya kallesu da mamaki ya shiga gida ya sanar kamar mintuna Sai ga Dady da carpet irin k'aramun nan ganin ya doso tsalha ya sunkwi da Kai ,sallama yai musu yayi musu iso da su shiga soron hakan kuwa suka zauna suka kuma gaisawa. Kawu ya kalli tsalha to rasa kunya agaban ka za anemi auren".? dariya yai ya tashi ya fita. Baba na soro "yace Alhaji dama yau ne akai yaron nan ya turo magaba tan sa ko"?. "to Alal hak'ik'a munji dad'I saboda yanda aka girmamu. Mu awajenmu kusa-kusa muke san bikin ya kasance sede muji ta bakin ka tunda mune masu naima". Shiru na a n lokaci Dady yayi ransaa ab'ace san nan ya d'ago "malam gaskiya Ni wan nan magana ban Santa ba asali ma Shi wan nan yaron ban San Shi ba ban ta a ganinsa ba". Murmushi yayi ,"sai naji kuma wata magana haka ta neman aure Wanda Shi aure ba abun wasa bane. Maganar gaskiya Ni banyi Alkawarin wani ya turo iyayen saba" Cike da bacin rai kawu ya dago "Alhaji ko Dan ka ganmu na k'auye mai sa zaka yaudare mu yaron nan yaje ya same mu da zan cen ance ya fito Amma kuma sai muji sab'anin hakan " Daka tardashi baba na soro yayi san nan yace "ina Shi tsalhan Shi za a tmbaya kawu da d'ina dakai baka da hakuri ". Tsalha ne ya shigo wular sa tai baya ya zauna agefe Dady ya kalle Shi yace "Kai yaro ka taba ganina "? Tsalha yace "Aa Amma zeena tasan dani ganin tana mun wala-wala yasa na turo iyayena" "Alhamdlh"Dady yace to" kunga magana ko yace ina zuwa", afusace ya tashi ya shiga gida. Baba na soro ya kalli tsalha "lallai sai yau na yarda da sokancin ka tsalha yanzu dama Kai bama asan da zamanka ba Amma ka tattago mu"? Malam hadi yace madallah aini naji Dad'i nan nan yake wulak'anta bintalo yarinyar abokina don yaga ta birni" Dady ne ya tawo bayan sa Zeena ce ta shigo kanta ak'as suka bita da ido nann yace "Zeena kalli wan nan da ido kin bashi izinin ya turo ne Alhalin kin san da Wanda yake sonki"? D'ago Kai Tayi ta mannawa tsalha wani wulak'an taccen kallo tace" Dady agaskiy Ni bami haka dashi ba Asali tun zuwan mu birji ne yake bina yazo har nan har sai da nagaya mai an mini miji Amma bai hak'ura ba to nidai ban san wani Abu ba bayan haka". Salati baba na soro yayi yace" Amma ka bamu kunya tsalha kuma dole muka koma ka auri bintalo domin dai-dai ruwa dai dai tsaki ,san nan komi zakai kayi gaskiya Gashi yanzu kazo kasa munji kunya". Gumi ne Kawai ke antayowa tsalha ya d'ago yace" don Allah Alhji ka auren yarka wallahi ina sonta " Hakuri sosai baba na soro ya bawa Dady. Dady yace ba komi yace su tsaya suci abinci Sun dako rans ba musu haka aka kawo musu sukaci suka sha ,tsalha kam yak'i ci. cikin mutunta juna suka tafi suna mai jin haushin tsalha. ********** Shigar Dady gida yai ta fa a ta inda yake shiga bata nan yake fita ba ,yace wa zeena karta K'ara Kula kowa tunda ya Mata miji . zeena dake aki mum na Mata magana tace" kibi ahankali zeena kinga mahaifinki yayi miki miji to ki nutsu baruwanki da barkatai en samari duk da nasan wan nan tsalha en shike shirmensa ". Zee tace" Toni mum mai zan da D'an k'auye tab ina yar birni shima don ya rainan hankali ne amma tun da yanzu anyi hakan ayya saman lafy" Mum tace zeena" ba a cewa mutum bai isaba ba saboda Shi aure hab'o ne ,ba a raina mutum ko yaya yake ,ina umatarki da duk saurayin da yace yana sonki to babu b'oye -b'oye irin na matan zamanin nan idan suna son yaudarar mutum, ki fito fili kice mai an bada ke yayi hak'uri ,tabbas nasan akwai 'yan naci to karki wulak'anta kowa ,ki mutunta shi ku rabu lafiya". "Insha Allah mum yanda kika ce hakan zany" Azuciyarta ta tana mum baki san san da nakewa Haidar ba ai Banda tym en wasu samari numfashi taja ta juya ta fita *Haidar* Haidar ne agaban mum ya dur k'ushe "mami don Allah ki yi hakuri ki daina fushi dani. Kallon sa tai "inde bazaka bi magana ta ba wallahi kana tartare da Fishi na". Husy ce ta shigo idonta na hawaye ta zauna "mami don sanki da manzon Allah. S.WA ki bar ya haidar ya aure zeena don Allah mami kinga Shi kad'ai garemu mami kullum haidar farin cikin mu shine nasa baya k'aunar ya ganmu cikin k'unar Zuci. "mami ki tuna soyayyar haidar gareki na tabbata zai iya hak'ura da zeena don farin cikin ki Amma kuma Shi zai,cutu azuciyarsa da komi ma . Mami kiyi hakuri ,nima mace ce idan akai mun hakan ba zamuji Dad'i ba mami pls help us wallahi I luv my brother bazan so ganin sa cikin damuwa ba". Mami datai Shiru ganin yanda husy ke kuka shab'e -shab'e tamkar wadda aka aikowa da sakon mutuwa, sai dai taji Dad'i ganin yanda 'ya'yan nata kesan junan su ta yanda d'aya ke damuwa da lamuran d'aya wan nna ka wai ya sanyaya heart nata taji zata iya amincewa ya auri zeena. D'ago idon ta Tayi tace" husna kenan Ka'nwar haidar" ,dariya husy tasa tabbas tasan inde mami tace Mata hakan to ta sakko. "Kuje na amince Allah ya kad'e fitina aciki" Husy tashi tayi tai tsalle san nan ta kwanta ajikin mami tace" mungode mami we luv u so much" Haidar kam bai ce komi ba sai kallon su yake cikin so da k'auna nan da nan yaji a zuciyar sa ta K'ara cika da soyayya yar k'anwar sa haka kuma yaji ya k'aara daraja mami ganin ta amince da farin cikin sa. tabbas naka sai naka dad'in zama sai bare.. Kallon sa mami Tayi tace" ja'iri rasa kunya kazo kai kana mun kuka kan budurwa" sunkwi da Kai yayi yace" Afuwa mami" yana dariya ya tashi ya shiga a kin sa ya bu e k'aramin firj nasa ya a kko maltina ya sha nan Sanyo. Ya ratsa Shi. Ya zauna kan bakin gadon sa ya akko wayar sa ya zooming picture en Hoton zee tana murmushi wushiryar ta tafito. Bugun zuciyar sa ne yaji ta k'aru inda yaji kir jin sa na kwaranyar da madarar k'aunar zee ,take ya danno layin ta ya kirata don Jin sweat voice nata........... *Written* *by* *Queen



* *Queen



* . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page25* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *dedicated to Lubie nd bena* *[10,Oct 2016]* *bayan sati daya* Yau ake saukar zeena tun K'arfe Goma suna can ita dasu Aneesa da yan gidan su .duk Sun hallara har Dady,haka aka gudanar akai musu karatu san nan aka basu zayyanar su inda kowa ka Gani fuskar sa d'auke da murmushi haka akaci aka sha,. su haidar ma sunje shida husy inda yaje da mai camera sai d'au kan su picture yake zeena da haidar su biyu Sun d'auka yakai sau goma. malam haruna da yazo wucewa,zeena ta gaida shi. yai dariya"ZEENATU yanzu an girma an daina fad'a ko,to madallah Allah yasa Qur ani ya zamo tsanin shiga aljanar mu". haidar dake murmushi yace Ameen. Haka akayi aka watse zeena ta dawo gida inda wasu 'yan uwansu suka zo haka dai akai aka gama tafiya sai fatan alheri. ************* *After 3month* Mata ne a manyan motoci guda 2 inda suka doso gidan su zee Wanda yake Cike da yan karbar kayan sa rana ,tsayuwa sukai suka firfto suka shiga ciki nan aka tarbesu aka kawo musu ruwa da lemo. Maza ne suka fara shigo da akwa tuna har set takwas mamaki k'arara afuskar yan uwan su zeena. Zama sukai san annan wata daga cikin matan tace" gashi kayan sa rana ne da lefe muka had'o ,mahaifiyar yaron ce tace akawo an wuta". wata tace" Masha Allah hakan yayi nan akai ta bu e kaya jingim sai tubarkallah ake zubawa, bayan angama bu e wa suka ce sa rana kuma wata 3, lokacin Sun k'are makaranta wato bayan candy da two week .,nan de duk aka yarda da hakan da zasu tafi aka basu tukwici mai tsoka saboda ganin irin tsadadden lefen da aka kawo. Bayan sun tafi mak'ota sukai ta shigowa Ganin kayan 'yan gulma kam kamar b'arko dasu ake haka akai sati a ya Ana Gani san aka hak'ura. B'angaren Zeena da haidar kuwa soyayyar su ,suke sha kamar ba gobe basason abunda zai raba su,musammn haidar bata ginin kowacce mace da gashi inba zeenar Shi ba. tunda aka sa Ranar su haidar yace duk unguwa Shi zai dunga Kai zeena, mum ta togace haka ya hakura. ********* Mami kuwa bayan haidar ya sanar da ita gidan da zai,saya wato gidan da zai zauna . Nan tace tunda ga su da part ba kowa aciki ,a nan gidan mai girma Kawai ya hak'ura yazo d'ayan part en Wanda gidan in ka shigo Shi bayan parkin space babba , to sai part in guda 2 d'ayan shine Wanda su mami suke ciki, ayan Shi kuma dama arufe yake to nan mami tace haidar ya shiga, dama agyare yake tunda ba zama akai aciki ba . Shidai haidar ya fiso ya tafi da Amaryar sa wani gidan ba nan gidan nasu ba , saboda yanda yake so su munji soyayyr su ,baiji Dad'i ba Amma ba yanda ya iya tunda hakan mami take so, kuma ba yanda zai yi tunda bashi da wadda ta fita dole ya bita kuma. Haka aka fara a gyaran side en duk wani kayan more rayuwa haidar siyowa yake amak'ala . A b'angaren zee kuwa abubaw Sun kacame Mata ga shirrin biki ga exams duk ta rame Abinci ma da k'yar ta keci duk Alhinin auren take Dan ma su Aneer da munay na tayata......... *Written* *By* *Queen



* *Queen



* . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: . . . *ZEENATU by Queen



 page26* ?. ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* *dedicated to Lubie & bena* *11oct 2016]* Lokaci sai tafiya yake tare da burukan Mutane Wanda ke cikin farin ciki ya koma bak'in ciki haka Wanda ke cikin bak'in ciki, dama rayuwa bata tab'a zama d'aya haka lokacin bikin su zeena ya k'ara to dama duk abinda aka sawa rana sayya zo. Saura kwana goma bikin su zeena ,yayin da gidajen biyu kowa sai shirye-shirye suke. zeena kuwa suna tsaka da exams ta dage sosai saboda wan nan ce damar ta ta k'arshe, yau ma agajiye ta dawo, bayan tai wanka suka tafi gun tailor Kai d'inkin fitar biki. Sunje bakin titi itada Munay taji kanta na Sara wa, nan ta dafe munay tace "zee ki koma gida Ni zan je wai bakiga yanda kika rame bane? ga exams ga shirin biki". Zee "tace to ya zan munay dole nai kuma gashi inaso nai karatu gobe". pls" Kije jikina ba k'wari" Munay "tace to zee". Haka ta koma gida,mum na tsakar gida ta shiga Kawai juya ta d'auke ta ta fad'i k'ass da gudu mum ta zo ta d'ago ta tana shafa fuskarta. "Zeena kina samun hutu kinji tunda Allah ma ya had'aki da k'awayen kirki ki bari su aiwatar da komi: ke kuma sai ki zauna tunda ma kun kusa final exams ". Sai da nutsuwa tazowa zee san nan ta tashi suka shiga aki,mum" tace kinga ma gobe mai gyaran jiki zata fara zuwa Tanai miki. daga school ba inda zaki Kara zuwa". *After 1 week later* Yau su zee ke final exams tun safe sai 3 suka fito, tana fitowa ta hau kuka saboda next week ta zama matar wani balalle ta kuma ganin school mate nata ba,haka sukai musayar numbers da frnds nata san nan ta basu iv na bikin ta duk Sun mata Alk'awarin zuwa. Cikin farin ciki ta koma gida tsayuwarta a Adai-data sahu haidar na tsayawa Shiva a motar sa ,murmushi yayi "congratulation my Queen Amaryata, yau kin k'are school sai kuma wata ". Murmushi Tayi "Angona ke nan Naga har ka fara k'yallin angon cin" . "nikam ka ganni sai ramewa nake" . "bakya cin abinci ne babyna amma tunda kin gama exams pls ki dai na fita". bu e motar sa yayi ya akko ice cream da shawarma ya mik'a Mata ahankali ta karb'a "pls dea kije kici in kuma ba haka ba wallahi zan shigo gun mum na baki da kaina". harara ta daka mai da murmushi, "bashi kika auka dea". aguje ta shiga cikin gida murmushi yay bita da Shi . Dama ganin ta yazo yi sai Kawai ya shiga motar sa ya figa gurin frnds nasa don,rabon iv. *************** Gyaran jiki ake wa zeena tunda aka fara ko nan da can bata fita, kwana 2 kenan da farawa da yake Allah ya yita fatar ta mai kyau ce. nan da nan tai sulb'i ta K'ara haske ga wani asirtaccen kyau da take zuwa bawa gashi duk inda ta xauna ta tashi kamshin turare zaka ji tana yi gashin shima yana Shan gyara,haidar kam tun san da suka had'u bai sake ganin ta ba saboda bata fita ko nan da can. Aneesa da munay ne keta zirga -zirga sai kuma sadeey dake taya su. Yau shine ranar da za a fara biki ,zee ce cikin shiga ta Alfarma hannun nan yaci zanen fulawa bak'I da ja haka k'afarnan Tayi balain kyau, kamar ka sace ta ka gudu da ita, fuskar nan sai sheki take true colour enta ta fito rad'au Masha Allah. An gudanar da kamu lafiya Washegari da juma'a akai walima nan ma fa ar irin kyan da zee tai b'ata lokaci ne Anty bara ta gyara ta sosai domin itama ta zo dangun su na ensa da kusa nan ma haka aka gudanar da walimar ansha hotuna zeena da k'awayen ta da 'yan uwa. Haka akayi aka watse. *Washe gari* Yau daya kama asabar rabar ne dubban jama a suka shaida d'aurin auren ZEENATU DA ALIYU HAIDAR bayan Mata suka zarce da yinin manya aka ci akasha mai kid'an kwarya na bidirin ta . Wajen K'arfe 8 angwaye da Amare suka tafi dinner inda nan ma fad'ar kyan zee da haidar kamar ka sace su ka gudu Allah yayi halitta sai dai mi musu,fatan zama lfy Haka akayi aka watse dai dai Karfe 10. Washegari shine ranar da aka mik'a zeena gidan mijinx ta Karfe 6 na yamma zo kuga yanda zeena ke kuka harda Amai sai da aka canja Mata kwalliya,nan ta k'an-ka'me mum sadiq da su sadeey faty har,da boy Khalid Wanda ba a dad'e da Haifa ba . Dak'yar aka sata mota su munay da Aneesa suka rufa Mata baya saboda sabo har kuka sukai. Tamfatsetsen gidan ta aka shigar da ita inda direct wajen mami aka mika ta. inda yake Cike da 'yan biki Nasiha akai Ma zee san nan aka Mik'a Amanar ta gun zee ,bangaren ta aka kaita part enta Mutane suka watse aka barta da ita dasu munay kafin angwaye suzo , Auren yak'in Mata ... Bari na dakata anan kafin zuwan angonta *Written* *by* *Queen



* *Queen



* . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: . . *ZEENATU by Queen



 page27* ?. ?. ? ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *Dedicated to Lubie & bena* Haka suka zauna sai hira suke suna K'ara kallon akin ganin yanda aka cika Mata Shi da kaya munay tace kinfa more zeey ga handsome husband ga gidan ki mai kyau" Aneesa tace ko kin manta ba ita ka ai bace a gidan "? Ita dai tana duk'un-k'une tana kuka motor ango ce da abokansa suka dira hayaninyar su ita tasa su munay Shiru direct aki haidar ya shiga nan su Aneesa sukace Ango kasha kamshi. "to ko zaku ce k'awar taku ta fito falo za a gaisa" Ahankali ta mik'e haidar ya bita da ido yana murmushi haka su Anee ma suka au mayafan su suka fita. Shak'iyanci sosai abokanan ango ke mai kb daya kafawa Aneesa ido tun shigowarta falon don tai mai. Shafa hab'ar sa yai to" Amarya ga ango nan Allah ya bada zama lfy ya kad'e fitina ya kawo 'yan 3" . Haidar na tsaye "oya kb time fa ya cika 'ibrhm yace lalle anyi abun kai haidar" Haidar yace" naji gwauro" haka sukai musu nasiha ibrhm ya rufe da addua .wani taf keken kwali suka aje Cike yake da kayan make -up mayuka da su lemuka da kud'i ha fa kayan sayan baki nan. Haka suka tashi su Aneesa ma sukai Mata sallama da k'yar ta sake su jikin ta har zafi ya d'auka kamar mai zazzabi. Bayan tafiyar su tana falo tana kuka, haidar ya rufe gidan ya shigo ya zauna gefen ta. "wan nan rana itace ranar da nake jira Allah na godema daka mallakan farin cikina". Tashi tai ta shige aki ta kwanta kan gado saboda jin kanta da tai yana ciwo. ahankali ta tashi cikin jiri saboda tun safe bata ci Abinci ba, sai aukin kuka. Jiri ne ya kwashe ta saura kad'an ta fad'i k'as caraf haidar ya rik'o ta yayin da ya k'urawa manyan idanuwan ta kallo, girar ta ya shafa da lips enta ,d'ago ta yai ya rungumeta yana jin wani iri ajikin sa tamkar mai jin sleep. Ita kam lafewa ta kumai ajikinsa jikinta ba K'wari gam -gam ya matse ta. san nan ya saketa ya d'auketa cak ya kwantar da ita akan bed jikinta ya tab'a yaji zafi zauuuuu. Toilet ya shiga ya murd'o ruwan zafi a wata yar roba ya auko Sabon towel ya fito bakin gadon ya zauna yasa towel en cikin robar ya Matso ruwan ya matse ya dannna Mata a wuyan ta . Kar-karwa jikin ta yake take ya tashi ya cire Mata. rigarta haka yai ta dad-dadna Mata, yana Mata tausa ,magani ya auko panadol ya bata tasha kallon sa take Cike da so da k'auna, har wata kunya da ta shige ta ganin yanda idanuwan sa suka k'an-k'ance yana Mata wani wahalallen kallo. Bayan ya gamai Mata ya akko fresh milk da gasasshiyar kaza yana bata a abaki . "Pls my choculate kici mana ,jikin ki fa rawa yake saboda rashin cin abinci, ya tsine fuska tai "dear na koshi fa". Ganin ya damu yasa taci kad'an tasha fresh milk en tanaci yana danna Mata jikin ta ,cikin k'an-k'anin lokaci taji kwari a jikin ta. already dama tai sallahr ta haka tabi lafiyar gado. Sai da yai nafila san nan yakwan ta abayan ta ya sak'alo hannun sa ya Matso da ita ajikin sa, take bacci ya sureshi da wani Dad'i da yake ji aran sa ganin zee kwance kusa dashi. ************ Washegari garau zee ta mik'e wanka ta feso ta fesa kwalliya ta fita falo sai tashin k'amshi take fuskar nan fiyau ,tana kallon gidan k'arshe ta dire a kitchen nan ta hau k'ok'rin yi musu toye-toye. Jitai haidar ya sak'alo ta ta baya ya kwanto kansa a wuyanta nan k'amshin jikinsu had'e "my baby good morning " Lafiya Lau kai fa"? Same u my choco" "Waya baki izinin shiga kitchen yau ko so kike ko wahalar min da kanki"?. " dear gani nai ya kamata" "to ki bari mami zata kawo". 'Yar aikin mami ce ta shigo da flask a hannu ta aje "gashi inji mami wai tana gaisheku. "Zee tace kice mungode". Zama sukai kan dining suna break shiya bata itama tana bashi. Haka suka gama ciyar da junan su, haidar ya kashe phones ensa suka koma aki yana tayata jera ka yanta a wardrobe,haka tun safe suna ask'ale da juna duk inda tai sayya bita. Wajen k'arfe 8 na dare suna zaune a falo manne da juna haidar na wasa da gashin zee ji yake tamkar ya had'iyeta ,ita kanta zee jin sa take har ranta tashi yai ya mik'ar da ita tsaye ya rungumeta hannunta ya rik'e suka shige bedroom sukayo Alwala sukai sallar nafila ta godia ga Allah. Hira suka hauyi tun farkon had'uwar su sai dariya suke, A hankali hirar tasu ta koma ta soyayya take zuciyoyun su suka zurfafa ganin yanda suka Lula dausayin masoya tamkar saci babu yasa na fito na rufo kofar...... *Washegari* Cike da farin ciki,haidar ya mik'e wani soyayuar ta yakeji a ransa musamman in ya tuno daren jiya, zee kwa in Banda kunya ba abinda take yi. Wajen K'arfe goma suna zaune kan 2seater sunci wanka da kwalliya sai tashin k'amshi suke ,in banda soyewa ba abinda suke. wayar haidar tai k'ara ganin kiran mami ya d'aga da sauri. Ba tare da komi,ba tace" kazo ina nai manka",k'it ta kashe a hankali ya mik'e yace "tawan mami na kirana bari na je". "dea ko nazo muje" ? "Bari na dawo sai ko je". Oke habiby Shiga yai mami na kan dining tana Shan kunun gyad'a. "mami ina kwana". Kallonsa tai" sannu ango tun jiya ina lura da kai bakaje sallahr asuba ba ko"? "Mami naje ta k'aramar kofa na fita bata get ba, kuma bada motana na fita ba". "To ya dace ace yau 3 days kenan ace matar ka ba tazo ta Gai dani ba" "Ayi hkr mami tace zata shigo nace ta bari sai gobe" "Yayi maka kyau haidar. To dama husy ce ke so ka bata no en Amaryar ka, ta buga tata akashe yanzu ma tai mun waya kasan jiya tabi Su Anty kano zatai holiday kamin exams nasu,ya fito". "To mami za atura Mata". "To kadai gyara tabbas zan kiraka da asuba ka dunga fita don wan Amaryar taka da alama kanai -naye ka zatai" Kai mum zee fa good girl ce, tashi yay ya fita ..... Ku dakacen my fans ,kuci gaba da kasancewa da Queen taku don ganin wainar da za a toya *Written* *By* *Queen



* *Queen



* . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: *ZEENATU by Queen



 page29* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. *® NWA* *Dedicated to Lubie nd bena* *15,Oct 2016* *Queen



* *Like Queen



 group of novel @ facebook* Jin arar bu e k'ofa yasa Zee ta mi e da magagin bacci toilet taje ta wanko fuskar ta ,zuwa tai ta bu e ganin Mata tai rututu suna shigowa Sun kai su goma sai Masha Allah suke cewa sannu da zuwa tai musu duk suka zauna kan kujera suna kalle -kalle . Zee tazo ta tsugunna ta gaidasu wata tsohuwa tace "yarinya ni nan k'nawar kakar haidar ce, wan nan k'anwata ce haka dai taita lussafosu Zee kam murmushi kawai take. pure water na leda ta kawo musu da lemo , ta zauna suna ta a hira wata ta tab'e baki. "ruwan leda" wata tace Dariya suka sa zeena jikin ta yayi sanyi ta Shiga kitchen tana kiciniyar D'ora girki wata k'arama acikin su ta Shiga kitchen in sai kalle- kalle take "karfa ki b'ata lokacin ki tafiya zami" Aki ta Shiga, wata daga cikin matan ta kalli aya "ai naso ace hajara ce ta shigo daular nan ai da bare gwanda an gida" . d'ayar tace" ai da sake kede barni kawai". Haka Zee ta akko musu turare da su mai da kudin mota, bayan fitar su ta koma aki ta kwanta . Wajen Karfe 3 haule ta Shiga side en zeena , tana gyara flask en abinci a dining . "Anty Zee wai kizo inji mami". "haule kice gani nan zuwa". haka ta tashi ta akko hijab inta ta Shiga. mami na zaune kan 2 seater tana waya sai data kare then ta juyo gun Zee tace "ke zeena dama baki da tarbiyya? ace 'yan uwan mijinki su zo Amma ki ka sai musu tarbar arziki ,sai ruwan leda , ina swan water da mijinki ya aje? ko sai 'yan uwanki sunzo zaki basu ehe"? Zee da zuciyar ta ta gama b'aci ta ago. "hajiya haka suka ce mik"i? Wallahi lemu da ruwa na kawo musu lokacin ban ora girki ba fa na tashi zan ora sai wata ta cemun wai kar na ora yanzu zasu tafi, da zasu tafi har su sabulai da mai na basu Allah ya gani nayi musu tarbar arzik'i". wani ban zan kallo mami "Tayi tiryan-tiryan kin sako magana to wallahi ban lamunta ba kin gane inde kina son zama lafiya dani to ki girmama an uwana". Zee ta ce" Allah ya baki hakuri". ******* tashi ki oran faten doya asalub'e Zee ta mik'e tana tunani wata aya da aure har an fara takurawa an aramin tsaki Tayi haka taje ta hau girki sai wajen 3 ta gama san nan ta aje a dining ta tafi side enta. Sanin haidar sai 5 zai shigo yasa ta kuma ora wani girkin. Tana zaune taci wanka tai kwalliya suna waya da mum haidar ya shigo da gudu taje ta rungumeshi "oyoyo swrht I miss u". peck ya bata a wuya "me too my choco". Aki ta kaishi ta tayashi ya rage Kayan sa yaje yayi wanka ,k'ananan kaya ya saka dining ya fito ya zauna cin abinci inda yake ta santi suna dariya ,dai-dai lokacin wayar sa tai K'ara mami ce akan layi ahankali ya auka "kazo ina son ganin ka". "to mami" Hira suka cigaba dayi wajen Rabin awa sai Ga haule ta shigo " wai hajiya na kira " Jikin Zee ya bata akwai wani Abu ta basar tashi yayi ya fita. Da sallama ya Shiga hajiya ta kaimai harara " zama yayi. "Hajiya gani".wato haidar matarka tafi arfin ka ko sai yanzu ma ta baka izinin tawo wa kirana ko"?. "Mami ba haka bane". "yanzu ace 'yan uwana suzo tai musu wulak'anci sai wani ruwan leda haba adinga Sara Ana duban bakin tulu mana,ya kamata kai Mata fa a amatsayin ta na matar ka ". Kan haidar dake sunkuye Shi a fa in zaman sa da Zee bai ta a ganin ta da bad hali ba . "kayi Shiru baka ce komi ba". "mami zan Mata". "yawwa har fad'a nai Mata Amma take neman tai min.rashin kunya" ,ransa ne ya baci . Ya tashi ya futa ransa a had'e ya Shiga binsa da kallo Zee Tayi . "lafiya habiby naga ranka aba'ce abinda ban ta a gani ba"? "Yanzu Zee abinda ki kaiwa su kaka kin kyauta kenan karki manta an uwana ne ace ruwa Shi zaki basu ,san dan mami tai miki fa a Kiyi Mata rashin kunya"? "To wallahi ki sani duk sonda nake miki akan mami zamu iya batawa". Idonta ne ya ciko da hawaye ta taso ahankali ta kwanta kan cinyar Shi ta kwantar da kanta kan kafa arshi ta Shiga raira kuka. Bai hanata ba Amma kukan na Shiga ransa ,ta ago tace "habiby har Ababa ni bazan wula anta 'yan uwanka ba, sunzo na kawo musu ruwan leda ganin swan ba sanyi na hado musu da drink ina zaune suka sha muna hira na tashi zan dafo abinci suka ce na barshi sauri suke, taja numfashi. mami ta Kirawoni bayan tafiyar su tana mun fa a ban musu tarba mai kyau ba". Allah ya huci zuciyarka Allah shine masanin gaskiya . "bai ce Komi ba ya tashi ya Shiga beadroom nasa ". Binsa tai da kallo itama ta tashi tana kuka ta shige aki tai flat akan bed tana kuka. Ganin ba sarki sai Allah ya sa ta Shiga kitchen ta hau clean en sa ta fito ta zauna ta kunna tv tana kallo Sam ba kallon take ba , bata son bacin ran haidar ,a hankali ta doshi a kinsa har ta bu e sai kuma ta koma da baya ta Shiga nata... *_Writting_* *_Queen



_*. . [9:18am, 02/11/2016]



 basheer: . *ZEENATU by Queen



 page 28* ?. ? ? ?. ?. ? ?. ?. *®NWA* *Dedicated to Lubie & bena* Bu e k'ofar falo haidar yayi zeey na kwance tana danna phone en ta, wuyanta ya an tab'a ta tashi firgigit ta tace" Wayyo haida" . dariya "matsoraciya". juyo wa tai ta ganshi da sauri ya rungumeta "oh my baby sorry na baki tsoro ko"? Turo baki Tayi ta an Harare Shi tare da kai mai dukan wasa, dariya yasa ya kamo ta yana shafa bayan ta, nan ya zame an kwalin data kafa auri yana shafa gashin ta . "Wa kike harara" baki ta murguda tana dariya lips en ya kamo yana shafawa ,ahankali ya fara kissn en ta, Sun Lula wata duniyar, wayar haidar ta hau ruri tsaki yayi ya k'yale wayar . Kira ne ya kuma shigowa zee ta an matsar da Shi "habiby ka au wayar" ,ta Shi tai tana girgiza ya bita da ido ta akko ta kawo mai . Sunan mami ya gani da sauri ya auka "hello mami" daga can tace" Naga ka koma side naku wai baza ka fita bane "? Mami ai na au hutun 2 week Hafez yana Kula da komaai" . "uhum yayi maka kyau" nan ta kashe . Zee data kwanta a kafa ar sa "habiby bari na Shiga gun mami". "Tam me kyau" Tashi tai ta akko Maya finta da wayar ta fito, caraf haidar ya riketa yana murza hannuwanta Wanda yajisu tamkar tuffa saboda laushi "I luv u so much Zee ta" luv" u too my habiby" da an gudunta ta fice ahankali take tafiya . K'irr ta danna ofar falon mami, haule ta tazo ta bu e Mata, kanta a sunkuye ta Shiga ,mami ce ta sakko hannunta rike da cup tana Shan fura. "Zee har k'as ta tsuguna ta gaida ta a ya tsine ta amsa "hakima sai yanzu zaki zo yau kwana hudu"? murmushi tai Kawai . Kallonta tai sosai ta tab'e baki "kuna zaune lafiya ko" zee tace" eh mami". "to yayi kyau sai kuma a kular mun da d'a kar da " zee tace "insha Allahu mami" "Mami ba abinda za ai miki"? "Babu idan ina da buk'ata zan kiraki". tashi tai ta fita daga falon ahankali zee ta mik'e ta tafi side nasu. Haka dai haidar da zee suke murzan soyayyar kamar saci babu haidar ko nan da can baya fita har hutun daya auka ya k'are. Ranar da zai fita kuwa zee har dasu kuka na kissa haka haidar ya shashance da k'yar suka hak'ura da juna . ************* *After 2 weeks* *10pm* Zee na zaune tana bawa haidar labarin kallon da suke a Bollywood nan wayarsa tai k'ara ganin.kiran mami ya d'auka "k'arar tv har nan haidar sai ka rage ,kuma kazo ina nai manka yanzu" "to mami gani nan". Zee ta kalle shi "mami ke kira". "eh beauty,bari naje" tashi yayi ya fita murd'a falon mami yayi ganin bata falo yasa yaje d'akin ta, tana zaune bakin gado ta kalleshi "Me kuke ne har yanzu Baku kwanta ba "? Haidar yace" mami ba komi kallo muke" nan ta kalleshi wato haidar tunda kai aure kullum kana mak'ale da Matarka so d'aya ma kake shigowa wajena". "Mami yi hakuri". "matarka ko D'an Aiki bata taba zuwa ta taya Ni ba kullum tana K'unshe a gida ita bata san ya kamata ba ko"?. haidar yace" Ayi hak'uri zata fara zuwa gobe Dan ma naga Ga me Aiki nan " "Kai dai ka sani". "Yadai ka Mata ka nunawa matarka matsayina domin Ni mahaifiyar kace". "Ayi hak'uri mami". Ahankali ya tashi ya mik'e yana tafiya yana tunanin mai sa mami ke haka bayan tasan kullum Zee na zuwa gaida ita. Yana komawa suka tafi bedroom don kwanciya. *3am* wayar haidar ta motsa cikin magagin bacci ya d'aga mami ce daga can "ka tashi haidar asuba Tayi "mami ai ba ai kiran sallah ba". "au se anyi ma zaka tashi"? To mami kit ya kashe Damuwa ce Fal aransa kan irin abunda mami ke mai bama su dad'e da kwanciya ba. Ganin yanda Zee ke bacci lakadan yasa ya kyaleta bai tashe ta ba ya bari sai ankira ya tashe ta. *Washegari* Wajen Karfe 9 Zee ta Shiga gun mami ta d'an-d'asa kwalliyar ta gaisa wa sukai Zee ta Shiga kitchen tana taya haule girki ganin bata lokaci yasa tace haule ta bari Tayi haka ta zage tai Mata girki mai nyc bayan ta gama ra kawo dining ,mami dake zaune Zee ta tsugunna mami na gama "tashi tai taje dining en ta zauna ta bu e flask ta iba ta fara ci ,yatsine fuska tai . "ya kika bari gishiiri yayi yawa"?. "mami bansa gishiri bama magi ne Kawai". kunun gyada ta kurb'a to adai gyara". Ahankali Zee ta fita side enta tana mai mamakin mami da komi zakai Mata baka birgeta, d'akin ta ta shige ta haye gado nan ta koma bacci. *Written* *By* *Queen



* *Queen



* . . *ZEENATU by Queen



 page30* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. *®NWA* *Dedicated to Lubie &bena* *15oct 2016* Juyi kawai yake saboda baiji dad'in fa an da yai Mata ba, ahankali yafito daga akin sa ya doshi nata.Kirr ya bu e tana zaune kan stool tana gyara kanta run gumota yayi ta baya ya sumbaci sumar ta, zame jikin ta Tayi ta fita falo. ya bita zama tai kan kushin ta au waya k'wacewa yayi . Ya damk'o ta "ni ka sake ni" "Sorry baby raina ne ya b'aci" . kuka tasa "na fa a maka Amma baka yarda ba". "Na yarda man pls baby" haka dai ya lallab'ata har ta wu ce soyayyar su suka zarce dashi . *Washegari* Da yake weekend ne tun safe Zee ke Shirin zuwa gida sai oki take saboda yau ne fitar ta ta farko kwalliya taci Sosai kana ganin ta kaga amarya ,haka Shima haidar in yayi ,fitowa sukai sak'ale da juna suka doshi new car ensa sai daya bu e Mata ta Shiga san nan yaja, mami da taji k'arar fitar mota yasa ta bu e labule da yake tana bene ganin fitar su haidar yasa tai k'wafa. Mum na ferayar doya sadeey na wanke-wanke Zee ta Shiga a guje ta fa a Mata tana dariya. Mum tai dariya "su Zee na Amare" dai-dai lokacin haidar ya Shiga nan suka gaisa ya aje kayan da Zee tazo musu dashi ya fita . Zee da su sadeey faty suka baibaye ta don sunji da in ganin ta mum sai kallon Zee take ganin yanda tai fresh ta ara kyau skin enta ta da a haske tamkar black American hira suke Tayi mami tace ba wani Abu ko " Zee tace babu Wlh muna zaune lafy. Sadiq ne ya shigo agajiye,daga school ganin Zee yace tab wayaga Amarya harara ta zuba mai. "yarinya bar ganin kinyi aure . " Zee tai dariya yaro dole ace da mijin iya baba". Haka dai sukai ta hira "sadiq yace exams en ku fa ta kusa fitowa ". Zee tace" kai don Allah addua tai tayi Allah yasa ta samu 9 credit sadiq yace" wai bazaki jamb bane? Tace "zanyi mana lokacin da zakayi nima zanyi." "Mijin naki zai barki? harara ta kai mai "to sai ka ce miji, ba sai kace kace yaya haidar ba ,D'an rainin wayo". Dariya yasa ato "ke kika ce kina so ,daba kice kina so ba daba a baki Shi ba". Dariya tasa "kaji dashi" haka sukai ta hira cikin jun Dadi ,'yan uwan rabin jiki *6 pm* Haidar yazo d'aukar Zee haka ta fito suka tafi ahanya sai hira suke nan ya biya ta fish fark ya sayo musu sukayi gida. Shigar su get in gidan motar k'anwar mami na fita lokacin,mami ta juya zata Shiga ta tsaya ,firfitowa sukai Zee taje ta tsugunna ta gaida mami. "amsawa tai adak'ile ta kalli haidar "Yayi maka kyau ace zaku fita Amma ko ku sanar mun kai sai abunda wan nan figaggiyar matar taka ta ora ka ,wallah zamu sa k'afar wando aya da kai haidar". "ke kuma da kike kallona oya tashi ki barmun nan waje zamu gana d'ana, a hankali ta mik'e tai side en ta. Ran haidar ya baci Amma ba yanda zaiyi cuz uwa -uwa ce. Fa a take ta mai kansa ak'as. Zee kam bayan Shigarta ta zauna r akan kushin ta hau tunani tabbas ni Zee nayi sanyi ina mamakin kaina Amma abinda matar nan take ya fara isa na ace bakada sakewa kaida mijinka tsaki Tayi ta bu e akinta ta canja kaya ta hau tunani. Fuskar sa a washe ya Shiga falon ,tabbas yasan dole ran Zee ya b'aci ,ciccibar ta yai tamkar 'yar baby ya Shiga aki akan kujerar dake akin sa ya aje ta ,ya kalleta ido cikin ido " "zeeta kiyi hkr da abinda mami Tayi pls" murumushi Tayi "ba komi fa" . "yawwa tawan sumbatar lips enta yayi ya rungumota pls ki k'arfafan gwiwa akomai kinji my wife ,zama da babba dama sai hkr". murmushi Tayi ta shafi gefen fuskar sa dont worry habiby I luv u". Cikin farin ciki suka tashi se lokacin ya tuno da kifin su nan ya akko suka Shiga kitchen sukai sharp-shap girki a tare ,suka gama suka cinyar da junan su. ******* Haka dai rayuwa take gudana yau watan su 2 da aure ,basu da wata matsala a tsakanin su sai ta mami domin Zee na jure abin da take Mata Wanda ya samo asaline da yanda take son haidar shiisa take hkr ,karku manta makaranta tun tasowar Zee bata da hak'uri to Amma soyayyr haidar tasa tana jurewa ,to ko zata cigaba da hkr ku biyo



 don jin yanda zata kaya. *_Writting_* *_Queen



_* . . . . *ZEENATU by Queen



 page 31* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *Dedicated to Lubie nd bena* *16 Oct 2016* "Hajara Amma kin kyauta da kika zo min hutu saboda kadaicin husy na damu na"(hajara 'yar kanwar mami ce) hajara tai dariya "mami ay dama ni tagunki ce boko ne ya sani gaba ",haule ce ta shigo da try d'auke da five alive da cup ta aje ,hajiya ta kalli haule tace ta dauki trolly en hajara ta kai akin baki . Tashi hajara Tayi yawwa mami bari naje nai wanka tabi bayan haule ,dariya tai ta zauna gefen gado tana tunani saida tai wanka tai sallah nan ta dawo falo ta zauna ,dai-dai lokacin zeena ta shigo tasa after dress ta yane kanta har kas ta durk'usa ta gaida mami hajara ta kalleta ta juya "hala mami wannan ce Amaryar"mami ta ce itace tab'e baki tayi "bale fi tayi" kitchen zeena ta shige ta hau ora sanwa haule na tayata "wajen Karfe 1:30 ta gama ta fito taiwa mami sallama ta koma . Hajara dake ta zabga Loma ta kalli mami "Amma ba ta iya girki,mami Nifa jiran yaya nake ya dawo" mami tace sai 5 zaki ganshi "dan ma wan nan figaggiyar matar tasa na kanai naye shi aida kullum yana nan" ,hajara tace" tab Amma ta samu sake" . ************ K'arFe biyar haidar na shigowa ya faka motar sa agajiye ya Shiga Zee da sauri ta rungume abin ta. tana mai Welcm wanka yaje yayi ya dawo Zee ta zauna tana bashi abinci suna hirar su rufe Mata ido yayi ya saka Mata key a hannu bu e wa tai taga na mota ne "na meye habiby"? Naki ne tsalle ta daka ta rungume shi "thnk u so much my haidar "U deserve it dea". Kiss ta bashi a lips Burum a ka shigo "ya haidar dama ka dawo"? Juya wa yayi ganin hajara tsaye tana dariya yace "Aa k'anwataa saukar Yaushe "? Zama tai da fari ko kallon Zee batai ba "dazu na sauka zanwa mami hutu ,Ay naita tryn number inka is switch off". "Eyya kin san na canja shiisa" ,naga Amaryar ka sede da alama zatai jin kai kallon -kallo,sukai da Zee da haidar ,yak'e kawai yayi "haba kawai don Baku,Saba bane ba". Tashi tai ta shige kitchen sai kace gidan ta ta akko lemo ta dawo "Amma ya haidar side enka yayi mun kyau " Hira sukai tayi san nan ta koma .. *8pm* Haidar ya Shiga gun mami tana zaune suna kallo da hajara, bayan ya gaida ta sayya ce dama hajiya magana zami kallon hajara tai ,tashi tai ta shige aki . "Dama mami mota ce karama na saiwa Zee saboda ko zata unguwa Kinga ta huta inta fara zuwa school". Wani banzan kallo tai mai "to uban Almubazzaranci yanzu ba ka saiwa k'anwarka ba , Amma zaka saiwa wata matarka" . "Mami ai husy tana da tata motar " "To ban lamunta ba salon ta sake mik'e k'afar shirya tsiya ko ". "Mami na Riga fa da na bata key". "Yayi maka kyau" "Kiyi hakuri mami" bata ce Kimi ba saima tashi da tai ta Shiga aki. Asanyaye ya tashi ya fice.mami data zauna kan mudubi wallahi dani yake zancen, dama can ni jini na bai hadu da yarinyar nn ba" ***** Washegari wajen 11 motar aka kawota red 207 Zee Cike da Murna ta fito tana shafa motar, bu e wa tai ta Shiga tama rasa murnar da zatai mai kawo motar ya tafi da Murna ta Shiga gida sai tsalle take . Yau ne shigarta na farko side en Zee tunda aka kawo ta ,a fusace ta banke kofar "ina kike fito nan aguje Zee ta fito tace gani mami "shasha bani key in motar nan kin mallaken d'a sai abinda kika ce to idan kwance kika Kwan ni kullum atsaye nake k'i gam". kuka ne ya zowa Zee da sauri ta akko Muk'ullun ta mik'a Mata afusace ta fita. aki zee ta shige tana kuka . Mami data Shiga side enta tana ta fa a hajara ta fito "mami meye "? mami tace barni da waccen figaggiyar wai yanzu Dan rashin ciwon kai haidar ya bata mota" . Hajara tace aini tin gani na da ita yanda naga haidar na Rawar jiki a kanta na san an gama da Shi ,"ai mami ki tashi tsaye kina zaune xata rabaki da Shi". k'wafa tai "bar ni dashi inya san wata ai besan wata ba. Bayan dawowar haidar Zee ko a fuska bataa Nuna mai ba, saima wata sabuwar soyayya da ta Farai mai tana kwance kan cinyar sa yana shafa gashin ta "babyna Kinga mota ko"? " Na ganta har Shiga nai ba abinda zan cema sai dai Allah y saka da Alheri". shafo face enta yayi ya matseta a jikinsa kirrrrr wayarsa tai K'ara . K'irjinsa ne ya buga ganin sunan mami,ahankali ya d'auka "kazo yanzu ina son ganin ka"k'it ta kashe Tashi yayi ya fita hajara ce a bakin ofa tana waya fari ta sakar mai d'auke kai yayi mami na hakimce tana duba less less da super. zama yayi a d'aya daga kujerun yace mami gani. "Haidar wai Meya canja ka? tunda kai aure ban isa na gaya ma ba ka dauka ba yanzu ashe sai da kasai motar ?,to na k'wace ,tashi ka tafi yana son magana Amma ba yanda zaiyi ganin ta had'e ya tashi ya fita . "Ya haidar" juyawa yayi ganin ta tawo tana girgiza kawai ya daga Mata hannu "pls kaina ciwo yake" gaba yayi ,binsa tai da ido ta tab'e baki. "Ko mai zeena, komai zeena. to wallahi nima sonka nake kuma dole ka auren ,ciki da shige. Rungumeta yayi ta baya ,don ji yayi ta K'ara kima a idonsa "Zee ta baki fad'an abinda mami tai miki ba, naji Dadi tabbas nasan zaki riken sirri, but kiyi hkr insha Allahu zata dawo miki da motar ki ". bakomi masoyina murmushi tayi mai, tareda kashe mai ido daya........ *_Writing_* *_Queen



_* . . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . *ZEENATU by Queen



 page 32* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. *®NWA* *Dedicated to Lubie &bena* *17,Oct 2016* Yau da ya kama weekend haidar yace yana sha awar kunu da kosai , Zee na kitchen sai kacaniyar tuyar kosai take ,da yake ta gama dama kunu in, haidar na zaune yana kallon wani film game of the throne, a laptop ihun Zee ya juyo daga kitchen a guje ganin tana yarfe hannu yasa ya kama hannun yana firfitawa da bakinsa. "Meya same ki dear". idonta daya ciko da hawaye tace" mai ne ya fallatso mun", sannu yay Mata ya karanta Mata falaqi da nasi don kar gun ya tashi ya rofa ,yace ta bari ya k'arasa tuyar . Tana tsaye gefe suna tab'a hira tana had'a sauran kayan Shi kuma yana kwashe k'osan . Ba sallama su kaga hajara a kofar kitchen en . "Aa ya haidar yau soyayyar ta motsa ne hararar ta yai "ina miki wasa ne" . dariya tayi "dama mami ce tace kabawa maigadi ya sayo mai motar ta babu" . "ok zan bayar". kallon Zee tayi ta sakar Mata harara tai waje. Aguje ta Shiga akin mami ta tsaya "mami lalle yarinyar nan tana neman Maida ya haidar solob'iyo duk gayun sa Amma shike tuyar kosai ". Dariya mami tasa lalle kuwa tab namiji da suna hajara " Hajara tace" mami wan nan Karin maganar ai da suna nane,". mami tace" barni dashi lokaci ne" . Hira suke cikin so da k'auna nan Zee ta ya tsine fuska "wallahi cikina ciwo yake habiby" . kallon ta yayi yace"sannu" kad'an- kad'an sai zazzabi ya rufe ta, kafin K'arfe 11 Zee jikinta yayi zafi zau ganin haka yasa haidar ya kwasheta zuwa aaibiti . Taimakon gaggawa akai Mata cikin mintuna aka K'ara Mata ruwan akai Mata Allura bacci ya kwasheta. Gun doctor yaje doctor yake gayya mai ai tana da typot ne . Waya ya bugawa mami ya gaya Mata Allah ya sawwake tayi Mata. haidar bai gayawa mum ba (gidan su Zee) saboda doctor yayi masa confirming tana tashi zata ware tunda abin baici k'arfinta ba. Haidar na zaune wayarsa tai K'ara mami tace "hala kode ciki ne". Haidar da yaji kunya "yace Aa sunce typot ne". jinjina kai tayi ta kashe. Haka ya zauna a hospital in yaa kwana tunda bai gayawa yan uwantaba Kwa nan su aya Ana treatment en zeey ta warware aka basu sallama tare da magunguna *********** Wajen 11 suka shiga gida mami da hajara na zaune kan kujeru kusa da wata bishiyar umbrella, suna hira haidar ya fito zeey ma haka wurin mami sukayi zeey ta gaida ita haka Shima haidar in hajara ma ta gaidashi ,Amma ko kallon Zee batai ba, balle tai Mata ya jiki. Mami tace" ke ya jikin naki"?. zeey ta ago manyan idanuwanta tace da" sauk'i" "Ai na auka ciki gareki Ashe dai cima zaune ce ke". Kunya ce ta kama ta suka mik'e . Bayan Sun shige mami tace ace wata biyu babu amo ba labari ,hajara tai dariya "lalle kuwa". ************ Bayan kwana biyu a tsakani zeey ta warware tana zaune tana waya da munay tana Mata zan cen zuwan su. Bako sallama hajara ta Shiga taci kwalliya direct kitchen ta shige ta bu e gidan sanyi ta akko exotic ta fito tana zuka ,zeey da abin ya bata mamaki da sauri ta tashi. "ke wama kike da suna yanzu in Banda shirme keba matar gida ba sai kawai kizo ki shigemun kitchen Kamar naki, ba tambaya ki au Abu ki fito kina mun kallon banza kina zuk'a ko"?. Wani lalataccen kallo hajara taiwa Zee "lalle wuyanki ya isa yanka dama kin iya fa a"?. Dariya zeee tayi "rashin sani ayya fi dare duhu,ni enn nan zeena idan rashin kunya kike ji dashi na fiki haka in fa a donni ba kanwar lasa nace". "Tun zuwan ki naga irin abinda kike min hak'uri dole nake ,idan nai hkr akan Wanda suka can-can ta, to wallahi k'aryarki na k'yaleki ki raina min hankali." Hajara tace" naga gidan wana ne don haka sai abunda nai niya" Zee tace "sannu husy to ko ita bazan lamunta tai mun irin gadarar nan ba, ita da suke ciki aya ma, balle ke da kike cosin. Dan haka Kije ki koyo ladabin Shiga gidan mutane". Fita hajara tayi tana fa a ,zee kam zama tai kan kushin tana huci ,tuno nasihar mum tayi data ce ta koyi hakuri kowa yayi Mata zancen ta koyi hakuri akan zaman aure ,tun da Sun san bata da hakuri Amma tana dai -dai gwargwado sai an kaita bango. tashi tayi ta kulle gidan ta shige can uryar aki ta hau bacci. Da yake tasan yau haidar take away zaiyo musu shiisa batai girki ba ,wajen 4 taji bugu tashi tayi taje ta bu e ganin haidar rai ab'ace tasha jinin -jikin matsa wa tayi ya shige. Aki ya Shiga ,ko magana bai mata ba baice ala ba sai daya gama wan kansa ya fito. Kallon sa tayi "yadai habiby waya bata ma rai". Zama yayi ya kalleta "Yanzu zagin da kikaiwa mami kin kyauta ke nan yanzu in taki nayi wa ya za kiji "?. Ago ta yayi ya girgiza ka fa arta ki" gayan" kuka kawai take. Zamewa tai ta zauna "duk Wanda ya gaya ma wallahi bai mun adalci ba tashi tayi da gudu ta akko qur ani ta aje zan iya rantsuwa da wan nan qur anin ban zageta ba, haba ina fa da hankali" Jikinsa ne yayi sanyi ,auka tayi zata rantse ya dakatar da ita. Zama yayi kan kujera "dama nima nasan hakan ba zata faru ba". "Amma Waye ya gaya ma"?. "hajara ce". bata ce Komi ba ta tashi ta fice can bayan gidan taje ta zauna tana kuka..... *Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . *ZEENATU by Queen



 page33* ?. ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* *Dedicated dis page to all lovers of ZEENATU* *18 Oct 2016* *Queen



* Zama tayi abayan flowers ta k'unshe an kwalinta ta tusa kanta ciki tana ta kuka tunani ta hau yi tana 'yar K'ara Marta ta Shiga jidalin aure mesa haidar bazai gasgata abinda zata iya da Wanda Baza taiba,tsinke flower en take tana ta watsar ta tana kuka. Haidar dake tsaye akanta yaji zuciyarshi babu Dad'i ahankali ya taka ya kamo ta ta baya ya rungume "sorry my sweathat wallahi rai nane ya b'aci shisa ,kin san akace uwa to dole mitum yaji ba Dadi, Amma yanzu na gane k'aryar hajara ne pls baby say something" . "Enough haidar,bana son wasu maganganu daga gareka ,nayi mamaki duk soyayyr da muka sha Amma har yanzu Baka tantance abunda zan iya da Wanda bazan ba, haba iyaye ai ba wasa bane nasan k'imar su don haka bazan iyai ma mami abinda nasan bazan wa mahaifiya ta ,tamkar uwa take agareni". Numfashi tasha "Amma habiby Abu ka an ba bincike sai ka hau sama ace aure ko 3 month banba Amma matsala sai Shiga nake" . Janyo ta yayi "sorrry dear kaina bisa wuyana" tsugunnawa yayi alamar kamun kunne dariya tayi . Ya kamota yai Mata chakulkuli ta hau dariya,yana shafa bayan ta aukan ta yayi cak suka shige side in su ta baya . Falo suka shige ganin an kusa kiran sallah yasa yai alwala ya fita masallaci ofar fita yaga hajar na waya ta na ganin sa katse ya" haidar" tsayawa yayi ya had'e rai "me zan miki."? "Sai ma kashedi da zan miki ba ruwanki da wifey ena kin gane". Tab'e baki tayi Amma ya nai mamaki ace ta zagi hajiya kaki aukan mataki ,kai ko kishin mami ba kai ,Mari ya kai Mata ta dafe gun kuka tasa ta shige ciki aguje ,shi kam yayi tsaki ya fita. Tana Shiga ta zauna tana kuka ,tana ganin mami ta kuma fashewa ,mami tace Aa hajar "Meya faru ,mami wai yanzu ace zeey ta zageki wai don na tanka shine ya haidar ya mareni ". Har damun gorin gida mami tace" zai zo ya samen" murmushi tayi ta shige aki ta au wayar ta mamin ta ta bugawa "wallahi umma har yanzu baya kulani ko kallona baya yi azu ma Mari na yayi ni Wallah Shi nake so. Daga can umman tace karki damu next zanzo gun hajiyar ai ai Komi ya k'are,tsalle ta daka . *After 1 week* Yau haidar ke shirin tafiya Lagos akan wasu ayyuka da suka shafi companyn su to 3week zaiyi shiisa ya yanke sha warar tafiya da zeey. Bayan Sun gama shiri ya ciccib'o trolly en zeey ya saka abayan mota Dad'i kawai Zee take tafiyar da zasuyi, ta samu sa idar zaman gidan dama Kamar akan k'aya take. Mami ce ta fito husy da hajar a bayanta sai hararar Zee suke don itama husy tun dawo warta hajar ta suge ta yanzu har da ita ake Mata rashin mutunci. "Bade da ita zakai tafiyar ba" haidar tsugunnawa yayi "eh mami tare zamu",to ban Baka izini ba. Salan ka tafi da ita Shi kenan bazan sake ganin ka ba ,dama ta samu kenan". ta kalli zeey "wuce ki koma kina wani kallona" ,da gudu ta koma tana kuka. Haidar daya ji kanshi na Sara wa "mami ki bari mu tafi" . Hajara ta tabe baki husy tace "ya haidar wai mesa tunda kai aure duk ka canja". Mari ya kai Mata "wallahi zan huce a kanki"Shiru tayi tana Sosa gun. Tashi yayi ya shige ciki ,hajar "tace wallahi mami ki bari mi Mata duka wallahi ko Ido bana san na bu e naga wan nan banzar". husy tace "Nifa da ina son ta ,Amma tunda naga yanda ta kanai naye ya Ta ficen arai" komawa sukai ciki. Lalla shin ta yake da k'yar ta hak'ura tashi tayi "habiby kabi maganar mami kaje Allah ya kare ka, zanwa mum magana ta turo sadeey sai ta tayani kwana" ba yanda ya iya haka ya rungume zeee har k'walla yayi "I mss u so much , da da yanda zan damun koma gidan mu , mu ka ai Amma mami taki,kiss tai mai a lips ensa bakomi dear muje na raka ka, haka ta fita ,haka sukai sallama cikin kewar juna. Bayan tafiyar sa in Banda kuka ba abinda take ,sai daga baya taiwa mami waya kan sadeey tazo,tunani ta hau yi yanda ta tsinci kanta ,ta rasa mesa mami bata sonta ....... *Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . . *ZEENATU by Queen



 page 34* ?. ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* *Dedicated to Lubie ,bena & Antysis* *Queen



* Ganin tunanin bazai kai Mata ba yasa ta tashi ta shige d'aki ta d'auko al qur'ani tana karantawa nan da nan taji ranta yayi wasai duk wasu b'acin rai taji Sun gushe,bacci ne taji ya kwa sheta . Jin K'amar buga k'ofa yasa ta mik'e ta bud'e sadeey ce agaba sadiq na binta a baya, murna ce ta kama ta ta rungume su, zama sukayi sadiq "yace bamu gurki mu kwasa saboda yunwa na keji". Zeey "tace sai kace ba daga gida kake ba". "ke wallahi ina dawo wa daga school mum ta had'o ni da sadeey" . abinci ta Zubo mai da zob'o yaci yasha ya tafi haka itada sadeey sukai ta hira . Da dare suna zaune har Sun rufe side d'in su ganin 8 tayi bugu sukaji Anayi Zee ta tashi taje ta bud'e, husy ce da hajar suka Shiga bako sallama suka zauna ,husy ce tayi wa zeey magana "zami kallo saboda nan ne kuke da govt kuma muna son kallon zeeworld" . Zee "tace ba matsala ku yi volume suka k'ure" sadeey tace" don Allah ku rage" ,hajar "tace anki" , shiru tayi da bakin ta ,yasa zeey ta tashi ta rage hajar ta kuma tashi ta k'ure volume ,Zee ta kalleta "haba hajar sai kace gidan kallo". Kallon ta tayi tace" to meye Maraba". "ba zadai a janzawa tuwo suna ba",husy kam tashi tayi tai kitchen "zeey zan dafa indomie" haka ta Shiga ta dafa ta dawo suka ci gaba da kallo hamma sadeey ta fara yi ,kwanciyar ta taje tayi Zee ta kalle su "ni zan rufe gida",husy tace" bamu gama ba ki tafi idan bacci kike ji in mun gama zamu rufe miki gidan" . Tsayuwa tayi na D'an mintuna kawai ta shige d'aki K'irr wayar zeey tai K'ara hajar dake kusa da ita tai saurin d'a gawa murmushi tayi kai dama ta samu. "Hello haidar" daga can yace "my life hope kin wuni lafiya ya missn D'ina" ?,dariya hajar tayi "ya haidar bafa ita bace nice hajara" "Meya kawo wayarta nan gunki". fari tayi "ai muna gidan" to" bani ita". Gyara zama tayi "ai ta fita waje tun d'azu daka tafi tana wajen har mami tai Mata magana ko kallo bata ishe ta ba". Duka husy ta kai Mata ,ture hannun ta tayi daga can haidar yace" kai Mata to" ,kit ta kashe wayar ta wullar da ita. Sai wajen 10:30 suka bar gidan ko rufewa ba siyi ba cikin magagin bacci zeey ta taso ta rufe gidan. *Washegari* Zee ta fito ganin wayar ta ak'asa d'auka tayi ta kunna kunna warta keda wuya wayar haidar ta shigo "habiby ka sauka lfy" baby jiya na bugo akace kina waje" Zee tace ai ni bacci nayi jin hakan yasa kawai ya basar da maganar,nan suka gaisa suka musanyawa juna dad'a d'an kalamai. Maman hajar ce tazo t Zee taje ta gaida ita ta ajiye flask cike da dambun shinkafa da miyar hanta ,gaida mami tayi ta amsa a dak'ile, bayan sunci sunsha har dasu santin dadi sa san nan suka Shiga hira inda Maman hajar ta kalli mami. "wai ni yarinyar nan har yanzu ba amo ba labarin ciki", mami ta tabe baki "ni ta ficen daga rai. umma tace nikam inada wata shawara yaya da zaki d'auka da hankalinki ya kwanta ". Mami "tace wace shawarace? nan ta gyara zama ,kin san meye ?kawai da ki zauna tana b'ata miki ,me zai hana ba zaki had'a hajar da haidar ba wato ai tuwo na maina Kinga wan nan duk naki ne" . "Kai Amma umma kin kawo shawara dama wallahi abinda ke ci mini tuwo a kwarya ke nan" "Yawwa Shi nagani ai sai ki tambayi Shi haidar in inya amince haka ita hajar din". "Yo sai ya wani amince ai kawai idan yana son Albarka yayi mun Biyayya". Hajar dake kitchen a lab'e ta daka tsalle tana rawa da Juyi,ganin hak'an ta ya kusa cimma ruwa.haka suka yanke shawarar inya dawo Ayi ta ta kare,wan nan ke nan. Tunda akai Wanga magana hajar ta canja salon yiwa Zee rashin mutunci ,yauma da zeey ke zaune a fararen kujeru ita da sadeey tana karanta Mata novel suna ta dariya ganin yanda jarumar book din ke tinb'ele. "Ke bani kujerar ki" sadeey ta juya hajar ce sai girgiza take tsam sadeey ta tashi ,zeey ta kalle ta "koma ki zauna". Hajar tace" ni da kayan wana Amma anunan gadara". tunkud'e sadeey tai taja kujerar a afusace Zee ta kai Mata maree tace wan nan ai k'arfin hali ne b'arawo da sallama, itama taja kujerar. Nan suka hau kici-kici tas wayar hajar ta fadi k'asa ta tarwatse,saboda jin haushi yasa ta rarumi Zee nan fad'a ya kaure tuni zeey ta canjawa hajar kamanni . Mami ce da husy suka fito "ke ba zaku rabu ba" sai da ta daka tsawa san nan suka hak'ura . Mami "tace Amma ke kam ba ai sirukar arziki ba ki rasa dawa zaki fad'a sai da k'anwar mijinki" . Hajar dake huci "tace mami wai daga d'aukan kujerar da kanwar ta ke kai yasa ta mareni ,ta fasan waya". "Lalle kin samu sake ,don k'anwar taki tazo ci ranii shine zaki hana yar gida sakewa to wallahi ki kiyayeni idan Shi haidar dinne ya baki lasisin kiyi abinda kike to wallahi yazo,karshe sai kin rai na kanki ,yau da ace kina da juna biyu ne shine zan raga miki zeey dake kuka tace "mami kiyi hak'uri wallahi ita ke Shiga hurumi na,asali ita tazo ta same mu awajen" . ko kallon ta ba tayi ba tace hajara su huce suka juya .,haka itama taja hannun sadeey suka shige gida,sadeey tace" wai ya zeey haka ake miki agidan nan ". Bata ce komi ba itama sadeey shiru tayi da d'aukan aneeyar in ta koma gida zata sanar da mum. ** Karfe 5 dai-dai saurayin husy yazo hajar tace zata had'a mai kayan motsa baki don salon tsokana gidan Zee ta Shiga ,suna zaune tanawa zeey kitso "ke zan dau aron cups da jugs na glass ,Zee ba tace komi ba zuwa tayi ta d'akko ta fita. Tana tauna cewgum da harara. Tsaki zeey tayi tace" banza kawai abinda kike mun insha Allah sai an maki irinsa,kuma ni da haidar mutu ka raba ,don zeey ta riga ta gano hajar na son haidar shiisa ma take wani abun da gayya Text ne ya shigo wayar Zee kalaman soyayya ne daga haidar murmushi tayi ta Maida mai da reply ,muryar sa ta keji har tsakar kan ta ,jin yana Mata wasu shu'uman kala mai yasa taji kewar mijinta dama yana kusa da ita..I miss u so much,text ya kuma shigowa karantawa tayi da gudu ta shige d'aki tai flat a bed sai murmushi take tana birgima ,dai dai lokacin ya bugo waya nan da nan suka hau hira mai Dad'i take ta manta da duk wani b'acin rai ......... *Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . *ZEENATU by Queen



 page35-36* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *Dedicated to Lubie nd bena* *After one month* Haidar na zaune zeey na kusa da Shi ta Dora kanta saman kafar sa ,yana wasa da gashin ta, "babynah gini zan fara don so,nake na d'auke ki daga nan mu koma sabon gidan mu Kinga ko ma bar mami ta sake". Dad'I ne ya ishi zeey "tace Allah ya yarda,kuma yasa mami ta yarda" ,hajara ce ta shigo sak'ale da jaka a hannu ta shigo falon ,had'e rai yayi "waya baki izinin shigowa" ?? Dariya tayi "mami ke kiranka" ta juya ta fita da murmushi kan fuskar ta ganin ta kusa cika burin ta, direct mota ta Shiga driver ya ja saboda yau zata koma gida ,Ga husy ma ta koma school. Da sallama ya Shiga zama yayi ya k'urawa tv Ido ganin ana wani film,sakkowar mami yasa yayi murmushi "Barka da warhaka mami". "Barkade my haidar" ,zama tayi ta kalle Shi "dama wata magana nakeso muyi dakai". "Mami fadi Inaj inki," gyara zama tayi "aure nakeso ka kara" a firgice ya d'ago kai "mami aure kuma"? "Eh Shi nake fada" Dariya yayi "mami Yaushe nayi auren harda zan K'ara wani k'ark'ari fa yanzu wata hudu". "Nuna min kalar ka, ai wuyanka yayi kauri saboda waccen figaggiyar ta hure ma kunne to ahir d'inka na gaya maka daga rana irin ta yau ka fara shiri ,don aure da hajara babu fashi". D'ago kai yayi "mami don Allah ki janye maganar nan wallahi Banda ra ayin mata biyu". "to ni kuma Inada buk'atar jika don naga alama matar ka bata shirya haihuwa ba ,ace wata hud'u yarinya bata fara laulayi ba, to bari ma kaji tun farko yarinyar batai mun ba don haka aure babu fashi ko kak'i ko kaso" Kan sa ne yaji yana sarawa "mami pls kibar maganar hajara wallahi Sam yarinyar bata da kunya" . "Aure de babu fashi idan kuma zaka nunan ban haifeka ba to Ga fili Ga mai doki,kuma nan ta wata biyu ba fashi" sama ta haye tashi yayi ya fita ya tsaya dai-dai bakin kofa ya k'urawa sama Ido "mayya sa mami ta canja mun tun San da nai aure ,kwafa yayi dole ya saita wa hajara kamanni . Wak'a take tana soya cincin ta baya ya rungumo ta my Zee ,juyawa tai tayi dariya "habiby ,bai ce komi ba sai sai Dan sakin jiki da yayi a bayanta , juyawa tayi "habiby yana Ga Kamar Wanda baka da lafiya" . Baice komi ba ya kalleta ya cakule Mata kumatu "baby ba komi". fita yayi ya Shiga motar sa tafiya mai nisa yayi ya tsaya ya dafe kai "oh mami pls ki janye" tsaki yayi ya d'auko wayar sa ya nemo layin hajara ,kashe murya tayi ta dauka "ke ni sa anki ne"? Tace "me nayi kuma"? "ke kika sani ,to wallahi ki janye duk wani k'udiri a ranki domin ni ba sa anki bane baki daga cikin tsarin matan da nake so ,if not wallahi zaki ga true colour dina stupid girl kawai" kit ya kashe. Tashi tai zaune ta fita "umma wai yanzu ni ya haidar zai ciwa mutunci kan maganar auren nan". umma "tace ki yi hak'uri bi komi a sannu dole dama afuskanci hakan ,inde yazo hannunki ai shike nan" ,nan ta had'e rai wallahi akan matarka zan huce. Sai wajen 9 ya Shiga gida mami na sama ta d'aga labule ,dariya tayi "yaro man kaza wallahi dole ka auri yar uwarka". Rungume shi zeey tayi habiby Ina kaje wallahi Ina ta jiranka kamo ta yayi ya ja hancin ta, na Dan je wani waje ne". dariya tai "tace zo muje kai wanka kallon ta yayi no dear kawon abinci inajin yunwa after sai nayi. d'akko flask tayi ta zuba mai white rice da miyar kifi da vegetables,tare da kunun aya mai sanyi ,ganin ya sa abincin agaba yana kallo ta taso "habiby kaci mana". Ganin hakan yasa ta d'akko ta fara bashi abaki yana ci suna hira har ya cinye. Tashi yayi ya shige d'aki yayi wanka yayi sallolinsa ya kwanta saboda jin kansa na ciwo, jin alamar bud'e kofa Sai yayi sauri ya juya ,kwanciya tayi ta bayan sa "habiby yau tabbas akwai abinda ke damun ka pls gaya mun." "Baby ba komi kaina ke sarawa" ,tashi tayi ta d'akko mai magani ya sha da kyar de sukayi bacci kowa da irin tunanin sa. *Washegari* Mami tasa akai kiran zeey Shiga tayi da sallama mami ta kalleta ,"dama nasa a kiraki ki ne saboda in shaida miki karkiji Abu daga sama ,ni nan mahaifiyar haidar na bashi Mata ya aura kuma ba wata bace sai hajara ,saboda ke naga tunda ya aureki muke can jaras dashi don haka dole ya auri yar uwar sa". Kukan data ke k'ok'arin had'iyewa yasa ya fito ,da gudu ta fita ta tsaya tana haki,"me nai ma matar nan? Ina dai dai gwargwado ganin na kyautata Mata duk bacin ranta bana so ,haka haidar dai dai gwargwado muna zaune lafiya,don Ban samu ciki yanzu ba har me wata hud'u shine za a San Ido",durk'ushewa tayi agun tana kuka ,tabbas basa k'aunata . Mami ce tsaye a kanta tayi shirin fita ,"au ke naki salon kishin kenan tun d'azu daga miki zan cen aure kina nan kina kuka ,ko tare aka haifo ki keda da haidar ku?, to kisani mijin mace hud'u ne". "Dan Allah mami kiyi hkr ,in wani abin nai miki , sai na gyara","baki min komi ba kawai inaso yayi aure ne" ,mota ta Shiga driver ya ja. Tunda ta Shiga d'aki take kuka, bata tab'a ganin amaryar da wata hud'u da aure ace za ai Mata kishiya ba ,kayanta ta fara tattarawa tana kuka haidar ne ya shigo gidan jin alamun kuka yasa ya Shiga d'akin ,idon sa ne ya kai kan kayan da take had'awa ,Janyo ta yayi juyowa tayi ta kalle Shi ,rungumeta yayi nan ta kuma b'arkewa da kuka sosai ...... *Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . *ZEENATU by Queen



 page37-38* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. ? *®NWA* *Dedicated to Lubie nd bena* Queen



 Bubbuga bayanta yake sai da suka Dad'e a haka San nan ta zame jikinta, tana share fuskar ta kayan nata ta cigaba da had'awa sai da ta gama tsaf San nan ta d'ago haidar ya buga uban ta gumi "tawan wai me zaki da jaka ne ". Cikin k'unar rai "tace zan tafi gidan masoya wato gidan iyayena ,yau aka shaida za aima aure ni kuwa dana zauna na ganka da wata gwanda na tafi gidan mu". Damm! K'irjin sa ya buga ta Shi yayi ya kamo ta direct kan cinyar sa ta zauna "zeeta ki mini uzuri ba laifi na bane, jiya a binda yayi ta nuk'urk'usa ta kenan,baby ke nake so karki barni baza ai auren nan ba duk yanda zan Bazan yar da ba saboda ke kad'ai ce zabina ZEENATU Ina sonki son da bana ganin Kowacce mace zeena kina mun abubuwan dana keso to mai zai sa nai miki kishiya. Zee mami ke da wan nan k'udurin don Allah ki zauna dani karki tafi nafi so ki kasan ce kullum kina tare dani saboda in bake Bazan iya ba". "My habiby nima Ina tare da kai, Kayi mun alkawari wata ma hudu ace za ai mun kishiya ,donni nafi kowa bakin jini" Sorry my baby d'aukan kayan yayi ya zazzage ya Maida su cikin wardrobe ,har wani D'an zazzabi Zee take ji, ganin hakan yasa haidar yaje restaurant yayo musu take a way ,da kyar take ci saboda d'acin data ke ji azuciyar ta ,abinda yake nuk'ur-k'usar Zee saboda ganin yanda mami ke Mata Sam ta rasa dalili . *Bayan kwana 2* Haidar da zeey sun manta da maganar auren da mami ta bijiro musu da Shi,soyayyar su kawai suke haka suka kuma lik'ewa tamkar mayen Karfe . Mami Dake zaune a falo ta had'e rai tana jijjiga ,haidar na gefe husy na zaune gefen k'afar ta . "Ban isaba ko? to wallahi na baka nan da one week muddin baka zo min da zancen ka Aminta ba to kasa aranka zaka Ga abin mamaki wallahi". haidar ya dafa kansa jikin sa har rawa yake abubuwan sun Cakud'e mai "mami ko ni ta b'angarena beci ace na K'ara aure age D'ina ayanzu ba" . Husy ta kalli mami yanda take ji tamkar ita za aiwa kishiya saboda Allah yayo ta da kishi ko wata taga zai ai wa kishiya sai taji haushi. "Mami don Allah kiyi hakuri da zancen auren nan wallah tausayi Anty Zee ke bani ,duk abinda ma nai Mata watannin baya hajara ce ke zugani Amma wallahi yanzu tana ban tausayi Dan ba kiga yanda ta rame ba. Wallahi mami duk da hajara sis D'ina ce Amma da kawai ki bar zancen auren nan tunda Kinga shima yaya haidar d'in baya so. Gwab'e Mata baki tayi "yimun shiru shasha shar banza 'yar 'yar uwar tawa zai ce baya so to duk kunci gidan ku, wallahi idan kuka Ga ba ai auren nan ba wallahi sai in bana raye" . Tashi haidar yayi "ni mami fa bana son ta". kallon sa tayi "ni kake gaya wa haka take tasa kuka nan hankalin sa ya tashi ya zauna mami kiyi hakuri don Allah . Kallon sa tayi wallahi sati d'ayan Dana baka inde ya cika to wallahi ko ka ki,ko kaso a babu ruwa na ,take ta tashi tayi d'aki nan husy ta Matso "ya haidar am so sorry komi zai dai- dai ta". Kallon ta yayi sis "mayya sa mami ta daina so na? ,meya sa mami yanzu ba ta son farin cikina"? . "Duk don saboda Zee batai Mata bane ba ,kayi hkr yaya dole mu bita ahankali tunda mahaifiyarmu ce". Bayan kwana 2 gidan ya riki ce Sam mami batawa haidar magana gashi kullum sai Zee tasha zagi,yau ma Zee na zaune ta gama had'a kunun gyad'a sanin mami na son Shi ,hakan yasa ta d'auka ta tafi kai Mata . Bayan ta gaishe ta ta ajiye kunun ,mami ta ya tsine fuska "ke d'auke wan nan shirmen naki kona watsa miki a jiki". Zee "tace mami don naga kina k'aunar sa ne". afusa ce ta d'au kunun ta watsa Mata a jiki, K'ara Zee ta saki ta mik'e tsaye . jikinta na rawa saboda zafin ya shige ta. mami dake huci "wallahi yanda kika hanani sakewa Daa d'ans kema ba zakiji Dad'i ba shu'uma kawai, wai ke ki sisina ko " . Da k'yar Zee ke taka k'afar ta ta fice daga gidan ta Shiga side din ta ta gyaraa jikinta ,wajen duk yayi jajawur alamar zai tashi Ga radadi daya ke Mata ruwan sanyi ta d'akko ta zuba agun san nan ta samu sa Ida. Cigaba tai da kuka ta d'auko phone dinta zata bugawa mami ,gargadin da tai Mata lokacin da za a kawo ta ne akan rik'e sirri da yawaita hak'uri yasa ta aje ta fasa kiran. "Na d'au Alk'awari ba Wanda zai San abinda nake ciki , Bazan gayawa yan uwana ba ,tabbas da can nayi k'uruciya da rashin hak'uri ,ashe haka hakuri yake da wahala, tabbas wani abin ke kore wani , gashi tsananin son haidar ,gashi yasa mun zan zama dashi hakuri yazame mun dole,na gode miki mum da kika jajirce ganin na koyi hakuri gashi yanzu na riske Shi a zaman aure na insha Allahu zan jure duk wani k'alubale". haka tayi ta magan -ganun ta da kukan tamkar tana gaya wa wani, tashi ta shige daki ta kwanta baccin karfi da yaji ya zo Mata Wanda bata shirya yin sa ba ,tunda bata Dade da tashi ba..... ... *Writting* *Queen



* . . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . . . *ZEENATU by Queen



 page39-40* . ?. ?. ? ?. ?. ?. ? . ? *®NWA* *I Dedicated this page to Autarhajiya,Antysis,Anee, ummul fadeela &salamatu faransa thank for d care* *Queen



* Dama ita Rayuwa bata tab'a zama dai -dai yau fari gobe tsumma,duk yanda kake tsammanin rayuwar ka yanda ka tsara ta,kana tunanin hakan zai kasance to kayi kuskure yanda Allah ya tsara maka haka zaka bita,dole hak'uri ya zamo babban jigo arayuwar mu , hakuri baya tafiya abanza kuma mai hakuri Shi kan dafa dutse har yasha roman sa. *********** Zee dake tsaye bakin gate tana jiran zuwan Anty bara domin tayi Mata waya tana kan hanya itada sadeey .zumud'i ne yasa ta kasa hakura taje k'ofa ta tsaya.motar mami ce ta Danni kai driver na tuk'i hajar ce ta fito bayan ta tsaya driver ya ciro Mata Jakarta ta shige ciki. Adaidaita sahu ne ya tsaya Antybara suka fito shigar su gate din gidan zeey ta rungumeta tana murna part din ta suka shige ruwa da kunun aya ta kawo masu suka sha da yake 11 ne shiisa bata D'ora girki ba zama sukayi suna hira Anty sai bin Zee da kallo take. "Zo nan Zee". juyowa tayi tazo ta zauna "Anty Yasu boy sultee"? . "yana boarding school". "wai ni Zee baki da lafiya ne ,naga kinyi fiyau kinyi zuru-zuru"?. Dariya tayi "nayi rashin lafiya ne Anty" haka sukai ta hira,bum aka falon hajara ce ke girgiza harara ta kai musu ta shige kitchen ta d'auko ragowar kunun data gani a gidan sanyi tayi waje. Anty ta jinjina kai "oh ni bara yau naga gadara, ke Zee wan nan wace ta shigo ba sallama ta shige kitchen ta dauko Abu"? Nan Zee ta tab'e baki kad'an ma kika gani Anty yar uwar su haidar ce wallahi haka take mini kullum . tuno da auren ta da mami tace haidar sai ya yi yasa ba tai aune ba hawaye suka zubo Mata da gudu tayi d'aki. Ahankali Anty ya tashi ta kwantar da baby data ke goyo ta bita d'akin. Flat ta ganta kwance kan bed tana kuka zama tayi ta d'ago ta "my Zee Meya sameki ne ,?wai meya faru gaya minn". shiru tayi ,Anty ta kuma tab'a ta "Zee ta . Idan baki gayan ba wa zaki gayawa tunda dai daga gani akwai matsala". Taso wa tayi ta rungume Anty "tace Anty basa sona tunda nai aure Banda kwanciyar hankali uwar mijina bata k'aunata kullum kyautata Mata nake Amma bata gani ,ita wadda kika Ga ta shigo cosin sis din sa ce ,to haka take mun gadarar nan ,yanzu matsalar mami tace wai sai haidar ya aureta saboda wai ni har yanzu ban samu ciki ba" Hankakin Anty ne ya tashi tace "yanzu ,kina cikin matsalar nan Amma kikai shiru ba Wanda ya sani sai kace ba kida mafad'i, Ah lalle na yarda Zee kin zama silent yanzu ,kuma kinyi hankali". Tashi tayi ta na kai kawo gaskiya banji dad'in wan nan abin ba, kina yarinya ace wan nan matsalar ta faru dake ta zaman aure Ga kuma kishiya ,sai dai ba zan zama uwar banza ba . Zee abinda zan gaya miki ki K'ara hak'uri kinyi kyan kai daba ki kai maganar komi dangane da zaman aurenki gida ba ,tabbas haka yana da kyau ,ki dage da addua Allah shine masanin abinda ke fili da b'oye yawaita zakiri da hailala yana gusar da bak'in ciki karatun Qur ani ya zamo abin dubawar ki ,ki Maida komi ba komi ba Allah shine mai sakayya Ga duk Wanda Aka zalunta". Taji dad'in nasihar Anty haka ta fito suka Shiga kitchen don D'ora sanwa,ba yanda Anty zatai Amma tana cikin damuwa idan ta kalli Zee da kishiya. Sai wajen la asar ta tafi tana dad'a jaddada Mata ta K'ara hakuri. Bayan zuwan Anty gida mum na falo tana ninke kaya,Anty ta zauna mami ta kalleta "har kindawo daga gun 'yar taki'? . Murmushi tayi "lafiya Lau take kam" Amma sai dai niko ta sanar miki da zancen K'arin auren mijinta Dafe kirjii !tayi bazata taji maganar nan dai Anty ta gaya mata duk abinda Zee ke ciki Allah sarki Zee nayi Mata jinjina Anan Godia Ga Allah da yasa har ta iya boye hakan Aa ta zama mai hakuri. Ba yanda mum zatai in Banda zuciyar ta dake k'una Kamar zee ace za aiwa kishiya har Yaushe akai auren,tabbas ni Bazan hana sunar annabi ba. domin Shi ya halarta,zan dage da addua Allah ya basu zaman lafya Haka suka yini suna hirar nan cikin jimami mum ta bugawa Zee waya tai Mata nasiha ,mai ratsa jiki. *Bayan kwana 7* Yau kwanakin da mami ta d'aukar wa haidar ya cika yana zaune wayar sa tayi kara, mami ya gani ya d'auka kazo Ina son ganinka, gabansa ne ya fad'i akasalance ya tashi,Zee ma haka,Shiga yayi yaga mami da umma mahaifiyar hajar akan kushin Ga hajara a k'asa a gefe. Zama yayi ya gaidasu mami ta kalle Shi "to haidar yau ne dama mukayi alk'awarin ayanzu inason ji daga gareka ,Kafin nan bari muji ta bakin k'anwarka" Mami tace" hajar kina son haidar zaki aure Shi"? Sunkwai da kaai tayi na gulma "eh mami na amince". Murumshi tayi ta juyo Ga haidar to "Ina jinka ka amince ne"?. nan ya gyara zama" mami don Allah ki hakura da auren nan ". Kalas ta ce tare da d'aga hannu insha "Wallahi Wallahi nan da wata d'aya za a daura aure". "Inde kana son gani da kyau to ka bini na riga na gama magana". Tashi yayi kawai a kasalnce ya Shiga mota ya figa tafiya yake kawai saida yayi nisa ya tsaya hawaye na tsiyaya. Zeey kam ganin har dare bai dawo ba yasa ta Shiga damuwa sai 10 ya Shiga da gudu ta tareshi "habiby na Amince kayiwa mami biyayya banso ka Shiga fushin Allah" . Rungumeta yayi "Allah yayi miki Albarka ,zanyiwa mami biyayya Amma Alal hakika bana son hajara da aure ,banso yi miki wata tazo matsayin kishiyar ki ba" "Kaddara ce habiby in Allah y hukunta ba yanda zami taimakon sa tayi yayi wanka yaci abinci suka je sleep. *bayan kwana 2* Kowa da irin tasa k'addarar tabbas baka isa ka ketare ba ,mutuwar Aure K'addara ne ,domin Aure rai gareshi duk lokacin da kaga ya mutu to dama Allah ya tsara hakan. Afusace hajar ta Shiga side d'in zina da misalin K'arfe hud'u na yamma , ball tayi da jakar Zee dake kan kujearar ta haye tana girgiza Zee kawai bin ta da kallo take haka ta canja tasha ,Zee ta dauka ta canja . Ganin hakan hajar tace ke dallah yanda kike tak'amar gidanki nima haka don nan da wata d'aya kin zama bora. Kitchen ta Shiga ta d'akko lemu ta tsiyaya acup ta tasha ta d'aga Shi ta rotsa agun ,zuciya ce ta d'ebi Zee ta wanke hajar da Mari so biyu. Nan itama ta rama cakumar juna sukayi ko wacce najin kishi Kamar ta murkushe daya??sai naushe naushe suka ,Zee ta samu sa a ta danna hajar tana duka duk da hajar ta fita jiki. Da gudu mami ta shigo lokacin Zee ta fasawa hajar hanci mami "tace tabd'i yau wallahi ko kinfi mayya naci sai kin bar gidan nan. Zee da idonta ya rufe "tace mami ki duba irin abinda ta ke mun yau ta kaini bango" . "Eh to ke kuma yau zaki koma gidan iyayenki dama kin rikitamun yaro" kuka Zee keyi ,ta tsugunna tana bawa mami hakuri. Haidar ne ya shigo ko zama bai yiiba mami "tace kazo ka sallami yarinyar nan don. Wallahi yau se ta bar gidan nan" Bai gane me ya faru ba Haka ya tambaye su ko wacce ta fad'a mai ,. nan ya b'allawa hajar Mari "ban hanakii shigowa ba".mami tace" lalle haidar bansan an shanyeka ba sai yau, to wallahi ka zab'a komi ko Zee". "Mami don Allah ki hak'uri karki Kashen aure" . "Idan ma na kashe wani zan ma" kuka yake yayin da Zee ma keyi. "Idan nice ma haifeka ka saki yarinyar nan in ba haka ba wallahi senayi maka baki ka b'alb'alce. Zee ta d'ago ta kalle Shi habiby kabi maganr mahaifyar ka don ka ga dai dai . "Zee Ina son ki, Bazan iya rayuwa without you ba" kuka tasa. "Mami tace inajiranka,". Kallon Zee yayi" Kije gida zan zo , ba haka nake so ba ,so nake inji kwalemar saki" . kuka ta saka "yau haidar ka nunan iya kata". takarda ya d'auko ya rubuta saki d'aya hannun sa ke rawa . "Bani ta kardar" mik'a Mata yayi ta karb'a ta karanta tareda murmushi. Gud'a hajar tayi .tayi wa Zee gwalo. nan mami ta mik'awa Zee takar darr sauka fice . haidar ya tsaya "Zee ki gafarceni har abada Ina sonki ba ason rai na bane Kinga de duk agabanki abin nan ya faru,din Allah karki tsaneni wallahi Zee har bada INA TARE DAKE." ba tace komi ba ta kalle Shi haidar "I will never forget u in my life & I will miss u everyscan. D'aki ta Shiga ta sawo hijab zumbulele tafito tana hawaye direct fita tayi haidar ya bita ko wai waye bata ,yi haka ta fita daga ai nihin gidan,haidar Kamar jela sai binta yake ,jefa k'afar ta kawai take ,wani adaidaita sahu ne yazo wucewa ,tsayar da Shi tayi ta shiga ya ja ,nan ta tusa hijab d'in bakin ta tana kuka ,shikwa haidar ganin adaidaita sahun yaja kawai ya zube kan gwiwoyin sa yana kuka tamkar k'aramin yaro....... * *Story & written* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . *ZEENATU by Queen



 page40-43* ?. ?. ? ?. ?. ?. ? *Oct 10,2016* *Queen



* Da sauri ta Shiga gida mum na yiwa faty tsifa gunjin kukan tane yasa ta dago,ta kalle ta ta dafe kirji !ganin yanda take gurshek'en kuka. "Ke meye"?. mum ta am bata tare da mik'ewa tsaye faty ta mik'e mum ta tashi ta kamota ta zaunar kanta ta D'ora kan cinyar mum tana kuka da shesh-sheka sai da tai mai isarta ,mum da tai tagumi tace "idan kin gama kukan sai ki gayan dalili". Matse Ido tayi "mami ta saka haidar ya sake ni," dafe kirji mami tayi,"lahaula Waka k'uwata illabillahi Yanzu zeena akan K'arin auren da zaiyi sai da kika tashi hankalinki ya sako ki",dafe goshi tayi inda hawaye ke zirara afuskarta. "Mum wallahi ban tashi hankalina ba", nan dai ta kwashe duk irin zaman da sukai tare ta gaya Mata ,numfashi taja "mutuwar aure ba Dad'i ballantana irin naki da k'ar-k'ari watanki shida (sis month) Amma har ya mutu, yi hakuri zeena da sanin Allah kinji duk abinda ya faru Kaddara ne,Ita kuma uwar mijin naki da tai silar komi Ai Allah baya bacci,duk abinda mutum ya shuka Shi zai girba". Zazzabi ne ya rufe zee magani mum ta bata tasha ta D'an kwanta take bacci ya kwasheta,da wasu rikitartun mafarkai ************** Da k'yar haidar ya koma gida ko kallon inda kofar gidan yake baiba, motar sa kawai ya Shiga a Afusace ya fice . gidan su kb ya zarce sai kuma wata zuciyar ta canja mai ra'ayi kwana yayi ya canja hanya tatarar gudu kawai yake tafiya mai nisa yayi bai tsaya ko Ina ba sai gidan gonar mahaifin sa daya ci gado. Bayan ya Shiga ya fito ya tsaya ya tak'urawa korayen shuke-shuken dake gurin Ido ,ya Dad'e a haka San nan ya bud'e mota ya d'auko robar paro d'aya ya kunce ta kwara akan sa yarda Ita yayi yad'an daki kansa. " mami ya kike so nayi Ina sonta banso auren na ya mutu ba ,mami bana son hajar ,iluv u zee ta" Kamar mashayi haka yai ta sumbatu Shiga can ciki yayi ya d'au darduma ya kwanta a kai ya k'urawa sama kallo ,Sam bai damu da duhun daya k'arato ba. Tashi yayi ya Shiga wani k'aramin gida dake cikin gidan gonar already yana da key ya bud'e ya Shiga yai zaman sa zuciyar sa na tuk'uk'i da zafi , wayar sa ya d'auka ya kira number din zee switchoff yaji ,wulli yayi da wayar,Kamar ya kurma ihu idan ya tuno Sun rabu da Zee din sa..... Ran dandy idan yayi dubu ya tashi lokacin da mum ke gaya mai mutuwar auren zee takadar da Zee ta bata ta bashi . "Ina zeena din"? "bacci take zazzabi ne ma yarufeta na bata magani ta sha". "Amma abin nan da mamaki aure 6month a sako mini yarinya ni ban tab'a sani akwai matsala acikin zaman su ba ganin bata tab'a kawo k'ara ba". Mum tace "ay tayi kyan kai daba tazo ta gaya mana ba da tuni ran mu ya baci kuma abin yazo yafi haka". Dady yace ba hujja nace data fad'a ai da ko tayaya an samar Mata mafita, Amma ba komi komi muk'addari kuma duk abinda mutum yayi Shi za ai mai ,wallahi ba zan nemi yaron nan ba sayyazo da kan sa ,yarinya k'arama an mai data bazawara" Mum data gara zama tace "Sai hakuri K'addara ta riga fata". "Yanzu ya kamata ta tashi Ita zeena saboda dare yayi" dai -dai lokacin ta fito nan suka bita da Ido gaida dady tayi . "Ga alama nan duk ta rame koda na San zeena nada fad'a da rashin hak'uri tabbas nasan wan nan Ita aka k'wara bawai don bin baya ba".mum Ita de hak'uri take ta bawa dad ganin yanda ya harzuk'a. Haka su sadeey da sadiq sukai ta jimami nan ma sadeey ta ware baki ta fad'i duk irin abinda akewa zee lokacin data je Dad yace" 'yata bazata koma ba kuwa ,koda sunzo biko domin Ina sonta" A ranar kowa na jimami duk basiyi baccin kirki ba zee sai juye-juye take saboda Sam ta kasa jin dad'in baccin saboda yanda ta Saba jinta jikin haidar duk setaji wani iri. Kuka ne ya kubce mata kewar haidar ke nuk'ur-k'usar ta da soyayyar sa ga wani kishi da ke cinta ,gefe kuma haushi yake bata duk da tasan ba shida laifi...... *Godin gareku masoyana aduk inda kuke nima Ina k'aunar ku ,Allah ya barmu tare .luv u oll* *Story & Writting* *Queen



* . . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . . . . *ZEENATU by Queen



 page44* ?. ?. ? ?. ?. ?. ?. *®NWA* *Queen



* Yau kwana biyu da barin zee gidan ,Amma ab'angaren mami hankalinta ba a kwancee ba,domin tun fitar haidar bai dawo ba ,hankalin ta duk a tashe yake wayar sa duk a kashe ,yauma dat ake zaune waya a hannu tana kira jin ta Shiga yasa tayi dariya wayar nata ring Amma ba a d'auka ba sai can ya d'auka. Mami "tace kai yanzu haidar don mai afkuwa ta afku ,shine zaka K'i kwana a gida ko ,to Ina maka magana da babbar murya ka dawo gida" kit ta kashe . Juyi yayi kan gadon yayin da ya k'urawa sili ido duk ya fad'a Kamar mara lafiya ,ahankali ya mik'e yana gauraye hanya yaje ya Shiga toilet yayi wanka .yasa jeans da tsht ya fito motar sa,ya Shiga bai tsaya ko ba, sai k'ofar gidan su zee yan mintuna yana tsaye sai ga fitowar dady da yake safiyace da sauri ya fito dady ya kauda kai tare da Shan kunu . Gaida Shi yayi ya amsa a takaice. "Dady son Allah kuyi hkr ba lai fina bane" D'aga mai hannu dady yayi dama banga laifin ka ba Amma sai dai ka sani idan biko kazo zee bazata koma ba" Daga haka yai wucewar sa. K'urawa k'ofar gidan yayi da Ido San nan yaja mota ya tafi. Fuskar nan tamkar an aiko mai da sak'on mutuwa ya Shiga falon Mami ,tana zaune itada hajar suna hira ,ganin sa yasa hajar ta kashe Ido an d'ame jiki sai wani barbaza Ido take ko kallo bata ishe Shi ba . Mami "tace to kaga duk abububwan da suka faru a yanzu ne zaka San kayi aure so nake afara maganar bikin nan kasan lokaci na wucewa". "Yanzu Mami baza ai maganar dawowar zee ba" . Hannu ta D'aga mai kaini na bar wan nan maganar an raba ka da k'wallon mangwaro Dan ka huta da k'uda Amma kai sai bibiya kake, k'walawa hajar kira tayi. Cike da karairaya ta fito "Mami gani". "To ga hajar,nan kaje ku fara shirye- shiryen yanzu so nake ka kaita ta zabi kaya Wanda zaka sa Mata alefe". Had'e rai yayi be ce Komi ba ,ya tashi ya fita . Mami tace "yaro ana so ai ma gata kai kana shirme ga hajar dam b'asheshiyar yarinya Amma ka zauna kana walagigi kan wata zee". Tsayuwa tayi a ajikin motar sa tana hira a waya ya fito ,dosar motar yayi yana waya ,direct gaban motar sa ya Shiga ya kunna. D'ago kan sa yayi " Ke bar nan" . juyawa tayi "ai kaji me Mami tace dai". Fito wa yayi ya kai Mata hauri da gudu ta matsa ,Shiga motar sa yayi ya figa Tana tsaye tayi k'wafa wallah duk randa guy din nan yazo hannu na, zai gane baida wayo,tsaki tayi ta Shiga gida. *After 1week* ******** Zee kam ta zama salihar k'arfi da yaji tun sanda ta dawo take zazzab'I ,yauma data tashi jikin ba D'adi sai. Amai da take kwararawa. Ga yawan kuka tana zaune bayan maganin da tasha ,wayar ta tayi ring ganin new no yasa ta d'auka . Tsaki taji anyi a ciki "nice hajar dama na bugo na gaya miki ne bikin mu da tsohon mijin Ki , saura sati 2 nayi winning akanki sai kuma kibi wani sarkin haidar nawa ne yanzu" Zagi zee ta k'unduma Mata yayin da kishi da k'unar zuciya Ke cinta . "tace karki K'ara kirana na tabbata haidar baya sonki duk Ki gama azarb'ab'inki ,Matar shige kawai.... Aje wayar tayi ta fara kuka take zazzabi ya rufeta ,tashi tayi kawai jiri ya d'ibeta ya ta fad'i akan cikin ta. Yar K'ara ta saki mum ta Shiga aguje ta ganta kwance ga jini na bin k'afar ta ,mamaki mum keyi,shigowar sadiq yasa tace yayi sauri yaje ya naimo mai mota bai Dad'e ba sai gashi da D'an adaidaita ya taro suka ciccib'e ta sai NAGARTA HOSPITAL nan aka kar b'eta ganin yanda jini Ke bin k'afar ta yasa suka rufa akanta. Bayan hours doctor ya fito nan mum ta bishi yayi Mata bayanin ta yi 'barin ciki na one month sakamakon firgici data Shiga. Mum ta kallo doctor "ai doctor Inaga Ita kanta bata San tana da shigar ciki ba, gashi har ya zube, ni kaina sai yau.Nama fahimci hakan ganin yanda take amai ". doctor "yace to madam kin san akwai cikin daba ba a gane shima da wiri wasu sai ya kai 2month suke ganewa" Drugs ya rubuta, San nan yace mun bata gado sai gobe idan ta D'an samu hutu sai a sallameku Sadiq kam gida ya koma Dan kawo wa Mami abinci, tunanin kiran haidar yayi sai kawai ya danna kiran sa,Haidar na zaune a d'akin kb suna Maida zance inda kb Ke dad'a bashi kwarin gwiwa,daukan wayar yayi ya Kara a kunne " Helo zee bata da lafiya ta samu miscarriage yanzu ma tana asibiti Nagarta" bai,jira mai zai ce ba kit ya kashe. A kid'ime ya tashi ya fice motar sa ya fafara ya Shiga direct nagarta hospital yaje mum na zaune yaje ko kallon sa ba tai ba sai daya kuma gaisa ta San nan ta amsa . " Mum naji ance ta samu b'arewar ciki". Eh hakane dafe kai yayi abinda Mami Ke so da tayi hkr ta barmu a tare da tuni Ita zatafi kowa farin ciki. Hawaye ya share ya tashi ya fita yace zai dawo, gida ya zarce shigar sa falon mami yaji hajar na waya. "Ai in gaya miki yau mukai,waya na ci Mata mutunci ,wai Sun na gaya Mata magana mai d'aci ,ai zee tana bani matsawa" . Duka taji ta ko Ina saida yayi Mata lilis San nan ya tsaya,lokacin Mami ta fito . " Kai haidar me tai ma yana haki Mami tabbas itace silar b'arewar cikin zee wallahi". "Au ciiki gareta, Ita bata samu lokacin da ake so ba.ai sai kayi hak'uri tunda zaka auri hajar irin haihuwa." Kuka sosai take nan Mami ta Jawota tana bata hak'ur. Fita yayi ya Shiga side din sa ,ji yake Kamar ya had'a kayan sa ya bar garin,ga tsananin kewar zee fake nuk'ur-k'usar sa, shawarar kb ya tuno na yayi hkr yaiwa maminsa biyayya insha Allahu ba zai tab'e ba.. *Story &Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . . *ZEENATU by Queen



 page45-46* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ?. *® NWA* *28 Oct 2016* *Queen



* Washegari da sassafe haidar ya tashi yaje ya sayo su fruit da yawa ya tafi nagarta hospital Ahankali ya bud'e d'akin ya Shiga zee ce zaune ta jin gina da fillow tana Shan tea, ganin sa yasa ta k'ware mum tace kiyi fa ahankali ,Sun gaisa da mum ya tambayi jikin zee . Ita kam Sunkwai dakai tayi, yayinda 'kirjinta Ke bugawa ji take kamar tai hug d'in sa Tsayuwa yayi ganin lokaci ya k'ure yasa ya d'ago sukaa had'a Ido da zee ya sakar Mata murmushi ,murmushi ne yaso sub'uce Mata sai ta basar don bata San yin dariyar," ya jiki zee"? . Ahankali ta dago ,"tace da sauki". Sallama yayi musu ya fita. Mum ce ta tashi ta rik'e zee suka Shiga toilet ta fito wanka zee tayi ta fito tasa kaya ,shigar doctor d'akin ya je ya d'au file dinta ya duba ya d'an d'ago ya tambayeta, nan ta amsa mai da bata jin ciwo sai jiri da take ji . "Karki damu kan Anjima zaki dawo narmal" nan ya rubuta musu sallama ,wajen 1 suka tafi gida Kafin yamma zee tayi garau. ************* Direct haidar gun aikin dad yaje nan ma duk akan maganar komawar zee ne Amma dady ya bud'awa idon sa Toka yace shikam bazai wa zee dole ta koma ba ,Amma idan Shi ya Janyo hankalin ta to ,asanyaye haidar ya tashi ya tafi gidan su kb . Wak'a Ke tashi a laptop d'in kb ta guzarish yaraf haidar ya zauna kb ya d'ago "ya aboki". Haidar yace" kaide bar ni nasan me nake ciki ,matsalar dad din zee yaki bari ayi zancen dawo warta gashi banso iddar ta ta fita . Kb yace" to kai na farko Mami ta amince ma kadawo da Ita"?. "Aa kb kwai nine" "Lallai haidar kafara shawo matsalar ka da Mami kawai idan zamanka da zee bai k'are ba zata dawo. Kuma kasan dole dad d'in ta yaji ba dad'i " "Ya zancen auren naka da hajar". K'aramin tsaki haidar yayi "kana son B'atan rai". "to ya zakai dole kaiwa mamanka biyayyaa" Shiru yayi na 'yan mintuna sukai sallama ya tafi. *Bayan 2week* Yau ake yinin hajar gidan ya cika da Mata sai kid'a Ke tashi hajar na zaune ad'aki Ita da k'awayenta sai dariya suke . Wata ta kallo hajar tace "Amma fa kina da sa a kin auri Wanda zuciyar Ki Ke so". tab'e baki hajar tayi kun san kwa gwagarmayar Dana sha ,kan na same shi ,sai da na fa rabashi da wan nan banzar matar tasa" ,tafawa sukai ai wata tace "ai dama Ke k'alatacciya ce". "to ya San ranki". Washegari aka d'aura auren hajar da haidar ji yake kamar ya mutu saboda bak'in ciki, fitowa yayi Daga d'aki don dama yace bazashi d'aurin auren ba jin gud'a acikin gida hantar cikinsa ta kad'a . Hajar ya gano taci kwalliya Ita dasu husy ko kallo bata ishi Shi ba ,zuwa yayi ya d'au kayan sa kala 2 ya watsa a mota ya fafareta ya tafi gidan gonar sa don samun sa Ida. *ZEENATU page47- 48* ******* Kuka sosai zeey Ke kwasa tun safe data tashi jin amsa da sadiq ya bata na an d'aura auren haidar da hajar, kishi Ke nuk'ur-k'usar ta,da haushi "Lalle zee kina da Aiki" cewar Mami,"na gaya miki Ki Maida komi ba komi ba ,kiyi hakuri kowanne bawa da irin tasa jarabawar,Kije kitchen Ki d'au abincinki kici". Tashi tayi tana share hawaye ,sallama akai ta amsa magajiya ce wata mak'ociyar su ta shigo",Aa zeena saukar yaushe" murmushi tayi suka gaisa ,binta tayi da kallo ta jinjina kai. Gaisawa sukai da mum take sanar Mata haihuwar k'anwarta,gulma na cinta ta basar ta tashi ta fita. ******* Acan b'angaren haidar kuwa ankai hajar tun shekaranjiya Amma Shi Sam Mami ta nemeshi ta rasa yau kwanan hajar 2 duk ta tayarwa da Mami hankali ,ko kunya bata ji ,haka take d'irkar kayan Mata San ranta,Mami kam sawa tayi aka kira kb ,ta tambayeshi haidar nan ya sanar Mata bai San inda yake ba ,Amma yayi Mata alk'awarin neman haidar duk inda yake ,Da haka suka rabu. Wayar haidar ya nema nan ya sameshi yayi mai nasiha ba yanda ya iya haka yace zai dawo Anjima . Tsaki yaja bayan Sun gama wayar ya nemi Layin zeey ya kira kirr 3 times ba a d'auka ba ,kiran na hud'u ta d'auka ,wani sanyin dad'i yaji "zeeta"ya ambata. Wani tukiki ne Yaa kama zee ta kashe wayar ,again ya kuma kira ta kashe sai ana ijin mum tace ta d'auka bayanda zatai ta d'auka. Haidar yana zaune ya mike "pls my love life" daka tar dashi tayi kabi maganar iyayenka haidar kawai kamanta dani . Kafin yayi magana ta katse cillar da wayar yayi ya tashi yana zagaye falon Muk'ullin car d'in sa ya d'auka ya fice Allah ne ya kaishi gida a salama saboda irin gudun da yake cike da firgici. Yana zuwa gun Mami ya Shiga ko amsa Gaisawar sa batayi ba ,ta wanke Shi da Mari huci take "kana son ka nunan baka jin magana haidar meya sameka ne ,an aura maka yarinya yau kwana 3 ka tafi bakai ba dalilin ka,karka manta yarinyar yar uwarkace to ahir d'inka na gaya maka ,yanzu kuma ka tashi ka je gun ta" Hawaye dake zuba a idon sa,tamkar mace ya d'ago Mami kiyi hakr,tausayin sane ya kamata Amma ta gintse, a salub'e ya tashi ya shige gida. Tana zauze taci wasu shegun riga da Wando Sun d'ame ta duk Sun fito da ilahirin halittar ta ,tashi tayi ta tawo zata Rungumeshi ya D'aga Mata hannu " don't touch me". Daki ya shige ya kulle . Tabe baki tayi ta cigaba da chatin d'in ta..... *Story & Writting* *Queen



* . [10:13pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . *ZEENATU by Queen



 page 49-50* ?. ?. ? ?. ?. ? ?. ? *®NWA* *Aftee two week* Haka zeena ta kwarzab'i kanta ,zuwan Anty fa iza yasa ta d'an ware,Anty fa iza tayi jimami sosai ,litttattfai jingim ta tawo Mata da su samun su yasa ta rage da muwa har ta fara Maida jikinta. Duk tama cire komi aranta ta fawwalawa Allah,'yan layinsu da gulma suke Shiga gidan domin jikin su ya basu zeena ba aure yanzu,gidan Abu mai kitso kuwa gulma ce ake yi gidan ne su ANEESA da Munay suka jiyo, suna San zuwa Amma saboda mum shiisa dalili ma da yanzu Sun Shiga school. Yau Anty fa iza ta bayar da sak'on zeena su kayan make up ne da dasu jewels da ta kala da yawa ta kawo don ta fara business taji dad'i sosai abubuwan Ke rage Mata kewa. Amma kullum dare da kewar haidar,take kwana take tashi *Gidan haidar* Tun da aka kai hajar haidar ko kallon ta bai tab'a yi ba har kar gabansa kawai yake Ita kam abin duniya yayi Mata yawa ,abinda take bukata ba dama gashi kullum cikin d'irkar magunguna take. Yana zaune yana danna laptop Wanda hoton zee Ke kai tafkeke ta baya ta tsaya tana jijjiga rufe wa tayi nan ya dago . "Ke ban hanaki tab'an kaya ba"?. "Eh ko tausayina baka ji ba kuma a gida na ka D'ora hoton wan nan yarinyar Ina gani ba,ace yau 2 weeks da aure Amma ko d'aki na baka tab'a Shiga ba to wallah na sare" Kallon mamaki yake Mata ya rasa ma mai ze ce kawai ya tashi ya shige d'aki nan ma binsa tayi ta kulle d'akin fad'awa tayi kansa ,shi kam yana tashi yakai Mata duka "inke zala mam miyace to se dai Ki hakura" . Da kuka ta fita ta d'au mayafi shashin Mami tayi ,da kuka taje ta zube kan kujera Mami tace Ke meye. "Yanzu Mami ya dace ace yau 2 week Amma ya haidar ko d'akina bai Shiga ba,nikam na gaji ,Mami tace karki damu bari yazo dole yayi abinda kikeso,yanzu je Ki mini kunun gyad'a". ya tsinee fuska tayi "Mami nifa ban iya ba" "Tom ba damuwa" ,haka tai kiran haidar awaya tace lalle kayi wa hajar abinda ta keso ko ranka ya sosu,kai ko kunya ba . Bai musa ba ya amsa hajar kuwa ko sallama bataiwa Mami ba ,ta fice yana zaune yana waya jin yana tambayar million yasa hajar ta washe baki ,key din sa ya d'auka ya fice. Wajen K'arfe 8 ya dawo hajar sai rawar jiki take leda ce guda 2 ya aje yace ta kaiwa Mami d'aya,kallon sa tayi" ban gane ba yanzu don ka kawon Abu sai an hada da Ita"? . "Eh mahaifiya tace dole". a yatsine ta d'auka a wulaknce ta kai Mata tana k'un-k'uni ,ajewa tai hajiya "tace hajar so nake gobe Ki mini dahuwar dambu pls" . "Gaskiya nifa hajiya baza a maidani jaka ba Haba Ina haule to" . "To mara Kunya in kina ganin ni uwarki ce to ,ai kya mun alkunya na matsayin sirikarki." "Nikam ban iya ba kisa haule tai miki". Fita tayi taje gida ta sillo wannka tazo ta tsaya kan haidar sai ka tashi muke. Kallon ta yayi da mamaki ,kuka ta saka kawai ya mik'e ya Shiga d'akin ta bishi har da sa key aranar ba yanda ya iya haka ya yi Mata abinda take so. Da safe sai haushi takeji kan jin yanda haidar Ke kiran sunan zeey ,ya gama komi zai fita tasha gaban sa yana mamakinn Ita ko gezau batai ba duk da kururwar data sha Amma har ta girgije tazo fad'a. "Ya haidar yanzu saboda Banda kima jiya muna raya sunna kana kiran sunan zeey to wallahi ban lamunta ba" Tsawa yayi Mata taja da baya yace Ke in Banda kida humanci Ke kika ce na biya miki ,to kanme zaki,zo kina b'atamun rai" Murgud'a baki tayi ya kama bakin ya murd'e ihu tasa yayi ficewar sa. Mayafi ta yafa tai gun momi tana haki" wallahi Mami kiyi wa ya haidar d'anki fad'a" a magagin baci hajiya ta tashi Ke meye. nan ta fadi karya da gaskiya,hakuri hajiya Ke bawa hajr. Matsawa baya tayi Haba hajiya ya dai kamata Ki nuna mai,kuren sa garam ta saki kofar ta fita Hajiya ta zauna yaraf kan kujera oh hajar rigima....ni



 nace baki ga ma komi ba tunda sirikar so ce. *Story &Writting* *Queen



* . [10:14pm, 01/11/2016] ?+234 814 783 0740?: . . . *ZEENATU by Queen



 page51-55* ?. ?. ? ? ? ? ?. ?. *®NWA* *Ina mai baku hakuri fanz d'Ina masu yimun waya da msg don son cigaban ZEENATU, godia nake agareku da k'auna,to hakan ya faru ne sakamakon abubuwa da suka shamin kai shiisa kuka Kwana 2 shiru Amma yanzu insha Allahu zamu d'ora inda muka tsaya* K'arar kid'a Ke tashi a d'aukacin harabar gidan har wajen gate Mami dake shararar bacci sakamakon kanta dake ciwo,figigit ta tashi tareda ya tsina akan Fuskar ta. Sakkowa k'asa tayi ta k'wala Kiran haule,da gudunta ta K'araso"Mami gani". "Ina kida Ke tashi ne? kamar a kaina akeyi". "Mami Anty hajar ce ta kunna" . "jeki ce ta kashe sekace gidan rawa". Hajar ce itada k'awar ta sumy Ke d'irkar rawa haule ta Shiga "Anty Mami tace a kashe kid'an". hajar "tace Ke dallah tashi anki a kashe." Sumy "tace Ke hajar ba uwar mijinki bace". "na sani ai Basai kin fad'a ba,ni ban San sa Ido" Mami na falo Ido duk yayi jajawur saboda jin bacci haule tace wai tace bazata kashe ba,cikin fushi Mami ta Maida hijab d'inta ta yi part din nasu Shiga tayi ganin su zaune suna ta loda alala suna korawa da lemu ga kid'a na tashi . Mami tace "yanzu fisabillahi hajar sai kace gidan rawa to bacci nake son yi". kit ta kashe hajar ta tura baki gaba "Haba Mami Gaskiy ba za a hanamu jin dad'in rayuwar mu ba, kunnawa ta tashi tayi. "To yar nema ai nasan dama bazaki kashe ba". "ni Debon alalan Ina ganin sa ya bani sha awa." "Mami na binta ne k'awaya yanzu zatazo Sai Dai Ki Hakuri" . fita tayi tana mai jin haushin hajar. *********** ZEENATU dake zaune ta tsala kwalliya zasu biki da yake ta gama idda tayi kyau sosai ,sadiq dake zaune ya kalli zee "Amma mum zee nikab zata sa ko"? Zee tace" akan me?wallahi Bazan sa ba" . sadiq" yace Ke bakya tsoron 'yan gulma suganki ,dama naji ana ta gulmar wai aurenki ya mutu,Allah akantin ya 'u naji". Mum "tace kanta farau ne? duk me gulma to bai San Kaddara ba ,oya ku tashi mu tafi." HAIDAR dake offici d'in sa ya kifa kai da gwiwa sosai yake son tuno mafarkin da yayi da zeena Amma kamar anyi ruwan sama an d'auke,Sam ya kasa tunowa. mansir abokin sa ya shigo, ya Dad'e akan haidar be sani ba sai daya daki bench d'in San nan ya d'ago tare da sakin wata ajiyar duniya mai k'arfi. Karb'ar laptop d'in mansir yayi ganin hoton zee akai yasa "ya ce haidar be a man mana kad'au K'addara rabuwanka da matarka Daga Allah ne. "Na sani mansir but soyayyar yarinyar kamar dad'a rura min Ita ake kullum kok'arin cire ta nake amma na kasa ,gashi har ta fita idda Ina tsoron kar wani ya d'auken Ita , kwanan nan I can't eat ,drink & sleep because of thinking her,pls frnd ya zanyi gashi nayi wa mahaifiyata biyayya na auri choice din ta Amma Sam bana jin dad'in zama da yarinyar duk da 'yar uwa tace". Kafad'ar sa mansir ya dafa kayi hak'uri komi yayi zafi maganin sa Allah ,kuma duk abinda zai Sami mutum komi dama a rubuce yake" "Hakane Nagode frnd" "Ok dama wasu files na kawo ka cike" . a kasalan ce ya karb'a tamkar majin bacci,wajen 5 haidar na bisa hanyar komawa gida ga wata azabbiyar yunwa daya keji. Shigar sa gidan tana zaune falon kaca-kaca gefe gashi sai cin biscuit da piko juice take, da d'aurin k'irji Sallama yayi ta kalleshi Aa ya haidar ,kallon ta yayi ya D'aga Mata hannu Sam atsarin sa baisan yaga mace da d'aurin kirji Amma Ita ya lura d'abi arta ce. shige wa d'akin sa yayi yayo wanka ya fito ya zauna dining ya Dad'e San nan ya kalleta "Ke Ina abinci na" . "Ban girka ba" tsaki yayi ya tashi ya fice side d'in Mami ya Shiga tana zaune suna hira da haule tace Aa haidar. "Mami inda abinci abani" "matarka batayi ba ne"?."mami batai ba ,dama yarinyar lazy ce ni kan Mami Ki Mata fad'a" Hannu ta D'aga "saurara bansan iyayi ". bum hajar ta shigo ta zarce kan kujera ta zauna ,haidar yace hajar jeki d'ebon abinci ". a wulaknce ta kalleshi ta basar Mami "tace yo ai babu sai dai ta girka wani". Kallon hajar tayi Ki girkawa mijinki ko taliya ce". Mami Bazan ba ,Haba an damen fa,kau taji Mari ,haidar dake tsaye yana huci. "Baki da kunya ko" ,Mami tace "to meya baka izinin dukan ta". kuka take sosai .Mami dake lallashin ta ta k'wace hannu Ki sakeni dama da biyu kikayi don d'anki ya daken, to wallahi bashi ya d'aika". "Haba hajar nifa tamkar mahaifyar Ki nake Amma kike mun irin haka". Tashi tayi " ni kawai Mami ban san sa Ido", k'ofar ta doko da k'arfi saida Mami ta toshe kunnuwan ta. Afusace ya haidar Ke yayinda ya d'au motar sa ,ya tafi restaurant don cin abinci yana mai tuna zee da tuni Ita Ke bashi da kanta ma. Zee dake zaune kusa da wata Mata wajen gun bikin da sukaje matar ta kalleta "yarinya Amma sark'ar ki tamun kyau ,Ina kika saya? zee tayi dariya "Nike sayar wa ai". matar "tace gaskiya Ina so nan sukayi exchange na number kan matar zatazo,ta saya. *Bayan sati d'aya* Hankalin zee akwance tana sana'ar ta tama manta da ta tab'a aure sai de soyayyr haidar na nan mak'ale aranta kullum tana adduar zabin Alheri. Samari kuwa Sun Mata caaa kullum ta fita sai ta samu masu sallama ,Amma Sam bata kulasu acewarta baza ta kuma aure ba ,adalilin hakan yasa masifar ta ta dawo ,kullum kaga Fuskar ta a had'e ko Ina zata don kar ace ma Ana sonta. Gefe d'aya gashi haidar kullum Kok'an barar sa yake kawo wa don zee.ta koma gashi duk ya rame,Sam baya jin dad'in zama da hajar ,Ita kanta mamin wahala take sha ahannun hajar . Kullum haidar sayyaje gun dad har dasu kuka yanzu tausayin haidar dad yakeji saboda ya riga yasan irin tsananin son da haidar kewa yar sa,Amma yace bazai wa zee dole ba sai in ta amince. Gashi kullum ya buga wayar ta bata d'auka ,inma ta d'auka d'in sai dai tace kaiwa mamin ka biyayya ka rabu dani. Ganin irin sintirin da haidar ke masa agun Aiki don har an sheda Shi agun yasa dad yayiwa Mum magana kan komar zee gidan haidar. Samun ta da zan cen da mum tayi yasa ta hau kuka ba zata koma ba saboda bata manta irin cin kashin da yan uwan sa sukai Mata,duk son da takewa haidar ta hak'ura. Gashi yanzu sana ar ta ta karb'u kudi ko ta Ina samu take ,Sam zee bata damu da kud'in samari ba tace DOGARO DA KAI (littafin Aysher chuchungaye)domin Ita yanzu dadin sana ar ta take. Sai 'yan gulmar anguwar su dake ta gulmace-gulmace musamman gidan Abu-mai kitso jin da tayi su munay Sun Mata maganar yasa taje taiwa Abu kashe mum ma bata san taje ba don inta Sami bazata bar ta ba,haka Abu ta sama Mata lafiya ,don ta San zee bata kyalewa. Ganiin maganar da mum taiwa zee na kome tace Ita kam bazata koma ba, dalilin hakan yasa aka fara maganar fara makarantar ta, bada b'ata lokaci ba dady ya samo Mata form na polytecnic inda munay da Aneesa keyi,duk sun wuceta da aji d'aya. Murna gun zee ba musaltuwa ....... Ku biyo Queen



 don jin yanda zata kaya. Akwai ba dakala a gaba ,karku bari a baku labari luv u ol my fan. *Story&Writting* *Queen



* . [4:42pm, 02/11/2016] Kaleesat basheer: . *ZEENATU by Queen



 page 56-58*  .  .          .   *®NWA* *Dedicated to MUNAY Lubie & bena* *11 Nov 2016* Zee na zaune tana game A wayar ta, k'arar msg ne ya shigo ta duba, _dole na ci gaba da binki,duk irin k'iyayyar da kike Nuna min your love always increase in my heart_ Murmushi tayi Tabbas tasan haidar ne ,batai reply ba, d'aga kai kawai tayi sama tace" haidar Ina sonka,bak'in ka nake ba,but mamin ka bata son zama na da kai ,am so sorry . sallamar su munay taji shigowar su ,yasa tai d'an yak'e bayan zaman su ,Aneesa ta dafa ta "qawas munzo mu baki hakuri ne" zee ta dago tace "me kukai mun". Munay tace "dalla can nasan Ki farin sani kawai de akan maganar da mukai miki ran nan ne ,kin San mu naki ne ko a gidan ma Abu sai da mukai fad'a da atine,baki fahimce mu bane". "Ni kun san Banda rik'o lokacin da akai Abu na tanka ya wuce aguna ni dama lokacin rai nane ab'ace". Aneesa tace" to yanzu de komi ya wuce ta kalle su da murmushi ai kunsan ku nawane ko munyi fad'a sai mun shirya" nan suka hau hira . K'irr wayar anee tai K'ara da smiling ta Daga "my one" tsam ta tashi ta fita waje. Zee "tace kin san me munay Allah banson ganin ma Ana soyayyawa se naji wani tukuki arai na, Naga an k'wareni da yawa ba gaira ba dalili an raba ni da ruhi na. Munay tace "se hak'urr fa,kawai Ki cire komi aranki Ki fuskanci future naki ba ko yaushe d'an Adam Ke dawwama a iri d'aya ba,Shi aure don baki dace da uwar miji ta gari ba gaba se kiga Allah ya baki me kirki, in kuma kuna tare da Ita Allah se kiga ya shiryeta, shiisa hak'uri yake babban jigo a rayuwar mu gaba d'aya" Zee "tace hakane Allah yayi mana me kyau". Yawwa "zee kin san me ni ya ma'aruf ma yaban sak'o na baki,had'e rai zee tayi "to me Ke tafe dashi". Dariya munay tayi "kin san de zancen gizo ay baya wuce na kok'i". Haka suka sha hirar su ganin mom ta dawo yasa suk tafi gida. *********** Tsaye hajar take sai jijjiga take tana watsawa mai gadi kira Afusace ta kalleshi "kai Haba baba mesa ba zakayi da jiki ba Ina sauri fa" Da gudu haule ta fito "Anty hajar Mami bata da lafiya da k'yar take nishi kiizo mu kaita asibiti" Tsaki tayi "Ke bar nan yanzu fa k'arfe 5 kinsan Bazan K'i zuwa biki ba saboda haka sai Ki San ya zakuyi". fuu ta shige motar da ko wata batai da koya ba kuma motar mamin ce ,fita tayi haule ta koma gidan aguje hajiya dake haki,tai Mata alamar data d'akko Mata maganin ta. Rashin Sanin gun yasa haule sai diri-diri take Ana haka sai ga haidar ya shigo ganin halin da take ya kwasheta zuwa hospital nan da nan akai treatment d'inta sai wajen dare San nan suka koma. Sai a lokacin haidar ya Kula hajar bata nan, shide ya San bai bata izini ba Amma tasa k'afa ta fice. Tambayar haule yayi ta gayamai cike da fushi yayi part din su ,wajen 8:30 sai ga hajar ta danno hancin motar ta,haka ta fito rik'e da jaka tayi part d'in su. k'as -k'as kake ji tana taunar chewgum,shigowar ta falon ta saki wani k'wan chewgum ji Jake fos- fos. "Aa ya haidar ashe kana zaune". "Ke waya baki izinin fita"? "Ni na bawa kaina ta wani ya tsina fuska" . "Anya kwa hajara kinsan meye aure kuwa hajar"? Kwai ta kuma saki toss! Kake ji Ta galla mai harara "ban sani ba". Mari kakeji ta ko Ina " ya nuna ta da yatsa "ba ai yarinyar da Ina magana tana min k'wan chewgum ba kin gane ,wallahi hajar Ina raga miki ne donke yar uwa tace don kuma mami". Ba wuyar ta fara kuka . "eh wane dare ne jemage bai gani ba ,ai se daran mutuwar sa idan kana ganin ban san aure ba,kace tsohuwar ka ta koyan" da gudu ta shige d'aki ta kulle zama yayi kan kujera ya dafe kai ,Wanda yaji yana sarawa tamkar zai tsage. *Washegari* Haidar ne gaban maman hajar wajen k'arfe goma sha biyu na rana ,duk ya ratta ba Mata abubuwan da hajar keyi. Cikin b'acin rai tace" yanzu Ita hajar d'in Ke wan nan ta 'asar to karka damu haidar ,tunda ta raina Ita mamin ni zanzo da kaina na sab'ar Mata,kayi hakur Anjima Ina nan tafe" Kud'i ya aje Mata ya tashi ya tafi. *After 3 hours* Hajar ce kwance kan carpet mama na kan gado tace "yanzu hajar abinda kike kin kyau ta kenan"?. "Kin san de yanda akai auren nan ba so yake ba Mami Ita ta shige gaba sai da ya aureki, Amma Ita kike watsawa kasa a Ido ,to wallahi ahir ban yar da ba 'yar uwatace don haka Ki mutunta ta wallahi duk randa kikai abinda haidar ya koreki to bazaki samu kamar Saba atom". Hajar tace "Haba mama Ita Mami kome ake idon ta akai,Nikam bana son hakan". " lalle se yanzu zakice haka? da ba dake akewa wata ba, ko Ita ba mutum bace ,wallahi nayi Dana sanin shige miki gaba kan auren nan ,ban san kin canja hali haka ba, koda yake Naga ai kin canja k'awaye ,Allah ya shiryeki nade gaya miki karna k'arajin wani Abu sab'anin haka ,Afusace ta d'au jakar ta ta fice. Hajar tayi kwafa tana had'e rai,tare da jin haushi. Wajen k'arfe takwas na dare hajar ta Shiga side d'in Mami , Mami Ido yayi zuru-zuru bako ya jiki ta zauna ta hau danna phone. Mami tace" yanzu hajar Banda lafiya tun Jiya ko kizo Ki dubani"?. Haushin Mami ta keji kawai tace "ai gashi Nazo yanzu kin ganni ai Naga ma kin warke". "Hajar kin canja hali". "nifa Mami an takuran haka d'azu ma mama tazo tana min fad'a". tsaye ta tashi tana gyara d'an kwailin kanta ,ta turo Shi gaba,"haka kawai ank'I a bari mutum ya sake shida mijin sa" haule dake kitchen tana Aiki ta jinjina kai Mami tace" to dan uwaki d'an banawa bane? aini na haifi abuna". Hajar tai hanyar waje tana k'unk'uni. *Story & Writting* *Queen



* . [2:13pm, 03/11/2016] Kaleesat basheer: . . *ZEENATU by Queen



 page59-60*  .  .    .  .  .  . *®NWA* *dedicated to Lubie bena & munay* *3 Nov 2016* *After 1 month* Yau satin zeena 2 da fara d'aukan lecture a polytechnic, zuciyar ta fari k'al takeji cike da kwanciyar hankali take karatunta da yake tana son abun abinda ya kaita school din Shi take yi ,baruwan ta da shirme ,department din su d'aya da Aneesa da munay. Tafiya take ahankali ganin had'ari ya had'o student sai rububin samun mota suke ,gefe kawai taja ta tsaya da alama Ana wuyar mota ,parking yayi ya fito ,cike da girmamawa ta gaida Shi,kallonta yake Ido cikin Ido yace "kanwata, ya ban ganki da k'awayen naki ba"?. "Ai ba class namu d'aya ba" "ok zo muje na rage miki hanya" murmushi tayi "ya ma'aruf ai yanzu ma zan samu mota". "Ke ban San shirme shigo kawai", ba musu ta Shiga gaban mota yaja hamdala tayi ganin ruwa ya fara sauka . Jiyowa yayi ya kalleta "hala de Kinga sak'o gurin k'awarki ko", murmushi tayi "nagani". "Amma ai ba amsa ko" . Shiru tayi ba tace k'ala ba har sukaje unguwar ya sauke ta da alk'awarin zai shigo da magrib. Jikinta a sanyaye ta Shiga gida ,tana ganin girman ya ma'aruf Sam bazata iya cewa ya k'yaleta ba. Bayan taci abinci wajen 4:30 suna hira da mum zeey ta kalleta "mum ,yayan munay ma'aruf wai zai zo Anjima" . Washe baki mum tayi "Haba dai wanne Daga ciki? badai Wanda yayi aure shekara uku da suka wuce ba"?. "Mum shine" . "Masha Allah zee Allah ya sanya Alheri,wani hanin ga Allah baiwa ne". turo baki zeey tayi gaba "kai mum nifa Bance Ina so ba". Had'e rai mum tayi to in banda abinki kullum samari zuwa suke kina korar su, in ma tsoro kike ji ai kin San ma'aruf da gidan su tunda yayan kawar Ki ne,kuma ya kamata Ki fidda haidar Daga aranki" . Bata ce komi ba sai Jikinta da yayi la' asar alal hak'ik'a haidar shine ta keso Amma ba yanda ta iya tunda mamin sa ta haramta zaman su,share hawaye tayi ta d'akko wani k'aramun hoton sa ta kafa Ido yayi mutuk'ar kyau yana tsaye jikin motar sa. k'irjin ta tasa hoton tana kukan zuci... Wajen k'arfe 8 na dare ma'aruf yazo da k'yar ta fita suka gaisa yana jingine jikin motar sa ,ya kafa hula ,alal hakika ta San haidar bazai nunawa ma'aruf komi ba , sai de da alama zai girmewa haidar ,amma kowa da irin structure nasa, sai kuma akace soyayya gamon jini,magana yayi ta d'ago manyan idanuwan ta tai mirmushi yayin da wushiryar ta ta fito . "Am Zeenatu duk wani Abu da zance kin Riga kin sani ,kin san dai inada aure da yara biyu ,nayi jimamin mutuwar aurenki duk da kina yarinya k'arama,Amma da na tsaya nayi tunani sai Naga komai muk'addari ne Daga Allah ,duk da Abaya kan Ki aure na d'anji Ina sonki to ganin zaki aure yasa na hak'ura"..... "Amma yanzu tunda ga abinda Allah ya tsara ,to na kawo k'ok'an bara ta Allah yasa na samu karb'uwa". Bugawar k'irjin ta ne ya tsanan ta ,ta d'ago Fuskar ta, ta kalle shi "to Allah yasa hakan Shi yafi alkhairi". "Masha Allah zeenatu insha Allahu zaki Alfahari dani",nan sukai ta dai hira, Wanda rabi hankalin ta baya wajen. ************* Mami dake tsaye kan hajar sai murk'u susu take da alama cikin ta ne Ke ciwo ga aman da take kwararawa. Mami ta d'ago wayar haidar nan ta gayamai. Ba ai mintuna ba yazo , direct hospital sukaje aka tabbatar da Shigar cikin hajar ,murna gun Mami ba kama hannun yaro haka shima haidar duk Da ba sonta yake ba Amma yaji dad'i. Harara kawai hajar Ke doka musu bayan Sun koma gida tasha magani tayi bacci . Wayar ta ce tayi K'ara ta D'aga ganin sunan sumy yasa ta washe baki . "Hajar Ina ta kira shiru" . "Ke ni Banda lafiya ga haushi ya ishen wai ciki gareni, nida ko gama Amarcin banyi ba ,ai da sake ,Mami sai wani dare baki take . Sumy tace "to Ke meye" . "Ke nifa ban so sumy tayi dariya ."Amma ni da zaki bi ta tawa da kin hak'ura, Kinga kin samu dama sai yanda kika soyi ,tunda Mami naso". nan dai ta shawo kanta ta hak'ura,haka suka gama surutan su suka kashe ********* Samun cikin hajar yasa ta tsiri iskanci kala-kala haka zata je ta tsaya kan Mami tace ga abinda take so dole kuma tayi Yau ma data zauna kan kujera a d'akin mami ,tace ba abinda takeso inba alala ba haka Mami ba yanda ta iya ta tashi ta keyi. Gamawar ta keda wiya! Ana kawo Shi hajar ta fara amai ,bayan ta wanko baki tazo ta zauna "Mami banacin alalan nan fa". Agajiye tace" hajar ban san tsirfa fa ,Ke kullum baki da Aiki se kwad'ayi ,wallahi dan dai kina da ciki ne yasa,kikaga Ina miki abubuwa" Had'e rai tayi ta tashi ta fita part d'inta *After 1 hour* Rake take sha duk wajen ya b'aci ga su bawon mangwaro ko Ina datti Daga Ita sai d'aurin kirji Mami ta Shiga da kwano "gashi wainar fulawa ce" Kallon wajen tayi "yanzu hajar d'an shigowar da kikai shine ki kai kaca-kaca da guri"? Hajar tace" Mami to meye? ai Naga gida nane " Mami yanzu fitsarar hajar har tsoro take bata,Jan numfashi tayi. "Sam hajar ban san inda kika koyo fitsara ba, Ina magana Amma ni kike gaya wa haka k? Ko ba komai aini mahaifiyar mijinki ce kuma yayar mahaifiyar Ki,na haifi d'an ai dake baki farin ciki,dole Ki mini abinda kikaga dama" Hajar ta had'e rai to "Mami ai seki maidashi cikin Ki,tunda kishi kike dani". tsaki taja tayi kitchen. kuka Mami ta fara tana tasa hannu. Dai-dai lokacin haidar ya shigo ganin Mami na kuka hajar na jijjiga yasa ya wanke ta da Mari. Ihu ta saka duk ta cika gidan Mami tace "kai haidar wa ya gayama Ana dukan mai ciki"? "Haba Mami idan Ita bata San k'imarki ba, ai ni na sani kawai dama wasu Matan na fakewa da ciki suna rashin mutunci,to wallahi Ki gane bana had'a mahaifiyata da kowa". Afusace yayi cikin d'aki, Mami ma ta fita side d'inta tana mai dana sanin had'a auren nan ,sai yanzu take tuna alherin zee. Ganin hakan yasa hajar ta kuma kurma ihu taje sai buga k'ofar d'akin haidar take,gajiya tayi taje tayi wanka ta d'au jaka ta fice . Jin shiru yasa haidar fitowa daga d'akin ,ganin yanda kallon dakin yake kamar na mahaukata,ba yanda zai yi ya hau share gurin ya karkad'e yayi cleaning ,zama yayi yana tunanin inda hajar ta tafi. Wanka yayi yasa jeans da tshart yayi fiyau dashi ya K'ara haske, Amma kana ganin sa kasan yana da damuwa,tunani yake yana yaron sa dashi matsala ta sha mai kai, direct gidan su kb ya tafi........ *Story & Writting* *Queen



* [8:59pm, 05/11/2016] Kaleesat basheer: *ZEEENATU by Queen



 page61-62*  .  .    .  .    .  . *®NWA* Yawan nacin ma'aruf da salon nasa soyayyar yasa zee ta aminta da shi,Amma ko rabin - rabin son da takewa haidar batai mai. Yau ma kamar kullum yazo, tana zaune a barandar k'ofar gidan su da make-ken hijab, da alama Sanyi-sanyi takeji ganin yanayin garin am fara sanyi, hira suke suna murmushi,leda ya mik'a Mata ta d'ago ta kalleshi "Aa kabar Shi". had'e rai yayi "tunda na fara neman aurenki ba Ki tab'a Karb'ar abin hannu naba Haba my wife" Dariya tayi ta karb'a sukayi sallama ta shige gida wani murmushi ya saki tare da shafo gemunsa ya fad'a mota yaja. Mum dake zaune tans irga kud'in sana' ar ta ,ta kalli zee dake d'aga wani swiss less tace" zeey yaushe zaki kaiwa goggo ta birji Hutu"?. Dariya zeey tasa "kai mum so kike tsalha ya dawo" mum tace "ai lokuta da dama Ina tuna wawtar sa wallahi" haka sukai ta hira nan ta mik'a kayan da ma'ruf ya bata mum tace "wan nan da gaske yake". Zeey tace 'nifa mum wallahi bana son ma K'ara aure" mum tace "aure kwa ya zame miki wajibi idan mun ajeki kallonki zamu na tayi? ,ai aure da kike gani shine jindad'i farin ciki da mutuncin 'ya mace". Zee ta ce "Amma mum nikam ki gafaa abinda su mamin haidar sukai mini aidole naji tsoro". "Ke ba dukka aka taru aka zama d'aya ba ,Shi kowanne d'an Adam da tasa jarabawar Allah de ya zab'i na gari". *GIDAN HAIDAR* hajar ba ita ta dawo ba sai k'arfe 9na dare ta shigo Allah ya sota haidar bai dawo ba ,haka ta shige kitchen ta d'ora indomie guda uku taci tayi nak ta kwanta akan kujera tasa wak'a tana bi. *9:30* Haidar ya shigo yana waya bai Kula da ita ba sai jin kid'a da yayi ,ya juya ya ganta had'e rai yayi "yace hajara Daga Ina kike ? Wama ya baki izinin fita"? Wani banzan kallo tayi mai, "malam ni na bawa kaina, ko ka manta ne?kai ko kunya Baka jiba ,za kazo kana neman inda nake ka damu dani ne? To ka saurara min " Kamota yayi ya matse Mata baki K'ara ta saka ,ni ka sake ni, gam ya rik'e bakin. "Ki sani, ko baki aureni ba ni me iya hukunta Ki ne ,karki d'auka wai na damu da Ke ne ,NO kawai d'an cikin Ki nake tausayawa saboda nasan baki da sense ba kisan ciwo kanki ba ,kuma duk randa kika kuma fita wallahi se kin gane bakida wayo". saikin ta yayi ya shige d'aki. K'ara ta saki ta wangame baki "eh naji kome zaka ce wallahi duk randa nayi niya Sena fita, kuma wallahi ka sa tsiya kaida tsohuwarka duk sena b'arar da cikin inga ta tsiya". jin alamar zai fito yasa ta fad'a d'aki ta banko. ***************** *BAYAN WATA D'AYA* *Ranar Monday da safe* *8:00* hajar ce ta fito sak'ale da jaka sai had'e rai take ,ga cikin ta ya d'an fito ,neman haidar take bata gansa ba ,domin yau zata fara zuwa awo. K'arar bud'e k'ofa taji haidar ne ya fito shida Mami ya rik'ota zuwa yayi ya bud'e gaban mota zai saka ta ,da gudu hajar tazo ta tsaya ,"waje na ne ka kaita baya" . Matsar da ita yayi ta dak'ire ta D'aga murya "wallahi Bazan matsa ba" "Ke wai mesa baki da nutsuwa ne? Haba mahaifyar tawa". Turo baki tayi "haka kawai don anga mutum zai,fita sai Mata ta langwab'e tace ba lafiya, ai sai kabari sai ka kaini, San nan ka kaita daga baya". Mari zai kai Mata, Mami tace ya bari zata koma ganin hakan yasa yace sai dai hajar taje ta hau adaidaita shikam inde be kai Mami ba Itama kwa ba zai kai ta ba. Gidan baya Mami ta Shiga tace hajar ta Shiga gaba ,bayan da ya iya haka ya jasu yakai su hospital din. Tana gaba tana harar Mami, zuwan su asibitin yasa suka fito, afusace hajar ta fito, tayi gaba har da takewa Mami k'afa. jinjina kai Mami tayi suka bita abaya. Da daddare Mami na kwance kan 3seater sai kuka take ganin irin cin kashin da hajar tayi Mata. haidar ne ya shigo ganin tana kuka yace "Mami badai ciwon ne ya tashi ba"? Share hawaye tayi "haidar da shine ai da da sauk'i akan cin kashin da hajar ta keyii min" Numfashi taja "Wai Daga nace ta taimakan har rok'anta da Allah nayi ganin bana jin dad'I ta daman kunun gyad'a, haka ta ce baza tai ba, taimun rashin kunya ,har da cewa wai na sa mata Ido ,wai ita ba baiwa bace". Bata bar ni haka ba , har sai data Bangaje ni, ta fita. Fushi mai tsanani haidar yayi ya tashi a fusace nan Mami ta daka tar dashi zama yayi tace "haidar ayau Ina Dana sanin rabaka da salihar matar ka zeey ba abinda tai mun na k'warzabeta gashi ita kuma kullum kyautata mun take bata gajiya,bana mantawa akwai ranar da tayo mun kunun gyad'a, ni bama ni nace tayo mini ba ,ganin Ina sha awar sa yasa tayo mini. haka na watsa Mata Shi ajiki ,Tabbas na San alhakin ta ne ,dama Allah baya barin hak'k'in wani,gashi Ina ganin hajar yar uwar ka, aganina kamar ita ta dace dakai ,ashe ba haka abin yake ba,kuma nasan baka jin dad'in zama da ita". Kuka ta cigaba da yi haidar na bata hak'uri " Dole naje har gidan su zeenatu nayo bikon ta, tare da ban hak'uri.... Sorry fans *Story Writting & editing* *By* *Queen



* . [9:38pm, 05/11/2016] Kaleesat basheer: . *ZEENATU by Queen



page 63-64*  .  .      .    .   *®NWA* mik'e wa yayi ya kamo hannun Mami "Allah Mami". Juyi yayi "iluv u so much Mami" ,dariya tayi son na cusguna muku kaida zee abaya , nasa ka k'untata haidar ka yafen". hannunta ya kama "Mami kin cancanci komi ,ni komi kikaimin Banda kamar Ki duk duniya naji dad'i da kika so zee,kidena ban hak'uri, har,abada Bazan tab'a biyanki abinda kikai mun ba tun Ina yaro, zan cigaba da miki biyayya inde abun bai sab'awa Sharia ba koda kuwa bana so" "Hawaye ta share Allah yayi maka Albarka haidar" Amin yace. Gyada zama yayi "Mami Inaga husy kawai ta dawo nan jigawa cuz bana son rashin ta a Kusa da Ke ,sai ai Mata Transfer uni ta nan" Mami tace "Aa k'yaleta Naga tafi san can d'in kawai saidai ta koma zuwa duk week end, tunda ba wani nisa muke ba kano da jigawa". "Ok Mami yanda kike so haka za ai". Burum hajar ta shigo rik'e da ciki haidar ya buga Mata harara,nan ta ce cikinta na ciwo ya bata kud'i zata asibiti . Banza yayi da ita saida Mami ta sa baki.gyara tsayuwa tayi dama nan kayo Ina ta nemanka,ko kallo bata ishe shiba. ya d'akko dubu biyar ya mik'a Mata arene, amsa tayi. "Yanzu dubu biyar za tai min kuwa"? . Ko kallonta baiba saima haushinta daya keji ganin irin abinda taiwa Mami ,gashi Mami ta hanashi d'aukan mataki,karamin tsaki yayi ya fita.. Tuwon samobita ta gani agefe yaji manshanu nan ta d'auke ta fara ci mum tace "to fitsararriya Nawa ne" . "Mami sede Ki hak'uri don d'an da kuka k'wallafawa rai yana buk'ata ". fita tayi Mami ta tafa hannu "oh ni na janyowa D'ana jangwam ,dama ciwon k'arya ne,gashi ko kunya ta bata ji".nan ta jinjina kai ta tashi jin k'afar ta tayi nauyi tayi bedroom. *Zeenatu* Tafiya take a Kusa da department d'in su munay da Aneesa , jiran su take ga rana Ana dokawa ,zee tace wallahi yunwa nakeji,yau lecture ta kwad'a ni gashi sunk'I fitowa da wuri,nan Aneesa ta tawo, zee "tace Ina munay"?. Aneesa tace" tana zuwa yanzu, ke nifa school d'in nan tafara fita araina kullum malamai sita kwad'a mutane". Zee tace "to ya za ai dama haka karatun yake" munay ce ta tawo tace "ku sorryn ku handout d'ina na karb'o gun lollipop kinsan ta yanzu sai ta b'atar. Dariya suka sa suna Tafiya suna hira dai-dai lokacin wayar Aneesa tai K'ara ta d'aga, "oke nawan gamu nan" . Munay tace "hala dai hubby dinne"? Aneesa tace ya San ranki shine mana". Bakin titi suka tsaya Zuu mota ta tsaya fitowa kb yayi ya matso Aa my Aneee nan ya bud'e Mata gaban mota, kallon su zee tayi ta ce "ku shigo". D'ago kai zee tai suka had'o Ido da zee kb yace "OMG! zeenatu ,kanmu bisa wuyanmu ,Kullum muna bada hak'uri". murmushi tayi "ai niba komi nasan komi muk'addari ne". Anee tace" kin San Shi ne"? kb yayi carab "yace Haba matar haidar ce da muka rasa". "Abokin haidar ne kai ashe"?. "eh mana amini kuwa tun muna yara" Haka dai sukai hira har suka ya kaisu . ******** Ihu zeey tasa mum daga d'aki tace"ke meye "? "Mami wallahi duk jewels da makeup set d'in nan duk an saye am very happy" mum tace "ai haka ake so zee,. Yawwa d'azu iyayen ma'ruf suka zo kina school". Gaban ta ne ya fad'i tace" Mami me sukazo yi" tace "gidanku suka zo yi" . Shiru tayi bata ce komi ba mum tace "to sunzo kan maganar kune keda ma'ruf kuma an dai-dai ta har sun aje kud'in zance duk da Ke bazawara ce Amma ma'aruf ya dage sai ankawo ,Kinga ikon Allah ko zee? ai wani hanin ga Allah baiwa ne". Zee da idon ta ya ciko da hawaye tace "Mami ayni ban sani ba"?. Mum tace "ke karki maidamu k'ana nan mutane mana? ,bafa mi miki dole ba tsaf dai sai da babanku ya tambayeki shekaran jiya ki kace kin amince, kina son ma 'aruf". Zee tace "Mami bafa haka nake nufi ba" . Mum tace" ah to". D'akin su ta shige, ta latso wayar munay ,tana d'auka tace "dalla malama ashe ke kin San yau za ai maganar mu, shine kikai shiru ko?duk kuka binne ni ba Wanda ya gayan ko yayan naki" Munay tace" nima ban fa sani ba". zee tace "to d'azu dai ankawo kud'I ,kinji sai kace wata budurwa". ihu da murna munay tayi tace "to dalla meye marabarki da budurwar. wata budurwar ma tafi ki shekaru da girma ,nan tace "bari na fesawa Anee". zee tace ni zaki kashen dodon kunne, duk in cikan kunne".Dariya tayi suka kashe a tare. haka dai suka gama hirar su suka kashe. *Story Writting & editing* *By* *Queen



* [5:56pm, 07/11/2016] Kaleesat basheer: . . . . *ZEENATUby Queen



 page 65-66* . . .  .      .  .  . . *®NWA* . *Queen



* . Zuu motar mami ta tsaya a k'ofar gidan su zee, suka fito itada husy driver ma ya fito ya kashe motar, a d'arare sukai sallama a gidan husy ce agaba, zee na zaune a tsakar gida tana surfa wake d'ago kai tayi ta amsa sallamar ,ganin su ne yasa ta shige d'aki a guje can mum tafi to tana musu marhabun ,iso Tayi musu suka Shiga d'akin suka zauna ,ruwa ta kawo musu suka sha, zama tai suka gaisa mami ta kalleta "nasan zaki mamakin zuwana sai dai wan nan ba komai bane ga ikon Allah ayau gani a gabanku Ina neman afuwa akan duk abinda yafaru Wanda na jagoranta da hannu na wallahi ni kaina nida haidar kwata-kwata auren da nasa yayi bama jin dad'in sa kuyafemin". Mum tayi murmushi "Allahu Alkabar naji dad'in hakan Allah ya yafemu gaba d'aya" mami ma tayi murmushi tace "Ina zeena d'in? kira mana ita" mum ta k'wala Mata kira ,can sai gata ta fito suka gaisa mami ta fara rok'anta gafaara harda hawayen ta zeey tace "mami babu komi na yafe" kamo ta tayi ta rungume "nayiwa D'ana rashinki zeena Tabbas nasan da hak'k'in ki" tashi zeey tayi ta shige d'aki jin yanda kuka Ke neman zubo Mata. . . ******* mami ta share hawaye San nan ta kuma kallom mum tace "muna rok'o iri ayi hak'uri zeey ta koma d'akin ta ba donni ba" mami tayi murmushi "Eyya ai ita an kusa saka ranar auren ta da wani sai dai mu baku hak'uri Allah ya bashi ta gari" ,kamar mami tayi ihu don takaici nan tace "Allah ya sanya Alheri tashi sukayi suka tafi. Bayan tafiyar su zee ta fito ta zauna, "mum jibi wani ikon Allah! "to rawar jikin me kike ne"? "Aa mum kawai dai na fad'a ne" ,mum ta tab'e baki nikoda bakida miji ba zaki koma gidan nan ba don naji ciwo kan abubuwan da sakai miki" wani siririn hawaye ne ya zubowa zeey dna tuno haidar da tayi, dai -dai lokacin Sadiq ya shigo futu-futu dashi tsayuwa yayi ya kalli zeey san nan ya kalli mum yace "wai mum mayya Sami Zee ne"? nan mum ta tab'e baki "wai don babar haidar tazo ban hak'uri da kome shine fa take kuka". . . ****** Dariya sadiq yayi "ai mum da nine saina musu korar kar",mum ta Harare Shi "da yake agarin gab'a- gab'a muke ko" sadiq yace "Ai mum da haushi ,wai Ina su sadeey ne Naga yau weekend" mum tace kana yawon gal-gal d'in ne zaka gansu, ai idan ka shud'a ba aganin ka sai yunwa ta ciyo ka ,wan nan ball bana sonta wallah" zeey ta kwashe da Dariya "mum gaya mai de jibi k'afafuwan sa duk an dokosu gun ball, kai ko irin wankan samari bakayi koda yake kai ba wani isasshen saurayi bane" sadiq yace "to Ina ruwanki kibari yamma tayi kiga yanda zan fece kede kiji da abinda ya dameki kawai" mum tace "oya sadiq yi waje ban san fad'a,Dariya yayi ya fita tsakar gida ya ware murya yace "ni sai haidar idan ba shiba sai rijiya" zee ta had'e rai "mum Kinga yana tsokana ta ko" mum tace "Ke ni rabani da shirmenku" fita tayi tabishi aguje Dariya yake Mata tare da gwalo, zee tace "Allah yau sadiq zaka gani a kwanon ka..... . . *Story Writting & editing* . *Queen



* . [7:21pm, 07/11/2016] Kaleesat basheer: . . . *ZEENATU by Queen



 page 67-68* . .  .  .      .    .   . . *®NWA* . *Queen



* . . Jugum-jugum sukayi kamar gidan mutuwa mami ta kalli husy "wallahi abin nan na damuna musamman jin yayinyar nan zatai aure",husy tace "mami kawai abar maganar koda ya haidar ya dawo kar a sanar mai a k'yale Shi kawai", suna cikin magana hajar ta shigo tana waya tasa wata d'agaggiyar Riga duk cikin ta daya fara girma awaje ,husy tace "Haba hajar kefa yanzu ba yarinya bace ya zakina fitowa haka" harara ta kai Mata "to yar gulma meye ruwanki dani banza kawai dama Ina ciki dake Kinyi gulma anki saimin mota",husy tace "tafi can Ke kin isaa wallahi tunda kike wa mami rashin kunya munsa k'afar wando d'aya dake",hajar tace "tabaya ta rago dai ni matar yayanki ce ba yanda zakuyi dani" husy zata K'ara magana mami ta tsaida ita "k'yaleta ban san tashin hankula" k'wafa husy tayi "mami wallahi idan hajar bata mutun taki wallahi wataran sena zubar mata da hak'ora",hajar ta tafa hannu tayi shewa "wallahi kuwa da Kinga yanda ake iya tsiya nan gani nan bari sadakin 'yar mayya" juyawa tayi ta fita ta doko musu k'ofa... . . ******** bayan fitar ta kawarta tazo da rawar jiki take suka zauna hira da sabuwar k'awarta sun had'u ne agun saloon tundaga nan suka d'inke lemo kubra ta kurb'a tace "Gaskiy new frnd Kina shanawa gidanki yayi min kyau" hajar tace "bafa ni kad'ai bace ba, har da uwarmiji wani tsalle kubra tayi "Ke Haba tab Kice baki da 'yanci kin ganni nan lokacin da nai aure acan muka tare Amma wallahi saida na takura ya canjamun gida" ,hajar tace "taf ni meye banyi ba dayake ma auren gida ne dadin abin ma basa Shiga harkata matsalata kawai baya sakar mini", Hmm! kubra taja numfashi lalle da sauranki hajar to inde kina san mafita kizo gurina zan sama miki wallahi tab" hajar tayi Dariya tare da zama kusa da kubra "Allah k'awas Amma naji dad'in had'uwa dake" nan dai sukai ta hirar su ,haidar ne yayi sallama ya shigo falon harara hajar ta wurga mai sai kubra ce amsa sallamar tab'ota kubra tayi "lalle dole mijinki yaja aji handsome" haka dai kubra ta k'araci sumbatun ta, data tashi Tafiya hajar tai Mata alk'awarin zata je.. . . ********** kuka take ta sharb'a d'ankwali a hannu fiskar nan duk tai face-face duk ta b'ata kwalliyar da tai numfashi taja "me yasa zakai mini haka? ka rasa abinda zakai min sai kishiya bayan kasan ni kad'ai ce taka, me na rage ka dashi? don tsabar cin amana" kallonta yayi ya sunkwi dakai ya kurb'i tea "Haba maryam kanki farau ne? ni nace ba don kin mini komi zan K'ara aure ba kawai don sunnce", "to ni ban isheka ba, haka kawai ina zaman zamana kazo kace zakai mun kishiya to wallahi sai dai koni ko ita don wallahi Bazan zauna da kishiya ba" "maryam Ina lallab'aki kina kutsewa karfa ki manta ni mijin mace hud'u ne, badon wai bana sonki bane", d'aukan waleed tayi suka Shiga d'aki tana kuka dafe kunci ma'aruf yayi nayi niya kuma sai nayi na samu yarinya sakin wawa zan yi sake tab haka ya tashi ya fice .... . *Story writing & editing* *Queen



* . . . *ZEENATUby Queen



 page69-70* . . .  .    .  .    .  . . *®NWA* . *Queen



* . . *Bayan kwana 2* . haidar na office wayar sa tayi k'ara d'agawa yayi "Aa kb yade"? daga can kb yace "pls idan ka taso daga office ka biyo ta gidan mu akwai labari", haidar yace "ok ba damuwa zan biyo" bayan kamar 1 hour haidar ya parking motar sa k'ofar gidan su kb 5:30 dai-dai d'akin ya Shiga kb yace "mijin hajara ya kwana 2" tsaki haidar yayi "kana son b'atamin rai, pls tell me kawai" kb ya matse gemu "zee aure zatai" da sauri haidar ya tashi ya kalle Shi "da gaske!? Pls in wasa kake ka daina",kb yayi tsaki "to sai akace don kai kad'ai aka halicce ta,tsaya ma kaji ma'aruf zata aura fa", "wane ma'aruf kake nufi ne"? kb yace "ma'aruf dai yayan muzzam abokin mu haidar ya daki bench d'in dake kusa dashi "oh my god! kai- kai da sake Bazan bari wani ya auri beauty ba" ,kb yace "tun yaushe kuma Ina gaya maka ansa rana kasan Aneesa budurwata to k'awar zeey ce ita Ke gayan" dafe kai yayi "kb meye shawara",kb yace "kawai ka hak'ura ka rik'e hajar d'inka", haushi ne ya kama haidar kawai ya shuri wayoyinsa ya fad'a mota ko sallama baiwa kb ba. . . aguje haidar ya aje motar sa ,part d'in mami kawai yayi suna zaune suna hira ita da husy,zama yayi kan kujera ya kalli mami yace "mami dama kince zaki gidan su zeey" mami tace "munje ai Amma aure ma zatayi damm! Yaji k'irjinsa ya bada "mami don Allah duk yanda za ki karki bari zee ta auri wani batare da ta dawo mini", idanuwan sa ne sukai jajawur mami tace "sai hak'uri" ganin yanda ya birkice lokaci d'aya yasa mami tace "Amma zan dad'a gwada sa 'ata Allah yasa adace" husy tace Amin, jiki a sanyaye ya tashi ya fice side d'insa muk'ulli ya gani a jikin k'ofa alamar hajar bata nan, dafe kai yayi ya zauna gun yana Maida numfashi,ganin zai b'atawa kansa lokaci yasa ya tashi ya koma part din mami ya bud'e tsohon d'akinsa ya baje kan gado tunano ranar daya fara ganin zee yayi da irin rayuwar da sukai har suka rabu,bai San sanda bacci ya kwasheshi ba. . . ******* _your love is always growing up in my heart zeenatu pls ki dawo Guna karki auri wani plss_ msg d'in daya shigo a wayar zeey kenan suna lecture karantawa tayi ta Maida wayar jaka Sam ganin msg d'in yasa ta daina ma gane karatun, tashi tayi kawai ta fita ,bakin bishiya taje ta zauna ta fad'a duniyar tunani ,wayar ta d'akko ta k'ara karanta msg d'in ,nan ta Maida mai reply kamar haka: _haidar rayuwa bata zuwar wa mutum yanda yake so ka d'au komai a matsayin k'addara kayi hak'uri haidar Ina sonka har abada ,Amma komawa gidanka bazai yiwu ba sabod Na kusa auren wanin ka Bissalam_gaba d'aya tama kashe wayar ta maida jaka ta cigaba da zama wajen. . Haidar kuwa ganin msg ya shigo da hanzari ya duba yana d'aki ko Aiki baije ba saranda yayi ganin abinda tace kawai ya aje wayar a gefe, ya tashi ya fita falo hajar na zaune tanacin gyad'a tana ganin sa tace "Yawwa ya haidar dama kud'i nakeso" ko kallonta bai ba, ya koma d'aki binsa tayi ta jawo shi ta baya ya Juyo tace "dubu ashirin nake buk'ata" mamakin rashin nutsuwar hajar yake yace "Ke ban dasu ko angaya miki hak'osu ake" "wallahi sai ka bani" bincike rigar sa da ya cire wadda ta gani a sakale tayi dubu goma ta gano ajiki ta d'auke tace "na d'auka" ta fice kasa magana yayi shi kawai tunanin zee ya Cika mai k'wak'walwa,ganin zaman bazai fishshe Shi ba yasa ya yi wanka ya d'au key ya fice.... . *story writing&editing* *Queen



* . . *ZEENATUby Queen



 page 71-72*  .  .      .    .  . ®NWA *Queen



* wajen k'arfe 11 na safe hajar ta fita bako tambayar haidar da tayi saima d'aukar mai kud'i da tayi,direct gidan kubra tayi shiga gidan tayi ta tarar da ita tana shanya da gudu ta rungume ta k'awata kin cika alk'awari nan taja ta falonta duk kujerun akarye ruwa ta kawo mata nan suka zauna suna hira ,nan hajar ta kalli kubra tace "dama na zone akan maganar mu dake mafita nake so ki bani" ,nan kubra tai wani lalataccen murmushi tace "kikawo kud'i kawai muje gidan boka" hajar tace "boka kuma nikam ban tab'a zuwa ba" ,kubra ta tab'e baki "ai se kiyi bakya son mafitar tunani hajar tayi yasa ta bud'e jaka ta d'auko dubu ashirin duk Wanda ta sata gun haidar kubra tace "yanzu naji zance" hajar tace "to yaushe zamu"? kubra tace "da zafi- zafi ai akan bigi k'arfe tashi mu tafi yanzu kawai",nan suka fito suka tari mota zata kaisu gidan boka... haidar dake kai kawo shikam ya gaji da halin hajar ga d'aukar mai kud'i data tsira ga yawo kamar taci k'afar kare,side d'in mami ya shiga jagwab ya zauna mami dake zaune tace "Anya haidar ka karya kuwa"? Naga idonka zuru-zuru ,kansa ya dafe mami "bansan ina hajar ta tafi ba daga fita naje na ciro kud'i a bank dawo wata na duba bata nan gashi yunwa nakeji", mami tace har akullm ina baka hakur haidar badon na had'a auren nan ba da tuni hankalin ka akwance,kayi mun biyayya haidar Allah ya baka masi ma" tashi tayi ta d'akko mai breakfast "nima hajar kaina bata girmamani Jiya har bangaza ta tayi ,San nan ta fasan kofuna nai Mata magana taumun gatsine" .haidar yace "mami kece tunfarko kika nace sai ita gashi yanzu tana bawa mutane wahala ,nikam mami rabuwa zan da ita" mami tace "Aa har abada Bazan kuma saka kayi saki ba tun Wanda nayi akan zee nayi nadama ko Allah ma baya San saki ka k'yaleta idan me shiryiwa ce Allah ya shirya ,yanzu kaga yar yar uwa tace" ,mami Amma bakya ganin Abubuwan datake yi ne ya shallake hankali" mami tace "zan yiwa umma magana" haka ya gama ya fita . wani surk'uk'in daji su hajar suka shiga kubra na gaba hajar na binta a baya kururuwa suka jiyo hajar ta k'ank'ame kubra ,Tafiya kad'an suka K'ara yakaisu wani k'aramin gida Bayan sun shiga boka ya kwarara ihu ,"sunnu da zuwa haj kubra. da samuwa kike ashe",kirari ta hauyi sai boka mai kankan ,muryar sa gandamemiya ya d'ago "to me Ke tafe daku"? kubra tace "ga wadda na kawo nan" ,hajar ya k'urawa Ido take ta firgita dariya ya k'yalk'yale "kinaso ai Aiki akan mijin ki to fad'uwa tazo dai- dai da zama" nan ya zaro wani leda magani ya bata "ga wan nan ki zuba mai a lemo wan nan kuma hayak'i ne zaki yi agidan to inde kikayi aise abinda kika ga damaryi a gidan ,Amma fa ki tabbatar ranar litinin kikai, inde aka samu sab'ani Aiki ya b'aci" kudi suka aje mai ya yafici kubra Bayan hajar ta fita "Amma kin iya farauta kubra wan nan tayi ,Amma zanyi Aiki akanta" ,Dariya sukayi dama kubra itake samomai customer sosai yake kashewa Mata aure ide yaga mace tayi mai,k'udi ya zaro ya bawa kubra. *story writing& editing *Queen



* .. [12:02pm, 10/11/2016] Kaleesat basheer: *ZEENATU by Queen



 page73-74*  .  .      .   *® NWA* *Queen



* Bayan gama breakfast d'in haidar direct makarantar su zee yaje ya tsaya yana daga cikin mota sai d'aga Ido yake ko zai gano ta,D'an sunkuyawa yayi yana duba wayar sa anutse take tafiya har tazo daf da motar d'ago war da zai ya ganta da sauri ya fito ya tare ta tsayawa tayi suka k'urawa juna Ido murmushi haidar yayi yana kallon cikin idonta ,batai murmushi ba kawai ta sunkuya yayinda take jin k'irjinta na bada dam! dam! ,tun bayan rabuwar su basu sake had'uwa ba sai yau "zeenatu pls shigo na kaiki gida" matsawa tayi ta baya taa wuce motar ya shiga kan yayi kwana har ta fita wajen gate kuu motar ta tsaya gabanta fitowa yayi ya tsaya gaban ta "zee hau ni haidar naki kike gudu",hmm! "to meye yayi saura tsakanina dakai Naga yanzu babu komi Haba kowa ya fuskanci future life d'insa mana". shiru yayi "zee kinsan ican't do without you saboda haka bai kamata kina mini haka ba", "haidar so nawa zan gaya ma ina sonka but na kusa aure kayi hak'uri kasan ba kyau nema cikin nema ammafa saka ranata end year don haka ka daina yaudaran kanka haka Allah yaso da Munyi rayuwa yanzu mun rabu sai kowa ya fuskanci gaba,haidar ina maka adduar samun farin ciki har k'arashen rayuwar ka" ,kasa katabus yayi har taje ta hau adaidaita sahu ya ja, da rud'ani ya shiga motar sa dak'yar ya iya kai kansa gidan su kb shigarsa d'akin ma ya tarar baya nan zama yayi ya dafe kan sa beauty face nata yake hangowa be auneba yaji hawaye na bin kumatunsa "ashsha!! Haba haidar akan mace ka zauna kana kuka" haidar ya d'ago yace "kb bakasan meye so ba wallahi son danakewa zee babu algus aciki ,ina sonta don Allah, na yarda da k'addara kullum sai na gwada cireta Amma kamar mayen k'arfe tak'i fita",kb ya kama Shi "sorry frnd Allah zai kawo mana mafita" sai wajen k'arfe 4 ya koma gida. hajar na zaune tana saurarar wak'ok'i a wayar ta haidar ya shiga harara tabishi da Shi zama yayi yace "hajar tun safe ina kika je"? shiru bata abashi amsa ba "tambayarki fa nake" tsaki tayi "inda ka aikeni" tashi tayi ta shige d'aki binta yayi d'akin yace yanzu abin naki yakai har kina d'ebar mini kud'i anya hajar kina son gamawa duniya lafiya kuwa,ciki ne da Ke haihuwa ko yau ko gobe kika sani ko ki mutu ko ki rayu, ya kamata ki gyara rayuwarki" "dalla.malam ya isa in so kake na mutu ai kaima zaka mutu ka damu dani ne ? don haka ba ruwanka da life d'ina" "hajar kefa kika nace kina sona har mami suka nace suka aura mini ke Amma ni kikewa haka" "nayi din kuma wallahi dani kake zancen kaida wan nan tsohuwar" fusata yayi jin ta ambaci mami k'yaleta kawai yayi darajar cikinta "hajar rabon wan nan cikin ne yasa kika zamo Mata ta Amma ki kuka da kanki",fita yayi daga d'akin yaje falo ya shiga kitchen yana k'okarin dafa tea..... *Story writing& editing* *Sueen



* . . [3:05pm, 10/11/2016] Kaleesat basheer: *ZEENATU by Queen



 page 75-76*  .  .    .  . *®NWA* *Queen



* "Ai wallah Amina na gano gidan nasu yanzu gani a mota gidan nasu zani Shawarar da kika ban Shi zanyi" aje wayar tayi dai-dai time d'im motar tayi parking a k'ofar gidan sun Dad'e a ciki Sa an nan ta fito wani yaro ta tsayar "kai nan ne gidan su zeenatu" yaro yace eh murmushi tayi San nan ta shiga gidan sallama take tayi da yake weekend ne wajen 11 duk suna d'aki bacci sallama ta kumayi da k'arfi San nan zeenatu ta fito matar tace "zeenatu nake nema" zeey tace "ai nice" Dariya maryam tayi azuciyar ta tace tabbs tana da kyau tsayuwa ta gyara "ni matar ma'aruf ce" zeey tayi Dariya "sannu da zuwa bari na kawo miki ruwa" dakatar da ita tayi tace "ba zama na zo ba kawai nazo nai miki kashedi ne, akan auren mijina da zaki domin na tanadi makaman yak'i akanki",zee ta yatsine "Ke saurara ya zakizo gidanmu kina mana hauka" ,maryam tace "wan nan har wani gidane" zee tace "tunda ba gida bane sai ki fita" maryam tace "ank'i" zeey tace "nakula baki da kai kuma mijinki ne sai na aura" Mari maryam ta kaiwa zee ,zafi taji itama ta rama da gudu mum tafito "Ke meye? Ke wace zaki zo kina dukar min 'ya"? maryam tace "wallahi idan bakiwa 'yarki kashedin aure min miji ba, sai na illatata" zeey tace "wallahi sai na auri mijinki sai dai ki mutu" janyo zee tayi ta kuma wanka Mata mari nan mum ma ta kaiwa maryam Mari "Haba Ke baki da hankali ne kizo har gida kina hauka wallahi in baki fita sekin gane aurenki,an gaya miki kishi hauka ne". sadiq ne ya shigo nan ya tarar maryam na surfa masifa,take ya zame hannu "wallahi ki fita konai boxing dake" zeey tace "kije ki sake shiri" maryam dake huci tace "to mu zuba ni dake D'an halak ka fasa" sadiq ne ya kai Mata naushi tayi gefe direct soro ta fita ta hau mota ta tafi,zee kuwa kuka ta saka ta shige d'aki, mum ma ta bita mum tace "kiyi hak'uri zee kowane bawa da yanda rayuwar sa take kasancewa", Bayan fitar mum zee ta d'au phone d'in ta ta sanar da ma'a ruf irin cin kashin da matar sa tai musu ,cikin fushi yace "zee kiyi hak'uri zan samu maryam d'in". *8:pm* ma'aruf ne zaune shida maryam ta inda yake shiga bata nan yake fita ba "Haba ya dace ace kije gidan mutane ki daki 'yar su kinga ai kin karya doka" kallonsa tayi "Haba wallahi Bazan zauna da kishiya ba" ma'aruf yace ai aikin gama ya gama domin d'aurin auren kawai muke jira idan zaki hak'uri ki rungumi k'addara to domin aurena da zeenatu babu fashi,zanyi auren nan be badon cin fuska agare ki ba sai don kawai nayi bouts, kuma last warning kar ki kuma fita da zuwa gidan surukaina na gaya miki ,kin jawon Jin kunya se kace kanki aka fara kishiya" da kuka ta shige d'aki binta yayi ya hau lallashi domin baya son b'acin ranta amma kamar zugata yake kawai seya k'yaleta ya fita ,direct gidan su zee yaje. kiran zee yayi ta fito idon nan luhu-luhu alamar taci kuka "ma'aruf mu hak'ura da juna tunda kaga yanda matarka tayi min", "Haba zeey kar wan nan ya b'ata ranki duk barazana ce yanzu ma saida nayi Mata fad'a don Allah kiyi hak'uri zeey I luv u so much,Bazan iya hak'ura da keba,ba yanda zatai tace ta hak'ura San nan ta kalleshi "Amma kaiwa matar ma kashedi bana d'aukar reni bar ganin tana ganina k'arama ko don ta girmeni, ni da zuciya d'aya zan shiga gidan ka" birgishi tayi yace "madalla zeey insha Allahu hakan bazata kuma faruwa ba" cewa yayi tayi mai sallama da mum soro ya shiga mum ta fito nanma itama ya bata hak'uri tace ba komi kishi Ke damunta ,Godiya yayi sukai sallama da zeey ya tafi cike da k'warin gwiwa. *Story writing &editing* *Queen



* . . *ZEENATU by Queen



 page 77-78* *NWA* Queen



 *dedicated this page to Maryam Oumeey & husna Tnz 4 d care* yau hajar da k'arfin gwiwar amfani da maganin boka ta tashi haka kubra ta bugo mata ta dad'a jadda da Mata wak'e- wak'e take yau waje satin d'aya bata lek'a kitchen ba sai yau ta tashi taje ta dafa wata indomie guda biyu da k'wai ta Barbad'oshi da magani duka dinning taje ta aje ta koma kan kujera ta zauna haidar ne ya fito da shirin fita Aiki da yake yau Monday tararsa tayi "ya haidar ga breakfast nan nayi maka", da mamaki ya kalleta yasan bata Saba ba ganin ta tsare Shi da Ido yasa ya je kan dining din ya had'a tea ya kurb'a, kubra tana tsaye kansa tsegege, "ya haidar kaci indomie d'in mana" "ai kinsan indomie ba cimata bace kawai ki cinye nagode" fita yayi tana tsaye kamar ta kurma ihu tsaki tayi "Yanzu nayi a sarar kud'ina Ke nan tab wallahi seka biya" da sauri ta bishi kamar ba bai ciki ba,kira ta k'wala Mai har ya bud'e mota ya tsaya ta karasa "ka bani kudi zani sai Abu" "wane Abu ne Abu"? tsaki tayi ta d'aga murya "malam in bazaka ban ba ka gayan ganin Mai gadi ya lek'o ta d'an d'a d'akinsa yasa ya zaro dubu d'aya ya bata ya shige yaja baki bud'e ta bishi da kallo,."na daiyi asarar maganin boka" basarwa tayi ta shiga ciki. yau mami ta kuma komawa gidan su zee lokacin dad na nan rok'onsa ta kan abasu dama ta biyu dad ya kalleta "hajiya agaskiya mun riga anyi magna da wasu kawai ayi hkr zaman da sunkai da ma ya wadatar, Allah ya harda kowa da rabon sa,ba yanda ta iya haka ta koma gida. Cike da jimami. zaune ta yi Tayi jugum hajar ta shigo "hajiya ga kaya na nan na kasa wankewa ki wanke mini saboda bana bawa Mai wanki sleeping dress" mamaki k'arara hajiya tayi ta d'ago ta kalli hajar "Yanzu don baki da ta'ido nice zan niki wanki"? "hajiya to meye aciki Naga cikin D'an ki gare ni" Mari hajiya ta kaiwa hajar ihu ta saka "wallahi akan haidar zan fanshe". kuka ne ya kubcewa mami ga haushin da takeji na zuwanta gidan su zee ,ga kuma hajar d'iban kayan tayi taje bangaren hajar din ta watsa Mata tace "idan ba zaki wanke ba ki zauna haka" tsaki hajar tayi "wallahi dani kuke zancen anbu an samun Ido" mami tana komawa ta bugawa umma waya tace tazo tana son ganin ta,nan tace zata zo Anjima. misalin k'arfe 4 umma maman hajar da kawu sule k'anin mahaifin hajar,suna zaune mami na zayyane musu irin abinda hajar Ke musu,hajar ce ta d'ago "wallahi umma wani abin kawai fad'a take" Mari kike ki kau kawu sule ya bata umma kuwa huci kawai take "lakle hajar wuyanki yayi k'wari, yayar tawa kike gayawa haka, to ko kema kin shiga layin da 'yanmata Ke Kar a ragawa uwarmiji? to ki sani Ke uwarkice domin yaya tace wallahi hajar idan baki hankali ba sai na miki baki" ,kawu sule "yace in Banda sharrin zamani har hajar guda nawa take" umma tace "sharrin k'awaye to wallahi ki sani hajar k'awaye sai su kaiki su baro muddin baki na kirki ba,Yanzu ko Ke ki kaga anama mami haka ai Kya shiga" mami sa ta share hawaye "da hak'k'i tabbas domin mun ci zalinn zeena nice ma na bada goyon baya hak'k'in yarinyar Ke bina" Amma nayi Dana sani" umma ta katseta "yaya nasan komi duk abinda ki kayi be kamata hajar tayi miki ba,ba irin kukan da bata minba kan na shige gaba, ta Auri haidar don tana son sa Amma Yanzu kika tulank'asa a Ido idan ma k'awaye Ke zugaki kaiki zakuyi su baro". d'ago kai tayi ta kalli mami ta harareta ta gefe kawu ya kai Mata duka cike da tsawa yace ta tashi ta fita ,umma ta tsaida ita "Allah idan bakibi mijinki da mami ba ,bani bake" fita hajar tayi tana k'un-k'uni tsaki tayi Wallahi duk abinda akai mini kan haidar zan k'are. to fanz Ina godia bisa k'aunar ku. *story writing&editing* *Queen



* . . *ZEENATUby Queen



 page79-80*  .  .    .  .    .  .   *NWA* *Queenmee* kubra na gaban boka Mai kankan ya kalleta "ina wan nan matar ne ina sonfa Aiki akanta don tayi mini",kubra tace "Aa bari ta haihu" to ba matsala inji boka,"tana haihuwa ki gayan" kubra tace "karka damu Mai kankan" . Mata ne dank'am sunbi layi suna jira a kirawo su ,Allah ya kiyashemu tab'ewa ka shiryi matan musulmi baki d'aya. *Bayan kwana 2* yau aka kawo lefen zee tamkar na budurwa Aneee sai rawar kai ake da munay suna tare a d'akin aneesa zee tace "nide gabana fad'uwa yake wallahi bana son aure Yanzu" munay tace "kaji banza idan ba kiyi bamu guri, don kin samu ma zance miki Anty inkika zama matar yaya" zee tace "dalla karki fad'an mana dole dai kice da mijin iya baba" Anee tace "Ke ki had'a mana k'auye day mana" zee tace "ba abinda zan kawai zan kirawo husna ummu samha tazo tai mana lucture" munay "tace bar matar yayan nan wallahi se Munyi" zee tace "ni fa nafiso abari na gama poly d'ina kinga Yanzu hutun second semester zami" anee tace "kyayi kya gama har anko sai mun fitar" wayar zee ce "tai k'ara ma'aruf ne ta juya musu baya tana k'us-k'us. haidar kuwa Dan tunda yaji ankawo lefen zee duk ya birkice domin yana samun information gun kb saboda Anee na gaya Mai ,yau da yake zaune office ya kifa kai yana tunani kansa yaji yana ciwo ya tashi ya fita ,gun kb yace su had'u gidan gonar sa yana zaune sai Shan tea yake kb ya shigo aboki ya fad'a haidar suka gaisa ,haidar yace "Dubai zan tafi ,Bazan iya ganin zee ta tare da wani ba" kb yace "har kullum ina baka hak'uri saboda komi daga Allah ne ka kwantar da hankalinka I tsumma a randa", Dariya haidar yasa "wannan Karin maganar fa"? kb yace "agun kaka na koyo kasan goyan kaka ne ni" haka sukai ta hira sosai ya mantar da Shi . *Bayan kwana 2* rashin kunyar da hajar keyi da irin tab'argazar da takewa haidar yasa Shi damuwa kad'an -kad'an ya fara rashin lafiya a tsai-tsaye ,wajen k'arfe 4 na yamma haidar yaje saiwa mami turare a supermarket Bayan ya d'akko yazo gun counting idon sa ya gano Mai zee da ma'aruf da faty sun shiga supermarket d'in Sam bai bari sun Ganshi ba saima wani kishi da yaji ya zubo Mai domin muddin ya tsaya zai iya barin abun fad'e don yanda yake ji kamar ya kauda ma'aruf haka ya koma gida a fusace tunda yaje gida k'irjinsa Ke ciwo ,ga hajar nayi Mai hauka aka kamar ya kurma ihu k'irjinsa har wani ta fasa yake zuwa yayi ya d'akko kank'ara ya d'ora ko zai samu sanyi a ransa Amma ko gezau kawai hawaye ne ke zuba,tashi yayi zai je side din mami kamar me yaji kansa na juyawa ga k'irijin sa ya rik'e be aune ba yajishi wanwar ak'as. ihun Mai gadi ne ya sa su mami suka fito lokacin husy ta dawo Hutu ,haka hajar ma ta fito nan suka cika gun da kururuwa da k'yar aka sashi a mota husy ta jasu sai hospital,nan danan aka karb'eshi da yake private ne cikin awa d'aya suka shawo kan matsalar fitowar doctor yana goge gumi yasa su husy saranda tunkan yayi magana cikin hajar ya murd'a take tafara nak'uda da yake dama watan haihuwar ta take ,kuma nan hospital d'in take awo cikin sauri nurses suka shiga da ita Labour room .. *STORY WRITING & editing* *Queen



* *ZEENATU by Queen



 page 81-82*  .  .    .  .   *NWA* *Queenmee* Bayan kamar awanni akace hajar ta haifi baby gal cike da farinciki mami ta tari nurse d'in, husy kam tana tagar dai-dai inda aka kwantar da haidar sai kuka take suna nan tsaye umma tazo nan suka tafi gun hajar doctor ya buk'aci ganin mami sun zauna yake gaya Mata damuwa ce tayi Mai yawa ya kamu da hawan jini Amma baiyi worst ba kuka ta saka "to doctor ya za ai"? nan yace "ba matsala mun shawo kan matsalar tasa tunda batai girma ba ,Amma adunga Kula da b'acin ransa tunda ga larurar data same Shi "haka ta fito a tana matsar hawaye nan husy ta tare ta suna kuka "husy duk nice silar saka haidar cikin matsala tabbas nasan da matsalar hajar gashi ya k'wallafa raiga zee husy tace "mami sai hak'uri" dai- dai lokacin aka fito da hajar akai rest room da ita wajen 6pm aka bawa su hajar sallama domin lafiyar ta lau, suka tafi itada umma direct gidan su aka wuce da ita saboda babu damar ta zauna anan tunda larurar data samu haidar,shikam haidar sai 8pm ya farka duk yayi zuru-zuru mami dake zaune ta kalle Shi "haidar sannu" husy ma haka da k'yar yasha tea mami kam ta kasa tsugum Washegari hajar da sassafe ta bugawa mami waya lokacin tana hadawa haidar tea wayar tayi K'ara ta tashi ta mik'o mata ba gaisuwa balle tambayar jikin haidar tace "mami babu naman gashi fa saboda Allah ace tun jiya babu Wanda ya kawo komi" mami tace "to rasa kunya har bakin naki ya bud'? kinsan dai halin da mijinki Ke ciki kuma ina wajen sa Haba kina alkunya mana" tabe baki hajar tayi ta kashe wayar. Bayan kwana 2 da haihuwar hajar mami tasa aka kai mata duk abin bukata can ma sai da sukai fad'a da husy domin suna kaiwa hajar ta ture kaya wai basi Mata ba da yake husy bata k'yaketa tace kar ta d'auka d'in, yau kwanan haidar uku ya fara dawowa normal waya aka bashi yayiwa hajar ba gaisuwa balle ya jiki ta hau fad'an kaya sunyi kad'an baice komi ba ya kashe wayar,haka dai hajar tayi ta rashin mutunci kubra na zugata k'arshe ma cewa tayi bazata shayar da 'yar ba tunda mami bata k'aunarta har haidar din sai da aka kai ruwa rana san nan tace sai an bata kud'in shayar wa ran umma ya b'aci tayi mata duka babanta kam cewa yayi zai sallamata duk da jegon data Ke, ranar suna kuwa yarinya taci suna Aysha an yanka raguna 2 aka duk gudun mawar data samu haka ta bawa kubra tace taje gun boka ai mata aiki kan haidar da mami,umma addua kawai takewa hajar. satin haidar biyu Allahu yasa ya warke kb ne ya d'auke shi suka koma gida yana son sanar Mai bikin zee da ya rage 3wk Amma yak'i gaya Mai saboda ciwon sa,bayann sati d'aya haidar ya dad'a girgijewa kullum sayyaje ganin baby Mai kama da husy sak Amma da b'acin rai yake dawo wa din hajar ta bud'e huta musammn da kubra ta dada shigarta yau sai data ambaci mami tayi rashin kunya haka ya mammareta taci kwalar sa badon da sanayyy ba da tuni ya saki hajar.Allah ya shirya maasu hali irin hajar. ganin katin bikin zee ya sa yayi haidar damuwa shiri yayi tsaf, yayiwa mami sallama zai je Dubai ya d'an huta yayi haka ne don ya guje ganin auren zee don Shi ya san wahalar da yasha tabbas ya san ya rasa zee zaiyi ta addua Allah ya gyara halayen hajar Washegari yayi shiri k'arfe 8 ya fita sai da ya biya ta k'ofar gidan su zee ya bawa sadiq later da ambulan yace ya bawa zee san nan kb ya Lula dashi birnin kano don ya hau flight da wuri . *Story writing&editing* *Queen



* . [3:30pm, 17/11/2016] Queen💋



: . . . *ZEENATU by Queen



 page83-84* â™  â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™ . â™  *NWA* *dedicated to Lubie &bena* *Queen



* sadiq kam komawa yayi ya mik'awa zee sak'on haidar akasalance ta bud'e ta fara karantawa kamar haka _zeey naji labarin zaki aure nayi jimamin rashinki zuciyata bazata iya ganin kin auri wani ba, ayanzu na bar k'asar ma ,Allah ya baki zama lafiya keda sabon angonki yasa ya rik'emin Ke amana ga gudummawa ba yawa luv u 4 ever_ _daga_ _haidar_ jikinta ne ya jik'e sharaf da gumi kamar me jin zaifi,zuciyar ta taji na rad'ad'i surar haidar ta fara tunanowa ahankali siraran hawaye suka zubo Mata "I miss u so much haidar" d'ayar ambulan ta d'auke ta Bud'a kud'i ne 'yan bandir na dubu suka suka zubo d'auka tayi yayinda taji kud'in na k'amshin turaren haidar lumshe Ido tayi tana ajiyar zuciya,ganin ba sarki sai Allah yasa ta tashi ta kwanta bacci,d'akin mami ta tashi ta lek'a ganin su sadeey tayi nata kuma kallon lefe "tsaki tayi ku bakwa gajiya da kallon lefen nan ne"?, "eh wallahi ya zee kinsan kayan da D'an karan kyau" tab'e baki tayi ta koma d'aki tana nai zancen zuci. mami na zaune Alhaji baba na kan kujera wan baban haidar ne "agaskiya mami banji dad'in abinda ya faru ba ,ashe Shi haidar sun rabi da yarinyar nan, ai ban sani ba sai jiya mariya Ke gayan kakanta abokina ne banji dad'i ba ,nan mami tace sai hak'r don nice ma sular rabuwar nasu gashi na aura Mai 'yar k'anwata Sam baya jin dad'in zama da ita har ni kaina" ,Alhaji baba yace "anyi kuskure dama Allah baya barin hak'k'in wani Dan wani idan kace tukunyar wani bazata tafasa ba taka ko gumi bazatai ba,Haba hajiya gashi kin sayawa d'anki rashin kwanciyar haankali da kanki, ina mamakin matan da zasu sa d'ansu ya rabu da matansa alhali ya naso don son zuciya ai gashi kin rabu data kirki a ganinki ta mallake miki d'a ko? to aiga irin ta nan kin aura Mai wata Ke tana gasaki" "sai hak'uri nayi nadama sosai", "Yanzu ita yarinyar aure zatayi Ke nan ko"? "eh wallahi" jinina kai yayi "Allah ya bata zama lafiya,ita kuma wan nan Allah ya shirye ta, kinga ko! gashi nan D'an naki yayi nesa dake ,d'a Mai biyayya Mai yasa wasu iyayen Mata 'ya'yan da suka fi muku biyayya kunfi tursasu akan abinda basa so"?. "Ayi hak'uri sharrin shed'an ne" tashi yayi "Toni kam na tafi Allah ya gyara al amuran" *Bayan sati biyu* yau ne aka shiga satin bikin zee da yake ma ambasu Hutu shiisa abiin yazo Mata da sauk'i duk wasu d'unkunan ta yana wajen su anee su zasu kai sun dai Nace sai sunyi event ko d'aya ne ,Anty bara kam yar sokoto ta d'akko tundaga kano aka fara gyara zee tana zaune suna hira ta fara fitowa ragad'ad'au ma'aruf ya bugo Mata waya yana tambayar ta yawan kud'in data keso na lunch nan ta had'ashi da anee Anty Bara Ke kiran sadiq Dan yazo ya sayo lemuka zee tace Anty "Ay tun last week ya tafi school kin san ya shiga KUST wudil" Anty bara tace "maaha Allah nayi Mai murna ,ashe badashi zany kaiki d'akin ma 'aruf ba" zee tace "wallahi nayi missn sadiq abokin fad'a na". Thursday suka fara biki duk daba auren fari bane nan dai akayi lunch police band na buga kid'a su anee an cashe ga frnds nata na school sunyi kyau sai selfie suke gwanin sha 'awa zeey tayi kyau tamkar flower an taru sosai akaci aka sha aka watse washegari Friday akayi lecture inda ummu samha tayi magana akan muhimmacin aure da zaman aure da hak'uri acikin sa nan ma kafin magrib an watse. Washegari ta kama Saturday wato ranar d'aurin aure zee ta had'u ta had'e da yake ta D'an Kara k'iba kad'an sai tafi kyau duk inda tayi walwali take k'afarta da hannu duk an mulmule Shi da k'unshi an yarfa Mata kitso mitsi-mitsi tamkar ka sace ta ka gudu an d'auro auren a masallacin jumma'a jama a da dama duk suka dawo gidan don cin abinci fateey ce ta shiga gidan da su zeey Ke tattare da k'awayenta tana haki "ya zeey wallahi bada ya ma'aruf aka d'aura ba! anee da munay suka mik'e zeey tace "to dawa aka d'aura" falfalawa da gudu tayi "Nima bansani ba"... "to masu karatu ku biyo ni don jin wanga wan nan sauyi da aka samu". *story writte &edited* *by Queen



* [3:52pm, 18/11/2016] Queen💋



: . *ZEENATU byQueen



page 85-86* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™  *NWA* *Queen



* *dedicated this page to oll fans of ZEENATU* kuma dawo wa fatee tayi tace"ya zee nifa banma sani ko gaske ne ko ba gaske ba, kawai de naji kamar maroki ba ya ma'aruf yake ambata ba",munay ce tace "Ke tsaya" fita sukayi tare ganin sabuwa na k'ok'arin shiga gidan su zee yasa munay ta tsaida ita "sabuwa wai bada ma'aruf aka d'aura ba"? sabuwa tace "eh man kinga ikon Allah ko",sai dai bansan dawa aka d'aura ba "dankari" munay tace wayar ta d'auko Layin ma'aruf ta latsa daga can ya d'auka "ya ma'aruf me nakeji haka wai dagaske ba da kai aka d'aura ba"? "eh mana" munay tace "to maiya sa ya ma aruf"? nan yace "in kinzo gida kyaji dalili" a salub'e ta koma gidan da suke zee na kwance ta tashi "dagaske ne"? "eh mana wallahi Yanzu ya ma'aruf Ke gayan" dafe kai tayi tasa kuka "ni to dawa aka d'auran aure na shiga uku" lallashin ta suka shiga yi Amma kamar zugata suke dai-dai lokacin Anty bara ta shigo,nan ta kama zee tace "muje gida mum nason ganin ki", san nan ta kalli su Anee tace"ku jirata". Bayan sunfita direct falon dad ta shigar da ita dad da mum ne a zaune dad yace "zeey zauna anan" nan ta zauna tana kuka mami tace "rabon kwad'o ko yana sama sayya samu,ikon Allah yafi ga haka ,an d'aura aurenki da haidar ba ma'aruf ba" d'ago kai tayi da sauri tace "mum garin yaya Bayan haidar baya kasar"? mum tace Nima dai bansan dalili ba dai dazu babanku Ke gaya mini. dad yace "baba Alhaji abokin kaka shine yazo ya Sameni da maganar duk da ina jin nauyin sa, Amma haka nace an gama magana da wasu sai dai hakuri,to Bayan yabar nan direct gidan su ma'aruf yaje ya tattaushe su baban ma'aruf yace bashine da auren ba nan ya kira mami sukaje gun ma'aruf mami har dasu kuka dan ya bari a d'aura da haidar tace ya kamu da hawan jini gashi yabar ma k'asar duk Dan saboda Ke haka dai aka had'u dad da baban ma'aruf da baba Alhaji da mami nan ma kukan tayi tausayi yasa maaruf yace ya janye shine fa aka daura da haidar,hatta kayan lefe yace yabar miki Amma Nace aa dole ya anshi abinsa anjima Bayan an kaiki za a kaimusu lefen su,zeey tace "Allah sarki ma'aruf" nan ta tashi ta fita no d'in ma'aruf ta buga ya d'auka ,kuka ta saka "ya ykai haka" nan ya hau bata hkr yace "zeey ki k'addara dama bani ne mijinki ba, bansan lokacin danace na hak'ura ba ,sai kuma Yanzu zuciya ta Ke tuk'uk'i da Dana sani domin duk wanda ya sameki ya more, Amma babu komi haka Allah ya k'addaro ina maki Fatan alheri" k'it ya kashe wayar tabi wayar Tata da kallo cike da mamaki, haka ta koma su Anee sunyi cirko-cirko nan ta zube ta gaya musu tana kuka. munay kam rik'o ta tayi "tace karki damu duk danima naso ace anyi da yayana don zumuncin mu ya d'ore Amma Allah bai yiba Yanzu kawai ki fiskanci gaba dama can haidar naki ne ,kin fidda rai dashi gashikuma ya dawo" k'arfe 6 dai-dai aka zarce da zee tamfatse-tsen gidan ta wanda haidar ya fara ginawa mami ta hanashi Yanzu da kanta tace a kaita can d'in,gida ya tsaru kamar ka sace kasa ajaka abin mamaki mami ce agidan ita da husy zuwan su zee da sauri ta rungumeta tana welcome back my douter anan ma saida ta kuma neman afuwar zee ita kam tace ba komai kowa ya tafi akabar zee husy dasu Anee . mami ce ta tsaida kb tace to kb "kaga haidar baisan am Maida auren sa da zee ba ,to nasan ka sai ka gaya Mai karka gayamai saboda ina son yimai suprise ne, don bakaga fad'i tashin danai kan adawo Mai da ita ba ,so nake yanda nasa ya rabu da ita gashi na dawo Mai da ita kaga na wanke kaina,haidar yayi min biyayya wallahi",kb yace "mami muna godia kuma insha Allahu Bazan gaya maiba" "yawwa kb sai de kagaya Mai ya dawo gida ka dai son yanda zakai Mai" kb yace "masha Allah mami godia muke ,dad'i ne yayi wa kb yawa ya fafari mota itama mami tashiga nata motar driver yaja . to makaranta Baku tambayeni labarin hajar ba ?. kodai Baku tambayeni ba insha Allahu komi zai gudana daga taskar yar mutan kano,karku bari abaku labari. *story writte & editted* *by Queen



* [5:57pm, 19/11/2016] Queen💋



: *ZEENATU by Queen



 page 86-87* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . *NWA* *Queen



* zee na zaune sai kallon d'akin take Anee tace "su zee manya gaki kuma kin dawo wa haidar",munay tace "kuka ya k'are" husy ta dafa zee ta ce "naji dad'in dawo warki zee domin ya haidar kullum sumbatunki yake" ,su Anee su ka k'yalk'yale da Dariya munay tace "ai sai su had'iye juna Yanzu" zee ta d'aka Mata duka tashi sukai suna zagaye gidan sama da k'asa ne duk abinda Ke a k'asa shike a sama ko ina zam -zam da kaya kiran magrib da akai yasa su Anee sukai haramar tafiya nan zee ta rik'esu su tana kuka "Banda kamar ku a k'awaye kun zame mun 'yan uwa Allah ya barmu tare ya kaimu aurenku kuma" jikinsu asanyaye suka tafi da yake dama kb ne zai Maida su haka gidan ya zauna daga zee sai husy ita zata na tayata kwana kan haidar ya dawo,hira suke tayi nan suka dad'a saita guraren sunayi suna hira wajen 8:pm driver ya kawo lafiyayyen abinci daga gidan mami wan nan Ke nan. kb dake zaune da laptop agabansa suna magana da haidar ta email nan yake ce Mai "shegen sama ka dawo gida kaga abin mamaki haidar dake zaune a farfajiyar hotel d'in da yake ya yinda k'afa fuwansa Ke cikin swiming pool d'in gefe laptop ce a ajiye, ya Maida Mai da sak'o ai na kusa nida bawo sai baba tagani" "kb yace matarka da babynka na jiranka tsaki haidar yayi "na bada amaanar su gun mami",kb yace "kai zancen gaskiya kawai ka dawo idan ba hakaba ta wuceka pls wallahi da gaske nake" haidar yace "ok ka saurareni next week" kb yace "oh no yayi yawa kawai ina laifin jibi,haidar yace dad'ina dakai naci kb" " no problem by the grace of GOD wenesday ina Nigeria" kb yace "okey ko kaifa Ana gaya maka kana kubcewa" haka dai suka gama hirar. hajar dake tumbotsai ta had'a kaya akwati ummm Ke ce Mata gana "hajar ko fa Arba'in bakiba ya zaki koma Bayan mami ma ban gaya Mata ba,zumud'in me kike Bayan saura 10days ki arbain d'in",hajar tace "barni umma wai ni za'aiwa cin kashi wan nan zee d'in za'adawo da ita to wallahi koni ko ita duk munafurcin mami ne" kau! kakeji umma ta kaiwa hajar Mari kuka tasa "Allah umma Yanzu bakya sona" umma tace "ai dole kin canja hali, agabana kicewa yayata munafuka wallahi hajar ina ji miki na dama, sai kuma ki bari Alhaji ya dawo kya tafi" cike da jin haushi taja jaka k'irrr ta fita Mai taxy ta tara shiya loda akwatinan ta a cikin jaka tana rik'e da baby umma na kiranta ko kulawa batai ba yaja suka tafi. mami na zaune tayi bak'uwa suna hira taji K'ara bata Kula ba, haka hajar ta kira maigadi ya d'ebe akwati nan ta ya shiga dasu shashinta haka ta bud'e tai zaman ta ganin alamar mami nada bak'i yasa ta basar,wajen la'asar ta shiga mami na sallah ta aje Aysha agefe Bayan idarwa tace "mami na dawo tunda bakya sona Yanzu bare ta fini kuma wallahi duk bak'in cikin D'an tsako baya ci D'an shirwa ba,naji labari andawo da zeey to wallahi Bazan yarda ba" mami "tace aike hajar na sallama lamuranki domin baki da kunya nayi dana sanin aurawa D'ana Ke duk da rabon wan nan 'yar ne Amma wallahi kishiga tai tayinki" hajar ta ture fulawar dake falon ji kake tossh!!! ta fita ta doko k'yauren kuma dawo wa tai "mami kuma wallahi Bazan co gaba da zama kusa dake ba, saboda Bana son sa Ido" jin-jina kai kawai mami tayi. Amarya zee kam kullum cikin kwalliya zaka ganta tamkar haidar na nan cike da kwanciyar hankali ga wayar ta da suke chating da frnds kullum mami Ke sawa a aika musu da abinci. *Bayan kwana biyu* yau ta kama wednesday tun k'arfe 2 haidar na Nigeria dai -dai bai shiga jigawaba saboda yana clearing wasu kaya a kano sai 6 dai-dai haidar ya iso jigawa direct gun mami yaje yana ganin ta yace "I miss u mami" cike da farin ciki ta tare Shi ,nan ta Kece Mai "hajar fa ta dawo Sai dai tsiya taku take abinda nake so dakai kaje d'akin ka na nan kayi wanka ka shirya sai kazo "akwai sak'on da nakeson baka ka kai wani gida, kallonta yayi "mami tom bari naje" fita yayi ta bishi da kallo tana Allah ,Allah ya gama ya fita don bata so su had'u da hajar ta b'ata masa shirin. 6:30 ya gama komai ya fito d'as dashi sai tashin k'amshi yake tana sanye da jins black da tshrt white ga shi yasa agogo k'irar Gucci ya manna sai tashin k'amshin turaren ud yake sumar nan ta taju kana ganin sa kaga handsome Sam bai dace da hajar ba sai da ya zauna yaci abinci san nan ya tafi. kaya ne a wani kit mami ta bashi tace ya kai tamai kwatancen gidan motar sa ya shiga ya faka ,mamaki yake ganin unguwar da gidan sa yake ganin gidan sa an k'arasa Gina Shi yasa Shi mamaki, waswasi ya shiga yi ganin maigadi a k'ofa suka gaisa direct gidan ya shige door bell ya danna tsayuwar mintuna ba a bud'eba mamaki yake kawai ganin haka yasa ya cusa kai cikin falon tsaruwar falon ya birgeshi direct kitchen ya zarce, tana tsaye tana yanka musu kankana sa zasu sha itada husy ,tasa wani riga da siket fitted d'inkin ya kamata d'as gashin nan daya sha yiri-yirin kitso ta bazo Shi 'yar wak'a take gama kallon ta yayi yasa k'irjin sa ya buga magana zai kawai ta juyo suka had'a Ido. "haidar" ta ambata D'an murmushi tayi tazo ta wuce ta haye sama aguje,shi kam mamaki yake me yasa mami zatai Mai haka Bayan tasan hakan matsala gareshi ,wayar kb ya buga nan ya labarta mai yarda ledar hannun sa yayi "pls kb da gaske ne" nan ya gaya Mai duk yanda akai Alhamdlh kawai yake fad'a k'it ya kashe ya buga wayar mami nan ma murna yayi tayi yace "mami kin mini komi nagode am proud of you mamina" nan mami tace "shine tukuicin da zamma don dawo maka da farincinka". sama ya hau ahankali ya bud'e d'akunan duk bata ciki d'ayan yaje ya bud'e tana kwance kan bed tana Dariya kamar an tsikareta ta tashi taje gaban mirrow tana kallon kanta ahankali ya taka ya rik'o hannunta ta bayan ya kwantar da kansa a kafad'ar ta "Alhmdlh masha Allah zee godia ga Allah mad'au kakin sarki daya dawo min dake farin ciki na,zee Ni dake mutu ka raba I luv u so much" ahankali ya fad'a Mata akunne "zee ina missn kamshin ki" juyowa tai suka k'urawa juna Ido "welcome back my husby" murmushi ta sakar Mai wani shauk'i suke ji duk su biyun wanda bazasu iya misaltawa ba gam-gam ya rungumeta suna shakar k'amshin juna..... *story writte & editted* *by Queen



* [5:34pm, 21/11/2016] Queen💋



: *ZEENATUby Queen



 page88-89* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™  *NWA* *Queen



* kwana biyu haidar da zee na murzar soyayyar su haidar ko fita baya yi duk ya kashe wayar sa jinsu suke kamar Yanzu ne had'uwar su na farko,har wani fresh sukayi Shi da ita haidar kam cimar sa ta canja,domin zee ta dad'a yo course na Kula da miji ga tarairaya da biyayya Sam sai Yanzu yakeji kamar ya dawo daga nauyayyan baccin daya ke,ga dad'ad'an k'amshin da yake kwasa. hajar ce tsaye a falon mami tana jijjiga mami tace "yau Naga ikon Allah" hajar tace "baki ma gani ba Sai randa haidar yazamo a tafin hannu na wallahi, da cin amana Ni za' aiwa haka wato an barni Ni kadai Ni da Ke su suna can sabon gida to wallahi ba'a isaba" kau husy ta kai Mata Mari tace "wallahi ki kiyayeni Yanzu na dawo Hutu Bazan yarda da rashin kunyar ki ba mami ai ba sa'arki bace" cakumar ta ta yi nan suka hau dambe da k'yar mami ta rabasu ta nunawa hajar hanya nan hajar ta d'au Aysha "wallahi dani kuke zancen ba'a isa a taka Ni na k'yaleba, fuuu ta fita part d'inta. tana zuwa ta d'au jaka da mayafi ta d'auka ta fita Mai adaidaita sahu ta tara dayake Yanzu mami tace ta daina hawar Mata mota ,gidan kubra taje nan suka rungume juna da murna hajar tace yau da zafi -zafi nake so ki zo muje gidan Mai kan-kan domin sun kaini k'arshe kubra tace "Hhh waya gaya miki barno gabas take ,ay dama kud'in ki na nan Sai kizo muje" hajar tace "da shirina nake" nan suka fita suka kuma tarar adaidaita Sai gidan boka yana zaune Mata sunbi layi su kubra suka shige, nan ya washe baki ya kurma ihu murmushi kubra tayi "Sai Mai kan-kan nan" yace "to Alk'awarin nawa ne"? ko kuma kubra tace "Aa buk'ata ce take tafe da ita, nan ta labarta mai kan a yi mataa maganin uwarmijin ta, san nan a karkato da hankalin haidar kanta" Dariya boka yayi muryar sa kamar ta jaki tsayawa yayi da dariyar yace "to a aje kud'i" wani magani ya d'auko ya nuna Mata "gashi wan nan ki barba d'awa uwarmijin naki a k'ofar d'akin ta, Shi kuma ki yi masa lemo yasha" washe baki tayi tana godia. fita sukai kubra ta dawo nan yace "Ke kubra kar mi fad'a dake, domin na gaya miki ina son wan nan Amma kink'i bada goyon baya amma wallahi Sai nayi Aiki akanta" kubra tace "Ni tausayi take ban dama ka k'yaleta", Mai kan-kan yace "auren Mata nawa na kashe? basu suka kawo kansu ba" ,kubra tace "to ba ruwana aciki" nan yace yaji haka ta kama hanyar fita suka tafi,hajar daga gidan boka bata zarce ko ina ba sai gidan zee. wajen 6 kubra ta tsaya kafar gidan k'wafa tayi tana huci ta shiga ciki "Lalle Ni za a yaudara, to wallahi da sake falon ta shiga k'amshi ya doko ta haidar ne da zee mak'ale da juna akan kujera suna soyewa ihu ta kurma "Yanzu haidar dama cin amanata kake? wan nan zee kwai mayya" aje Aysha tayi ta cakumi zee nan zee ta rike hannunta "wallahi kar hannunki ya tab'a jikina domin da ba Yanzu bane kin gane Mai guri yazo Sai Mai tabarma ya nad'e" haidar kam takaici ne ya ishe Shi yaje ya d'au Aysha dake kuka nan yace "hajar keda ko arbain baki ba shine zakina yawo da baby? kizo ki koma gida" harara ta kai mai"Bazan koma ba haidar wallahi Nima Sai anban d'aki anan zee tace "Kinyi kad'an domin nan gidana ne, ba naki ba" tsuke baki tayi ta kaiwa zee Mari zafi yasa ta dafe gun nan itama ta rama haushi yasa zee ta turmushe hajar tana duka idon ta ya rufe Sai ihu hajar keyi Sai da haidar ya daka musu tsawa san nan suka rabu zee ta haye sama nan hajar ta tashi tana kuka "wallahi tunda ta kwailen fuska Sai na rama" Mik'a Mata Aysha yayi yace ta fita direct yace driver ya Maida ta da k'yar ta tafi . tsaki kawai haidar keyi Shi kam ya rasa yanda zai da hajar saman ya haye inda zee Ke kuka nan ya kamata sorry my everlasting ganin Taki hak'uri yasa ya Lula da ita duniyar masoya take suka manta da wata hajar. hajar kwa 8 dai-dai ta shiga gida nan ta zauna tana ta sak'e -sak'e haka dai tayi- tayi ta kwanta bacci,da safe kuwa wajen 10 ta shiga side d'in mami suna breakfast ita da husy zama tayi tace "Amma wallahi mami Bazan tab'a yafe miki ba", nan haushi ya kama mami tace "Ke zee rashinn rashin mutuncin ki ko yayi min yawa ban san jaraba na kwaso ba wallahi ina tan tama akanki Anya ba aljanu gareki ba? haba yarinya Sai kace shed'aniya to wallahi zan mummunan Sab'a miki" ,tsaki tayi to ayi d'in wallahi Koni ko ku tashi tayi tayi hanyar kitchen don tasan dole mami tana shiga kitchen inde ta k'are karyawa ,barbad'a maganin tayi a k'asa ta fito d'auke da robar paro husy ce tsaye tace "koma ki aje kuma wallahi Sai na illa Taki tunda kin Maida mami sa arki" ,mami ce tace "husy k'yaleta ai kowa yayi na gari kansa. Bayan fitar ta tana shiga part d'inta ta dinga dariya. Shigar mami kitchen ta taka maganin nan ta gama abinda take ta fita zuwa d'akinta, tana zuwa d'aki taji kanta na juyawa 'yar K'ara tayi ta zube agun da gudu husy taje, nan ta ganta kwance ak'asa ihu tasa ta fita waje rasa ma Mai za tayi nan ta dawo ta buga wayar haidar lokacin yana office take ya d'auka kuka take tana sanar dashi baiyi wata-wata ba yaje ya d'au muk'ulli ya tafi husy na zaune gaban mami data farfad'o ko magana bata iyayi nan suka taimaka suka shigar da ita mota suka tafi hajar kam tana gano su ko ajikinta. *Bayan kwaana 2* haidar husy da zee na asubiti d'akin mami da tunda aka kaita bata magana Sai dai ruwa da take sha gashi likitoci since ciwon dai basu ga komi ba,haka dai suke zaune 'yan dubiya da 'yan uwa da abokan arixiki nata zuwa hajar ce ta shigo nan suka gaisa tana ma mami ya jiki Sai harar zee take sukam basu san tana yi bama nan tace "ya haidar ina son kud'i saboda zan kai Aysha asibiti" bai ce k'alaba ya zaro dubu biyar ya bata arene ta karb'a ta fita, dama ita bata tambayar sa unguwa duk randa tai niya fitar ta take ,Bayan fitar ta tana tsaye ta buga wayar kubra nan tace Ke Aiki yaci kuma da Alama haidar yasha maganin saboda Yanzu kud'i Nace ba gardama ya bani gashi mami akwance dama ita Ke hanashi min wani abun Dariya kubra tasa tace "ay dama ba ina gaya miki ba kika zauna shirme hajar tace "ai Yanzu na gano dawan garin". *Story writte&editted* *By Queen



* [5:35pm, 21/11/2016] Queen💋



: *ZEENATU by Queen



page 90-91* â™  â™ . â™  â™  â™ . â™  â™ . â™ . â™  *NWA* *Queen



* washegari zee ce zaune Ke matsa k'afar mami tana shafa Mata magani Bayan ta gama ta d'akko abinci ta tana bawa mamin bayan ta gama ta d'auki kayan mami ta wanke ta shanya duk ita Ke dawainiya da mami tun kwanciyar ta a asibiti don tama hana husy yi yau da yake satin ta d'aya abin dai ba labari kullum zee Ke zuwa da safeta ta zauna har dare san nan su tafi ita da haidar Sai husy ta kwana da ita ,su mum ma sunzo da dad dubiya soyayyar zee ce Ke dad'a wanzuwa a zuciyar haidar yanda yaga take Kula da mami duk irin abinda tai Mata bata Kula ba gashi hajar ma da take kamar 'yar Tata so biyu tazo nan ya dinga shiwa zee Albarka Yanzu ma da suke zaune a harabar asibitin yace "zee kin zama tauraruwa ta ki Kula dani san nan kuma mahaifiya ta Allah ya biyaki da Aljanna" murmushi tayi "my husby in ban maka ba wa zanwa? ka nunan soyayya kaine tauraro na dole na so duk wani Abu naka" lips d'in ta yake kalla yanda take maganar sai ta bashi sha'awa, suna hira sai ga dad d'inta ya shigo gano shi yasa suka mik'e nan haidar ya gaida Shi, suka shiga word ya kuma duba ta nan yaja hannun haidar yace "Ni ina ganin ciwon nan bana asibiti bane kaga yau fa sati daya ke nan ya kamata akoma da ita gida insha Allahu Ni zan samo wani malami" ,haidar yace "ba matsala insha Allahu zami magana a sallame mu. bayan fitar dad haidar yaje gun doctor yayi Mai bayani kan sallama zasuje suyi na Hausa bai musa ba ya basu saboda yana tunanin hakan. Washegari k'arfe goma aka sallame su suka tafi dad kwa zuwa yayi ya sanar da malamin abinda Ke faruwa nan yace zai istikhara san nan yazo gobe,kuma zayyo rubutu don yasha. mami kam har Yanzu dai baki bai samu ba zee kam tana gidan komi ita Ke Itada husy duk wani abin hajiya ita keyi sai dai hajiya taita binta da da kallo hawaye na zuba haka maman hajar data zo ita tayi ta d'awainiya dasu duk bakin da sukayi kowa sai Shi Mata albarka yake ,hajar kwa tana part dinta ko ajikinta duk yan uwan mami sai Allah wadai suke da canjin kawayenta,gashi idan haidar yayi Mata magana kam halayen ta ta hayayyak'o Mai sai dai yayi shiru. washegari da sassafe malam yazo haidar da husy ga mami a kwance yazo ya zauna ya Farai Mata adduoi tareda watsa Mata ruwan magani amai tafara nan yace wa haidar "abinda Ke damun mahaifiyar ka Gaskiya akwai sihiri ajikinta kuma abin mamaki na jikinta ne yayi Mata sai dai Bazan fad'a ba don gudun fitina sai dai duk acikin su wanda kukaga ya tsargu da harara to shine Allahu ya'alam". magunguna ya fad'a musu wanda za asayo da adduoi wanda zata na yi Shi kuma yace aje Islamic chemist sayo. jikin su a sanyaye dukkan su nan malamin ya fita suna Mai godia basu Dad'e ba hajar tazo sai cika take tana batsaewa ta zauna kan kujera tana harara basi mata maganaba tunda sun san ayanda hajar ta canja hali zata iya komai, ba wanda yace Mata komai sai cewa tayi "wanda dai yayi Ma mami sihiri sai a binciko Shi duk da duk mu nan 'yan uwa ne sai bare d'aya" ,nan haidar dake huci duk sun gane itace ya nuna Mata k'ofa ta fita tana ya tsina. kuka haidar yasa hakama husy data haye sama tana kuka mami kam bacci ta samu ganin hakan yasa zee tazo ta rungume haidar ta baya sorry my husby hak'uri maganin ciwo ne a komi mudai mu dage da addua kowa yayi na gari kan sa, sumar sa take shafawa kukan ya dena ya matseta gam ajikin sa yana Maida numfashi d'shiwa yayi ya shafo face nata yace "zeey bari naje na dawo". Baya son yanke hukunci nai shiisa yake so mami ta dawo hayyacin ta. *Story,writte&editted* *by Queen



* . . . . [4:06pm, 22/11/2016] Queen💋



: . . . *ZEENATUby Queen



 page92-93* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™  â™ . â™ . *NWA* *Queen



* tashin Mami daga bacci yasa ta dawo hayyacinta nan 'yan uwa akai ta san Barka su zee murna wajen k'arfe goma suna zazzaune Mami na kan kujera tana Shan kunun gyad'a, zee da husy na game a waya nan Mami ta kalli zee tace "zeenatu yau na tabbatar naka sai naka dad'in zama sai bare inji hausawa na munana miki, Yanzu kin zame min farin gani Allah yayi miki Albarka nagode" zee da kanta ke sunkuye tace "Mami ba komai innai miki kamar mum na yiwa" haidar ne ya shigo fuskar nan a washe ya zauna Mami naji dad'in ganin warware warki" kallonsa tayi "to yakamata ka d'auki matarka ku tafi kullum d'awainiya take dani ya kamata taje dakinta ta huta,wallahi samun sirika irin zee sai an tona Nikam Yanzu Bana ma sirika dake sai d'iya", kallon zee yayi ya d'aga Mata gira juyar da kai tayi tana murmushi tashi sukayi sukai sallama suka tafi. Bayan kwana 3 haidar na zaune yayi yana kallon sama zee tazo ta cakumo Shi ta Baya nan ya janyo ta ta fad'a jikinsa, kallon juna suka tsaya yi zee tace "husby mayya faru ne"? kallonta yayi yaja siririn haancin ta, yace zee "Ni fa na gaji da halayen hajar kawai zan rabu da ita tun abinda taiwa Mami kalli fa rashin lafiyar da tai duk itace sila, domin naso sallamar ta Mami ta hana Amma ku dubi abinda take" zee tace "Kayi hak'uri ka k'yaleta idan mai shiryuwa ce zatayi" baice komi ba yace "Allah yasa" nan kamata suka mik'e yace "zo na kaiki kisha icecream" da gudu ta tashi ta sako aftrdress suka tafi kana ganin su kaga masoya masu k'aunar juna. boka mai kankan na zaune yana surkulle nan yayi surkullen daya sa hajar na bacci ta tashi da K'ara ba addu'a balle salati, Aysha yar wata uku na bacci ta tashi da kuka ,kallon agogo tayi taga k'arfe d'aya dai-dai ko d'aukan Aysha batai ba ta fita shashin Mami suna zaune husy na karantawa Mami novel GIMBIYA MAIMUNATU tana jin dad'in book din duk da awaya take karanta Mata. . . hajar ce ba sallama ta shiga ta tsaya tsege-ge tace wa Mami "to tsohuwa ki gayawa d'anki Lalle ya zo ya maidani d'ayan gidan domin na gaji da zama dake ana samun Ido dama bakya k'aunata wallahi Bazan yarda ba" husy ce ta mike "hajar haukan naki ya isa haka" hajar tace "bai isaba ba banza kawai" dai-dai lokacin haidar ya shigo jiyo kukan Aysha yasa yayi part d'in a sukwane ya shiga d'akin yaganta ak'asa tana kuka da alama daga gadon ta fad'o d'aukanta yayi suka fita, dai-dai yana shiga hajar na watsawa mami ruwa a fuska mik'awa husy Aysha yayi ya zare belt yayi Ma husy duka yana gama dukanta ta cakumi kwalar sa Mami kam kuka take, nan ta bugawa umman hajar waya hajar tace "idan kacika d'an halak ka sakeni wallahi na gaji da zama da kai" shiru ya ratsa gun, jin hajar ta zafi zagi mami yasa haidar ya fusata yakai Mata Mari "hajar ki tafi bana son ganin ki, Mami sai dai ki hak'uri na saki hajar saki d'aya tunda ita ta buk'ata", tsaalle ta buga tace "tafi nono fari" fita tai part d'inta ta d'au waya ta bugawa kubra nan ta gaya Mata kubra tai shewa Amma "Kinyi tsiya tab! kubra da ta kashe wayar tace "dama banason ganinki da wan nan handsome guy d'in yafi dacewa da gentle lady" Ni miemie Nace Allah ya kiyashe mu tab'ewa ka rabamu da muggan k'awaye. Akwati hajar ta janyo dai-dai lokacin mamanta tazo hajar na tsaye tana yarfa hannu sai ambata 'yarta umma tace "Yanzu hajar sai da kika kashe auren nan? Allah yayi miki sittira Amma kin watsar shikenan ba baki nai miki ba, Amma da wuya ki Sami kamar haidar kuma nagode duk da abinda kikaiwa yar uwa ta" .umma ta kalli haidar tace" karku bata yar" afusace hajar ta fice wartata tafi gida. Mami ce ta k'arfi Aysha ta bawa umma tace abawa hajar ta cigaba da shayar da ita saboda yarinya ce hak'uri umma taita bawa Mami, Mami tace "karki damu aini Naga Darasi sosai Allah ya ganar damu Gaskiya ita kuma Allah ya shirye ta nan duk suka ce Amin. *Story writte & editted* *by Queen



* [4:43pm, 23/11/2016] Queen💋



: . . *ZEENATU by Queen



 page94-95* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™  *NWA* *Dedicated to Lubie & bena* *Queen



* Bayan komai ya lafa hankalin haidar ya kwanta shida zee zamansu mai cikeda k'auna da amana duk da hausawa nacewa harshe da hak'ori ma na samun sab'ani hak'uri shine jigon komi a rayuwa,zee na tsaye tana sawa haidar mab'allin rigar sa ta fesa mai turare k'ok'arin tafiya office yake Amma saboda shagwab'ar data ke zubamai ya kasa tafiya Bayan sun gama komi ya fito zai tafi suna sak'ale da juna dining table sukaje don karyawa haka sukai ta ciyar da junansu cike da shauk'i da k'aunar juna har bakin mota ta rakashi rik'e da briefcase din sa, ta juya zata tafi ya janyota ta fad'a jikinsa kallon tsakiyar idon ta yayi yace "am proud of you wallahi" nan ya bata peck a kumatu murmushi tayi mai "iluv u my haidar" Jan motar yayi ya d'aga Mata hannu da gudu ta shiga gida tana mai godewa Allah daya bata miji d'aya tamkar da dubu. hajar kuwa rayuwa ta juya Mata Baya domin ta kuma komawa gidan boka mai kan-kan kan yayi Mata asiri don ta koma gidan haidar,suna zaune boka ya tashi don dauko masu magani sai gashi wuta ta tashi a dakin da gudu ya fito ganga -ganga wuta keci nan Mata kowa ya kama gabansa boka sai sumbatu yake yana ihi kamar ya haukace kafa mai naci ban baki ba su kubra da hajar da sauran Mata ke gudu yana binsu,su hajar yake bi yana hajar ta tsaya har bakin titi suka je garin tsallakawa d'ayan side d'in mota ta kad'e hajar da kubra nan hajar ta karye a k'afa haka ita kuma kubra ta karye k'afa da hannu mai kan-kan. kuwa wata mota tayi ciki dashi ko shurawa baiyi ba yace ga garinku nan dama k'arshen mushirki ke nan .haka aka kawo hajar da kwatance gidan su ranga-ranta nan umma tai shiga dawainiya da ita wajen wata daya har ta samu ta warke ,haka umma take gidan kubra tai Mata kaca-kaca kan karta Kara zuwa gun hajar ,kubra kam ta kanta take domin ita bata da gatan hajar har yanzu tana kwance zaman jinya. Bayan warkewar hajar umma kam Sabon babi ta bud'e domin ta sakawa hajar ta kunkumi domin duk aikin gidan su wanki shara girki ita keyi duk ta rame ta fita hayyacinta, bata da tsugun ga k'uraje da suka fito Mata duk jiki ba gaira ba dalili Amma tana Shan magani sun fara warkewa zaman gidan ya isheta domin in tayi laifi duka takeci gun babanta domin yace tunda ta kaso aurenta to dole ta fuskanci matsi gashi ko cimar gidan ta isheta nan ta tuno gidan ta komai waja-waja dana sani ne fall aranta, yau ma data ci uban wankin k'annen ta ta gaji lub'us tazo gaban umma tace "umma ki taimakan na koma d'akina wallahi na saduda shed'an ne ya zuga ni nayiwa su Mami rashin mutunci Amma na saduda" harara umma ta wurga Mata "sai yanzu kika gane? ai kinyi rashi sai dai ki hak'uri haidar yayi miki nisa domin kinyi wasa da damarki dama ai na gaya miki ke ai kina ma da gata" kuka ta saka umma ta kai Mata hauri da gudu ta tashi ta tafi tana kuka. yau haidar ya kawo wa zee sabuwar mota Benz k'aramar ta mai k'ofa d'aya sai shek'i take ihun murna zee take ta rungume haidar Allah Yaso ta iya driving godia take ta zubawa da yamma suka tafi gidan Mami nan ta nuna Mata haka Mami tayi farinciki ta kalli haidar "Amma ka birgeni kyautatawa mai kyatata ma" nan ta janyo zee ta rungume "yata Nima insha Allah Bana zaki hajji keda husy tukwicina kenan" kukan hawaye ke zuba a idonta rungume ta tayi tana godia haka suka tafi gida aranar soyayyar suka gurza abar su son ransu dama Burin zuciya ta samu muradinta. Washegari zee taje gida tayi kyau tai b'ul-b'ul tasa wata super mai kyau ta d'ana dogon takalmi sai drivin take hankalinta kwance mum da dad sunji Dad'i ganin motar da zee ke ja sunyi wa haidar godia mum kam ganin yanda zee ta ta samu farinciki ya sata farinciki suna d'aki a zaune mum tace "zee kinga ribar hak'uri ko aishi Baya fad'uwa k'asa banza Allah ya dai Baku zama lafiya" sai k'arfe biyar na yamma ta tafi gida. *Bayan kwana 2* dayake yau weekend haidar da zee sunje gida gun Mami anata hira da jin Dad'i hajar ce ta shiga da sallama duk ta rame tayi baki ga tabon k'uraje duk ajikinta nan tasa kuka "Mami ki yafemin haidar kaima ka yafe haka kema zee wallahi sharrin she'd'an ne da rud'in k'awaye nasan nayi butulci ku yafe mun"ganin yanda ta koma ya basu tausayi yasa suka ce sun yafe ,gyara zama tayi "ya haidar ka taimakeni ka maidani d'akina" ,nan ya kalleta Kiyi hak'uri idan kin samu miji kiyi aure nai miki alk'awanni kayan d'aki 'yan waja ko ba komi ke k'anwata ce, kin ganni nan zeenatu ta ishen" Da k'yar ta tafi cike da dana sani dama ita rayuwa yanda ka d'auketa haka zata zo maka bikin kb da Anee ya taso su zee da haidar sai shirye- shirye ake haka satin bikin ya kama aka gudanar zee ta zamo babbar k'awa shima haidar babban abokin ango, anyi biki lafiya aka kai Amarya gidan ta sai kuma bikin munay da za ai nan gaba saura 2 month. Bayan wata d'aya suka fara shirin tafiya hajji itada husy sunje lafiya sundawo lafiya basu dad'e da dawowa ba akayi engaged din husy sai jiran biki kawai. wata biyu atsakani zee ta fara laulayi na samun cikinta sunje asibiti an gwada tana da Shi wata d'aya dai-dai nan Sabon tattali ya tashi gun haidar aikin kirki r Baya barin zee tayi haka school shike kaita ya d'auko ta yace tabar driving har sai cikinta yayi k'wari. An yi bikin munay da angonta musbahu nan ma zee da Anee sunyi rawar gani duk da zee na fama da laulayi anyi an gama lafiya ankai Amarya d'akinta sai fatan zama lafiya zee munay da Anee sun zamo yan uku sun rik'e kansu bisa amana da kaunar juna haka yanzu bussness suke su ukun ga mazajen su ma kansu a had'e don munay ma ta shigar da musbahu gun kb da haidar. *Story writte &editted* *by Queen



* [4:48pm, 23/11/2016] Queen💋



: *ZEENATU by Queen



 page 96-97* â™ . â™ . â™  â™ . â™ . â™  *NWA* *Dedicated to Lubie &bena* *Queen



* *END OF THE STORY* Haidar dake driving defense ga zee ta d'au ado da kwalliya zasuje gidan kb ga babyboy a hannun ta kyakykyawa dashi d'an wata uku ga aysha yar hajar yar shekara 2 abayan mota taci ado domin ba adad'e da maidota ba tun Bayan bikin husy da angonta Ibrahim inda aka kaita kano, to Bayan bikin ne aka dawo da aysher parking sukai a harabar k'ofar gidan kb nan haidar ya fito ya bud'ewa zee gaban mota ta fito, munay ce ta fito tana hararar zee da dariya tace "saraakan soyayya tund'azu munata jiranku" zee tace ke "barni kinsan in ban gyare husby na ba Bana samun nutsuwa" munay tace "ashe kina gane karatun" dariya suka sa munay ta karb'i Arif tana mai wasa nan suka shiga gidan Anee ta tare su da cikinta da ya fito dama lunch suka had'a agidan Anee haka suke duk wata sai aje gidan d'aya ai lunch ko dinner kb ya kalli haidar yace shegen sama kana sha'aninka na zeenatu bada kanka adade" haidar yace "to ya za ai tinda madam ta shagwab'ani" hajar kuwa da k'yar ta samu wani a Bayan layin su mai saida kayan miya matan sa biyu domin duk unguwar gunsa ake sayan kayan miya da farko ta raina Shi kancewa ba ajinta bane sai da dad yayi Mata fata-fata san nan ta yarda aka d'aura auren aka kaita gidan nasa itace ta uku agidan ba yanda za tai dole ta zauna domin girkin 'ya'yan gidan wajen su goma ita keyi,ga jarabar kishiyoyi sun isheta dana sani ba irin wanda batai ba Ni



 nace wanda baiji bari ba ai yaji hoho. *Bayan shekara* d'aya zee na driving amotarta Baya ga mai aikinta dasu aysha da Arif parking tayi a gaban wani supermarket nan ta shiga kana kallonta kasan Hutu ya zauna a jikin ta ta gama gama soyayya akayi counting ta fito taga wata Mata na kuka a gaban mota har ta wuce ta tsaya,tai Mata sallama matar ta amsa zee tace "duk da baki gayan matsalarki ba, nasan ciwon 'ya mace na 'ya mace ne kiyi hak'uri domin Shi hak'uri babban jigo ne arayuwa" ,matar ta d'ago ta kalli zee gata agirme matar ta girme Mata nan tace " bakomi wallahi matsalar uwarmijina ce da k'annen mijina ya damun yanzu ma sune sukai min waya suka gayan ba Dad'i" zee tayi murmushi hak'urin dai shine san nan kiyi ta addu'a ki zauna dasu tsakani da Allah ki kyautata musu wallahi da sannu sai kin musu zarra duk rashin sonki da basayi wataran zasu soki" matar tace "bakomi nagode insha Allah na dau shawarar ki" nan tai Mata sallama ta shiga motar ta taja. haka rayuwar zee da haidar ta kasance cikin so da k'auna awajen haidar kuwa zee ta zamo tauraruwa,domin mace ta gari itace jin dad'in rayuwa.bissalam *ZEETAHAIDAR* tammat bihamdillah Anan na kawo k'arshen littfain zeenatu abinda nayi ba adaidaiba Allah ka yafemun Amin. wasallallahu Ala nabiyur rahmati wa ahlihi wasahbihi ajma'in. Ina mika godia ga d'aukacin yan NAGARTA WRITERS ASSOCIASION Allah yabarmu tare Amin. gaisuwa ga my frnds: Autar hajia Lubie maitafsir benazir futha my miemiebee umma adnan Anee Anush mamu ummul fadeela feenat ja afar hawwa damary chuchungaye ummu samha sadyjegal feedoh jabo Ashnur pyar Zahra bb maman shakur da sauran wadanda ban fad'oba duk kuna raina 'yan group dina na



 novel ina mik'o gaisuwa ga duk wanda ke ciki,da kuma 'yan kasaitatun Mata kuna birgeni Allah ya bar k'auna. haka kuma 'yan excellent writers ban manta kuba. da sauran groups wanda innace zan fad'o su sai gun ya cika Allah ya bar kauna luv you Lodi Lodi godia gareku kun nuna k'auna ga zeenatu kamar su maryam oumeey aysha nuhu maryam kabeer Maryam Ahmed aysha husna danima rayyn halima sadiya fiddy da dai sauran wadan da ban anbato ba duk kuna raina godia Allah yabar zutunci. da duk wani mai kaunar littafina Nima ina k'aunar sa Ban mantakuba mutan group na kaleesat haidar Godia Agareku da kulawa luv much. *takaitaccen tsokaci akan littafin ZEENATU* *jigonsa hak'uri kunga yanda rayuwar zeenatu ta fara da rashin hak'uri da yanda daga Baya aure yasa ta koyi hak'uri da sanin rayuwa* *san nan kuma jajircewa gun iyaye kan taribya kunga yanda mum ta jajirce,har zee ta koyi hkr a rayuwa san nan dogaro dakai* *san nan kunga yanda Mami ta takurawa zee Amma duk da hakan tayi hkr ta jajirce Amma saida k'addara ta afka suka rabu dama rayuwa bata tab'a zuwar wa mutum daidai,kowane k'alubale yana tattare da k'addara* *aganinta hajar ce ta dace da haidar sai gashi tasa Mami tayi danasani sosai kunga Anan ya nuna matsalane iyaye suna sa yayan su adamuwa su takura musu kan abinda basa so akarshe kuma sune da damuwa*. *kunga yanda haidar yayi wa Mami biyayya ya shiga damuwa adalilin hakan Amma daga Baya sai gashi hakurin sa da biyayyar sa yasa yaci riba kunga yanda duk budurin da aka sha gashi dai zee ta zamo tauraruwa a gidan mijinta yayinda Mami tazo tana kaunar ta ainun dama hausawa nacewa naka sai naka dad'in zama sai bare wan nan shine* *Zuwa gidan boka kuwa babbar illah ne gun Mata sab'awa Allah ne ,kunga yanda adalilin hakan hajar tayi dana sani* *ta had'u da k'awa mai son kanta, ta kuma kaita ta baro Allah ya kiyashemu tabewa* *Da fatan fad'akarwar dake cikin littafin zata amfane mu nagode* *sai kun sake jina wataran a sabon book dina mai suna...........luv u oll* *Story writte &editted* *by Queen

Comments

Post a Comment